NOVELS

WATA ALKARYAR COMPLETE NOVEL

   …
Ina fita na gayawa Yoona inda zai kai ni, tunda na fita na zauna tare da shiru ina nazarin rayuwar da muke ne baki daya babu dad’i,

   Waiter din ne yazo ya ce min.
“Me za a kawo miki.”
“Americano coffee” gyada kai yayi can sai ga shi da shi. Yana kawo min na fara sha, ina jin kamar na fasa ihu, baki daya na rasa yadda zan yi da Jamilah, wallahi babu yadda xan yi da ita baki É—aya, bana son a fahimci matsalar da ke tsakanin mu balle ayi tunanin akan namiji muke wannan yanayin.

        Tashi nayi tare da shan rabin Coffee din sannan na tashi na ajie musu kudin su, nayi tafiya ta. A motar taxi  na tafi Rehab, ina shiga nayi na shiga hada kayan ta. Tana inda na barta.
“Ki zo mu koma gida, abinda Bilal yake bani ya baki kema kar ya hanaki”

Na fada mata, tare da fita na kai kayan taxi. Haka itama ta fito muka tafi gida. Ban gaya musu zan dawo da ita ba sai ganin mu Umma tayi, bata min magana ba, bayan na shiga dakina zube a gadon nayi. Kwalla ne ke zuba min, taya zan musguna mata? Amma idan na tuna last word na Ammyn mu sai naji na tsani kaina, domin ina gani matukar na mata wani abu Ammyn zata iya jin fushi dani dan ban rike amanar da ta bani ba.

         Ban san lokacin da kuka ta kwace min ba...

Kuyi maneji don Allah
300â‚?… Insha Allah’
+2347035133148 a tuntube Zahrah Addah Ramlat, Yan Niger su tuntubi Nana A’ichah
+22784506476
0472282105 Ramlat abdulrahman manga GT bank

Mai_Dambu

3/16/22, 11:16 – Nuriyyat: 82
“Kwarai! Nima aurenki zan yi” tab’e baki tayi tana me wucewa tashi yayi yana faÉ—in.
“Tafiyar tafi maganar jan hankali!” Juyawa tayi ta Kalle shi sannan ta ce mishi.
“Baka da matsala kana azumin Alhamis da Litinin zai rage maka damuwar ka.” Tayi tafiyar ta, ba so bane a tare da Alman, sha’awa ce da muradi da zai rage sha’awar shi ba zai kuma damuwa da ita ba.

   Shiryawa suka yi ya kai su Asibiti, sun wuni a can, sun leka dakin sauran marasa lafiyan. Kafin samu Bilal da Faisal suka dawo, anan aka bude hira,  suna cikin hiran Alkasim ya zo tare da wata yarinya. Kallon su Wasilah tayi kafin ta ajiye abin a ranta, tana kallon su har zasu fita ta Kalle shi.
“Ko zaki zo?” Kallon su Alman yai kafin ta dauke kai yana basarwa, domin baya jin akwai wani abun burgewa a tare da Alkasim. Bin shi tayi suka fita, tun kafin su yi nisa ta ce mishi.
“Ji mana!” Tsayawa suka yi.
“Yan mata ko zaki bamu wuri!” Kallon  wasilah tayi a wulakance ta ce mata.
“Kece wasilah Ishaq ko? Ai sami labarin ki, baby ba zan iya tafiya ni daya ba,  kayi maza kazo?”

    “Ok gani nan zuwa Aalimah” ya fada a dan kidime, kallon shi Wasilah tayi kafin ta ce mishi.
“Wacece ita?”
“Aalimah yar Boss dina ne”  ya fada yana kallon Yarinyar da bata wuce Rabi’ah ba.
“Ban gane ba yar ogan ka kenan? Koma me kasan yanzun zaman mu anan akwai matsala, ka tura DaÆ™ayyawa maganar mu”

“Gaggawan me kike yi? Idan kika yi hakuri ai abi kome a sannun ko, kawai idan na gama abinda nake zan Miki magana” kallon shi tayi kafin ta ce mishi.
“Kana nufin hmm! Ok” ta fada a hankali, gwanin ban tausayi.
“Idan baki manta ba, ai malam ta ce a cikin alamarin akwai matsala shine nake ganin ko zamu hakur…”

Wani irin murmushi tayi sannan ta kalli Yarinyar da suke tare ta cika fam, sai tsaki take.
“Ok thanks, Allah ya baku zaman lafiya” daga haka ta juya zata tafi Alman ta gani tsaye,  bai ce mata kome ba, dan ya ji abinda suke fada ya fito kamar yana waya ne.

