GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDANMU 1&2 COMPLETE HAUSA NOVEL

GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

Shakira..
3/22/22, 23:06 – Ummi Tandama😇: GIDAN MU..!
(Our House)
Book 1

Wattpad:Jamilaumar351
Mallakar:Janafty❤️

         🅿�26

Ba bata Lokaci sai ga Baba Asabe da Wani Hoto a hannunta an yi Elagement dinsa ta mika ma Daada,ta karba Lokaci Daya tana Kallon Hoton Cikin Raunin zuciya sai ga Hawaye Sharr sun Zubo mata hannun da Casbaha ke hannunta ta sanya tana Shafa Hoton Tana Fadin”Allah sarki Rayuwa…Zuwan da Zuwaira tayi na Karshe ne da bata kara zuwa ba Allah yayi mata rasuwa,bayan wata Karamar Sallar azumi ta kawomin wannan Hoton tace Daaada saboda ke na saka aka wanke shi aka Gyara miki shi Gamu nan dukkanmu Harda Marajin jikan ki an samu Dakyar ya Shiga Hoton watarana in kinyi kewar ganinmu sai ki Dauko ki Duba..!
Tabbas ta fadi gaskiya ashe Watarana Zan yi kewa kewa kuwa ta har Abada..!
Daada ta Karishe fada cikin karyewan Murya kafin tace”ALLAH yajikan ki Zuwaira ya Kyautata makwancinki..Ya”yanki da kuka Amsa kiran Mahallicinku atare suma Allah ya Karbi Shahadarsu Allah ya Hadamu a aljannah Firdausi..!
Gabadaya Falon aka amsa da Ameen Jikin kowa yayi sanyi kamar yau ce akayi wannan Babban Rashin Inna Maimuna sai sharan kwallah take Saboda Tana ganin kamar yau ne komai ya faru.
Share Hawaye Daada tayi kafin ta Mikama Baffa Kabiru Hoton tana Fadin”Ku bama Matan ku da ya”yanku su gani..!
Daga haka bata kara mgana ba ta Cigaba da Jan Cashabanta Cikin Rauni da Rashin Lafiyar Jikin Tsufa.
Bai ma Tsaya kallon Hoton ba ya mikama Daddy ya karba Shine ma ya Tsaya yana kallon Hoton,Malami ya Kurama ido yana kallonsa sai yaji wata Kwallar ta tarumai a kwarmin Idanuwansa Dukkansu ne da Sallah ne suka Dauki Hoton da Ya”yan da Uban Duka Farar shadda suka saka da Hula Anni kuma dasu Asma”u suna Sanye da wani Leshi mai kyau iri Daya sai Auta Munari Dake sanye da Shadda Fara irin ta su Abba an mata aikin mata Imran ne kadai a Hoton bai saka Shaddan ba,lokacin Ya dawo Daga makaranta Ibadan Ba”a son ranshi ma yayi Hoton ba sai da Anni tace in bai Tsaya ba sai ta Sabamai Shi Sanye yake da Bakin wando da Farar riga mai Kauri Gajeren hannu Gareta,kirar Armani Yadda ya hade rai ya kalli Gefe Fuskarsa ma bata Fito DAkyau ba Zaka Fahimci baiyi niyyar Daukan Hoton nan ba Dole aka sakashi Imran kenan.
Daddy saboda Raunin Dayaji zuciyarsa tayi yasa ya mikama Inna Maimuna Hoton suka Taru ita da ya”yanta suna gani tana Fada musu Sunayensu Sai da tazo kan Imran ne ta Dago Tana kallon Daddy Lokaci Daya Tana Nunamai shi Tace”Ya Mustapha wannan banganeshi ba. ? Me sunansa na kusa da Yusuf..!?
Kafin ya bata Amsa Daada Dake ZAune tace”IMRAN kenan Miskili kafin mahaukaci ban Haushi..!
Gaban inteesar sai da ya Fadi Dataji an ambaci sunan Imran haka take Fama da Faduwar gaba Tunda ta Dawo ko sunansa ta Tuna sai gabanta ya Fadi ballatana ta Tunashi ta rasa Dalilin haka..
Haka Hoton ya Dinga Zagaya Falon Daya bayan Daya,Inna Maimunace take nuna Wadanda suka Rasu da wadanda aka nema aka Rasa Daidai Lokacin da Hoton yazo hannun su Anty Hauwa ita kuma Inteesar tatashi Zuwa Cikin Dakin da Anty Hauwa ta Sauka ta Dauko Madaran Abiden Dake Cikin Fidarsa yana Hannunta sai ya Fara Kuka Umma tace taje ta Dauko to Dataje sai ta zauna achan ta Hadamai ta Bashi yasha koda ta Dawo Hoton ya bar Hannunsu yana Hannun Mami Asma”u wacce ta mikama Umaima ita kuma ta mikama Sajida wacce ta Dade Tana kallon Hoton Imran Take kallo duk da ba sosai Fuskarsa ta Fito ba sai da akallo Daya zakamai ka Fahimci yana da wasu abubuwan da bakowani Namiji ke dashi ba ta Shagala da kallon Hoton har sai da Khamis ya taso da kansa ya karba ya Koma Wajen zamansa suna Kallo su da su Sa”id dasu Ya basheer suna kara Jimanin Mutuwar su Anni da su Asma”u Allah Sarki da yau sunan nan anan Wajen da duk abunda ya Faru bai Faru ba.
Duk da Inteesar taso ganin Hoton ammh Ganinsa Hannun Khamis yasa bata ma ce Zata gani ba,Da Umma ta TAmbayeta ko ta gani sai tace Eh tagani Saboda bataso ace taje ta karbo hannun wannan mai Mayen Kallo.
Bayan kowa ya gama ganin Hoton aka Maida ma Daada abunta ta karba Ta ijiye gefenta irin su Sa”id dasu Ya Basheer harda Snaping din Hoton a Wayarsu.
Daada tayi gyaran Murya Tana Fadin”Ina Fatan kowa ya ga Hoton nan ko..?
Gabadaya aka jinjinamata kai kafin ta Cigaba da Fadin”Ina neman Taimakon ku..Ba Taimakon Dai dai kun ba..kowa Dake wannan wajen ban Dauke mai ba Mazan ku da matanku ina ji ajikina Malami bai yi Nisa sosai ba yana nan kusa Damu don Allah ku saka Ido ku nuna ma abokan aikin ku Da Wadanda kuke mu”amala dasu ko Kila wasu daga cikin su sun Taba ganin Daya Daga cikinsu,na tabbata baza”a rasa wanda wata Mu”amala ya Taba Hadasu dasu ba koda Bayan barin su gida ne..!
Gabadaya aka amsa mata da Insha Allahu Sa”id ne ya Daga hannu yana Fadin”Daada in kin bani Dama Ina so zan yi mgana. !
Daada ta gyadamai kai Tana Fadin”An baka Dama Sa”idu!
Mikewa yayi Lokaci Daya yana gyara Zaman Rigar jikinsa Data Tattare saboda Zama yana Fadin.
“Assalamu alaikum da farko dai Kamar yadda wasu suka sani ni Sunana Sa”id Sulaiman ni D”a nake wajen Inna Maimunatu da Farko wani dan Shawara zan kawo mana game da Riko da Zumuncin da Daada Tayi mgama..Gaskiyan mgana akwai gyara a Tafiyar nan tamu kamar yadda Mommy ta kawo mgana ne kan cewa Dukkanmu bamu yi nisan da zamu ki Ziyartar gidajen yan”uwanmu da iyayenmu ba,Sannan da yawanmu anan Wajen bamu san juna ba Akwai Kadan da na sani ammh da yawa wasu duk ban sansu ba sai dai kawai kasan kana da wan Mahaifiya yana da Mata yana da y”ya ammh kuma bakasan matar ba bakasan ya”yan ba kuma sunan an Fito Daga Tsatso Daya,Shine na yanke wani Tunani me Zai hana Tunda nasan kowa acikin mu Daga mu yaran Har iyayan namu muna da wayar Zamanin nan Data Zama ruwan Dare ko bamu Samu takawa munyi Zumunci ba ta kafa ba akallah kowa nada Lambar kowa bayan kowani kwana Biyu Zamu rika Kiran juna awaya muna Sanin Lafiyar junamu da kuma Sanin in wani abu ya Faru..sannan abu na gaba Zan Bude mana Group a manhajar nan ta Zamani Wato WhatApps Da sunan IYALIN MARIGAYI ALKALI DUKKU Zan karbi lambar kowa zamu yi adding dinsa acikin wannan Group Kama Daga mu har iyayanmu Inda Zamu Rika Sada Zumunci a Tsakanimu in wani abun karuwa ya samemu za”a sanar Domin mu Taya wanda abun ya sama Murna in Rashi ne ma kowa zai sani Tunda duka ana Chure waje Daya sannan in ma wane bai sani ba Wane ya sani zai sanar dashi..Mganata ta Karshe shine ya kamata bayan kowani Wata Biyu a samu Ranakun karshen Sati a Dunga Haduwa ana Tattauna wasu Batutuwan da suka Shafemu ta hakane Zamu san mtsalolin junanmu sannan Shakuwa mai Karfi Zata Shiga Tsakaninmu kuma hakan zai Sanyayama Daada rai Baza tayi Fargaban ko Bayan Ranta Rabuwar kai ZAta Shigo wannan gidan ba Daga karshe ina mai Sanar da Daada ta Kwantar da Hankalinta tunda ta Shigo Damu Cikin wannan Al”amarin sai inda Karfinmu ya Kare Indai Kawu Malami na Cikin kasar nan zamu nemosa Duk inda yake mu Dawo miki Dashi Gida shida iyalansa da yardan Allah..Wssalam..!
Ya karishe Fada yana komawa ya Zauna ba Daada kadai ba Kowa Dake Wajen yaji Dadin kalamansa kuma yayi Na”am dasu Daada na Mirmishi tace”Mustapah da Kabiru kunji Abunda D”anku yace ko..?kune Manya ku Zartar da Abunda ya kamata Duk abunda yace yayi Daidai yayi tunani mai kyau kuma naji Dadi..Allahu yayi muku albarka Gabadayanku daku da ya”yanku da Zuru”arku gabadaya Allah yasa yadda muka Hadu ayau anan Wajen haduwa ta gaba ace Ga Dan”uwanku agefeDaya Allah ya Bayyanasu Allah yasa suna Cikin Koshin Lafiya kamar yadda nake Fata..!
Gabadaya aka amsa mata da Ameen Jin an Fara kiran Sallar La”asar kana Daada tace”Kowa ya tashi yaje yayi Sallah..Daman Dalilin kiram nawa kenan ko ba Domin haka ba ina Bukatar ganin Ya”yana da Jikokina a kusa Dani yau gashi na ganku naji Dadi kwarai Allah ya maida ku Gidajenku Lafiya bazan zaunar daku ba Saboda akwai masu Ayyuka da yara Masu Karatu zuwa Gobe na Sallami kowa zaku iya Komawa Gidajenku Allah yayi albarka…!
Aka Shiga amsa mata da Ameen ta Mike Bayan Daddy ya Mike ya Taimakamata ta Kalleshi Shi da Baffa Kabiru Daya Mike Tsaye yana Duba agogon FAtan Dake hannunsa yana auna Lokaci ne in zai isheshi yau din Zasu juya abuja Daada ta gama batamai rai bayason ma ya kara Kwana agarin yaji tace”Mustapha kai da Kabiru in kun Idar da Sallah kuzo ina Neman ku..Asabe In kin idar da Sallah ayi Haraman Dora abinci mun cinye Lokaci anan wajen..!
Daga haka ta Juya tana Tafiya a Hankali Zuwa Cikin Dakinta Daddy ya Kalli Baffa Kabiru kafin su kada kai su Fice Baba Asabe kuwa Tuni ta amsa ta Shiga Dakinta Domin ta gabatar da Sallah Mazan ma sun bi iyayansu Waje Matan kuma Kowa ya kama Inda ya Sauka.
Bayan sun idar da Sallar ne Umma Tace Inteesar da Hafsah suje Kitchen su kamama Baba Asabe aiki Inna Maimatu harda karima da Zainabu tace suje suyi aikin gabadaya,Haka kuwa suka shiga Kitchen suka Zage suna Taya Baba Asabe aiki suna Hira Duk Rashin Sakin jikin Inteesar ta Fahimci ya”yan inna Maimunatu Dabam suke suna da matukar Kirki Shiyasa ta dan Saki jiki da su suna ta Hira Ita Karimam a Bauchi Take aure ita kuma Zainab tana auran Dan Wazirin Azare ne achan take da Zama duk adan Hiran da sukeyi ne ta ji hakan Daganan suka gangaro Hirar Inna Bintalo da ya”yanta yadda suke Fadan Halinta sam Inteesar batayi mamaki ba ko Daga ganin yanayinta,Daganan Hirar Mami Asma”u ya Shigo itama da ya”yanta Sai Hankali suna mgana sukace duka Laifin na Baffa Kabiru ne Shine ya Sakarmata Komai da kuma da Fifita Boko Fiye da al”adunn Addinin Musulunci,Suna labarin Halayyar Sajida kaf na Uwarta ne ta kwaso gwarama Umaima sau Dubu Sajida ga Rashin kunya ga ba kwaba sai Sangarta da Sakarci kamar wata yarinya Duk Inteesar na jinsu ita dai bata Tofa ba sai dai kawai ta Murmusa aranta Tana fadin ita Taga Rashin kunyar Sajida tun lokacin ta Gama Sanin Halinta kaf ta kuma san inda ta ijiyeta..
Sai gabda mangariba suka gama aikin white rice ne sukayi da Miyar Naman Rago sai Ferfesun kaji da Daddy ya bada kudi su Basheer suka Fita suka Siyo sai Salat da Lemon Aya da na Kankana suka Hada,Daganan kowa ya tafi yayi sallah Su Umma da su Inna Maimuna daman suna Falo suna kallo suna Taba Hira Mami kuwa da ya”yanta suna Daki basu Fito ba koda Umaima tace zata je Kitchen hanata Tayi.
Inteesar dai bata iya Sallah ba Sai da ta Watsa Ruwa kana ta gabatar da Sallah Tana Kan darduman har aka Kira Insha”i tatasshi ta gabatar ta Idar ba Dadewa taji Hayaniya afalo kenan Mazan sun Dawo daga masallaci sun Shigo kenan,Tana nan zaune bata tashi ba Hafsah tazo tayi Sallar Isha”i tace tazo su je su Taya Baba Asabe kawo su abinci Karima na Wajen tace Su Anty Aneesa gasu chan suna kwasowa jin haka yasa bata yi yunkurin Fita ba sai da Hafsah tace ta Fito suci abinci kana ta Fito duk da bama ci Zatayi ba ita abu mai Ruwa Ruwa Zata sha Shiyasa tana Fitowa Kitchen ta Nufa ta Tsiyayo Ruwan Zafi a Flaks ta Hada tea a wani karamin Mug ta Fito dashi da Cokali Tana Juyawa Daki tayi niyyar komawa Domin yau cin abincin basu Daddy suna Dakin Daada suna mgana Matan ne sai Ya”ya sai jikoki sai Tattaban kunnen Daada Dake Tsalle Tsallemsu afalon.
Har takai Kofar Dakin taji an ce”Ina Zaki..?badai bazaki ci abinci ba Inteesarr..!
Yadda ya fadi mganar ne Cikin Wata Murya yasa ta waigo Khamis ne ko ya Kureta da Mayen kallonsa kauda kai Tayi Tana Fadin”Eh am ok..!
Sai da ya wani kalletaa kasa kasa kafin yace”U are ok dame..? Me kikaci..?
Takaichi da Haushi suka kama Inteesar ba ita kadai ba Hadda da Mami Asma”u da Sajida da basu ga Dalilinsa nayi ma Inteesar mgana ba.
Rausayar dakai tayi Cikin Kosawa Tana Fadin”zan sha Tea..!
Tafada tana Dagamai Mug din Dake hannunta Zai sake mgana Mami Ta Kallesa Kafin tace”Khamis plz kaci abincinka Tace She is ok ko Dole ne..?
Tafada Cikin Halin ko in kula Umma naji batace komai ba sai chan Tace”Intee bamai cin abinci bane..Tafi daman shan Ruwan zafi in Zata kwanta.!
Mami Ta tabe baki Kafin tace”Plz Help me.. tell Him..!
Daga haka ta Tsuke bakinsa Shima bai kara mgana ba sai Binta yake yi da kallo Itama Juyawarta Tayi ta zata Shigo Dakin Sa”id ya Kirata ta waigo Cikin Girmansa yace”Ya Zaki tafi..? Da fa mun gama cin abinci zam karbi lambar kowa..Kowa kuma zai yi Sharing Cantact dinsa da Dan”uwansa..!
Yake Inteesar Tayi kafin tace”Ya Basheer plz ka bashi Cantact dina..!
Harara ya Dago ya Sakarmata yana Fadin”Ni dan aikin ki ne..?
Shagwabe mai Tayi tana Fadin”Plz Bro..plz Mana..!
Kallonta yayi kafin yace”Ok..Naji kafin ki samin kuka..!
Dariya tayi har sai da Fararan Hakoranta suka Bayyana tace”Tanque Bhaya..!
Sa”id ne yace”To in an bamu taki na Sauran fa yaushe zaki karba..?
Da sauri tace”In d mrming kafin mu tafi Insha Allahu..!
Kai ya jinjina kafin yace”Is ok..Buh ki karba kisan Is very Important..!
Kai ta gyadamai kafin ta Juya ta Shiga Cikin Dakin tana Sakin Sirrin Tsaki Aranta Tana Zagin Khamis kallo kamar Wani maye yayi ta Kallonta Haba ita fa ta kosa Gobe Tayi subar Gidan nan ta koma Tayi Shirin komawa makaranta Munari tace itama bazata Shiga School ba sai in ta Dawo su Shiga gabadaya.
Tana gama Shan Tea dinta ta Haye gado Ta gaji Barcine a Idonta Lokaci Kadan baeci ya kwasheta Sama Sama Tana jin Tashin mgangansu Daga Falon Daada.
Su kuwa sai wajen 11pm Taron ya tashi Adaran Sa”id ya Bude group din ya Karbi Lambar Kowa ya sakashi,Daga kan iyaye har kan Kanne da yayyi irinsu,Ya kuma Umarci Kowa ya Karbi Lambar kowa,haka akayi sukayi ta Sharing din Cantact din juna da alkawarin Kiran juna Lokaci bayan Lokaci,Umma daman Tana da Mami sai dai su yi Wata Biyar ba wacce ta kira Kowa acikinsu Sai ta karbi ta Inna Maimuna da Inna Bintalo yaran yaran kuma suka Karbi da junansu,Umaima ce ke bata Lambarta Cikin Dadin rai banda Sajida har gwarama Mami ta bata nuna wani abu ba Ba wanda na yabi ta kanta Ballatama ya Damu da ita banda Hafsah ba wanda ya karbi Lambarta,Sai ya”yan Inna Bintalo Daman Hadeje ce da kano,Lambar Inteesar kuwa Umma ce tayi ta badawa Mazan kuma Basheer ya basu Wannan abun yafi yima Khamis Dadi Domin Hanya mafi Sauki kenan Wajen Cimma Burinsa kan Inteesar da Tunda ya Fara ganinta Tunaninta da Soyayyarta suka yi mai mugun kamu basu barshi yayi barcin Kirki ba.,Love at first sight kenan
Su Daddy kuwa sai Wajen 12pm suka Fito Daga Wajen Daada suka ci Abinci suka Nemi makwanci Nasihohi ne Tayi musu sosai mai Shiga jiki wanda Har sai da shi kanshi Baffa Kabiru ya yarda da Kuskuransa kuma yayi ma Daada alkawarin Inshu Allahu zai gyara Daganan suka Shiga Hira da Tsara yadda Zasu Hada hannu dasu da ya”yansu su zama Zuru”a Daya ba Wariyar Launanin Fata shi ya bata musu Lokaci basu Fito da wuri ba.
Ranar Daada Tayi barcin Farincikin Data Dade batayi ba.
Washegari Tun 4am na asuba Kowa ya Tashi saboda Sammakon Tafiya,ko kafin karfe bakwai na Safe Masu Shirin Tafiya duk sun Shirya Baffa Kabiru suka Fara Tafiya Sadam wanda Zai je kano Inteesar ta karbi Lambar Matarsa Aneesa tayi mata alkwarin in ta koma kano ZAta zo Gidansu tunda tace suna Sharada Phase3 ne da Zama.
Daga sune sai Sa”id da zasu je Dutse Tare suka Tafi da Hafsah tunda Tana Wajensa ne itama sun karbi Lambar juna ita da Inteesar,karfe tara na Safe su Inteesar suka Mika Hanya sun bar Inna Maimuna na Shirin Tafiya ita da ya”yanta sai sun Biya ta Bauchi Inna Bintalo kuwa sai gobe Zata koma,gida duk yayi Shuru tunda Baki sun Watse Daada ta Bisu da addu”an Allah ya kaisu Gidajensu Lafiya kamar yadda suka zo hankalinta bai kwanta ba sai da Kowa ya Kira yace ya sauka Lafiya Har Inna Maimunatu da suka Tafi Daga baya suma sun sauka Bauchi lafiya sai dai kuma wani Haduwar In Allah ya nufa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button