   Tana shiga cikin dakin ya kalli Alkasim ya ce mishi.
“Ji mana!” Ya karasa gaban shi cikin wani irin taku, irin na Gayun da suka isa gayu.

“Wow! Kayi min abinda ya dace, da Kanwar naso, kasan Familyn mu muna kaunar abu me kyau shi yasa muke tattara su, kuma ko baka gaya mata ba, da nasan kai take so da tuni ba gaya mata ai kai kasa mu sadakayalla. So kayi min babban aiki bari ni kuma nayi sharan fagen” ya juya a hankali, ya koma dakin. Yana shiga ya dauki apple ya gutsira. Yana kallon ta.
“Ummyn na samu matar da nake so” .make shi tayi tana faÉ—in.
“Allah ya shirya min kai, amma baka jin magana”

     “Allah da gaske Ummyn wani ya jefar yace baya so ni kuma na dauka nace ina so sai na zama nayi laifi? Gata nan saurayin da take so yace ba yayin ta ni kuma na dauka ina yin ta my souvenir” kunya ce ta kama Wasilah ta shiga ban daki, ta bude ruwa, kallon kanta tayi a madubi, hawaye ne ya shiga zuba mata, shafa Fuskar ta tai tana jin wani irin daci a ranta.

    Tasan lokacin da ta fara karatu, alakar su tayi rauni. Amma ta dauki haka a matsayin daga shi har ita suna da abin yi ne, ba zasu yi wasa da damar su ba, ashe shi ran shi ba. Bata tab’a kawowa a ran ta zai wofatar da ita haka ba, kwalla ne ya zubo mata. Duk da haka basu da uba sama da Alhaji Muhammad a garin lagos dan shi ya bawa Bilal shawaran ya tafi da su,kuka take a hankali tana me dafe kanta, da ciwo a ce mutumin da kake so ya gaya maka baya son ka. Koda yake ai bai gaya mata ba, kawai ta bukaci su yi breakup ne kuma sun yi, yarinyar da ta gani bata kaita kyau da cikar halitta ba, kawai yana ganin tayi karama da ita ce hala.

Buga mata kofa aka yi, fitowa tayi tana goge fuskarta da mayafinta.
“Kuka kika yi? Ko Mazan duniya zasu  ki ni dai ina son ki kin ji yar abata me kayan dad’i”

          “Wannan ba abin wasa bane, abu ne na rayuwa da kuma daidaiton ra’ayi, don Allah ka rabu dani” ta fada tana me wucewa dani” ta fada tana jin kuka.
“Baki yi kama da wacce namiji zai saka kuka ba, me yasa zaki yi kuka yanzun? Karku yi kin ji ki ajiye kukan ki min daren mu na farko”
“Tir da halin ka” ta fada, tana barin wurin.

     Wato tun da Alman ya fahimci, Wasilah ba zata ba shi hadin kai ba sai ya shiga kunyatatta, da cikin jin dadi da nutsuwa, idan zasu fita sai ya kare mata kallo ya ce mata.
“Gaskiya na zaki fita a haka ba, kowa yayi ta kallon kirjina, bayan nawa ne da banza da wofi sun kare min kallo maza canza kaya domin wallahi idan aka yi auren mu hatta aikin nan barin shi zaki yi ki zauna kiyi reno na dan har yau ban fi karfin reno ba”

     Wani kallon banza take mishi ta ce mishi.
“Sai dai na saka ka a cikina. Na sake haihuwar ka.” Baki daya Wasilah ta gama rena Alman, gani take kamar ba wani abin arziki zai iya ba sai shegen cika baki. Kuma babban abinda yake kara daga mata hankali shine Alman akwai shi da farin jinin yan mata, wannan halin nashi ya kara sakawa taji baki daya baki daya ya fita mata a kai.

  Tun zuwan Bilal ya mika Junainah ga jirgin gombe, sannan ya kira Dr Hayat ya gaya mishi gata nan zuwa.

Alhamdulillahi Junainah ta isa gida lafiya cikin nutsuwa,

     **
Busan korea.

Kamar ba zan je Asibitin ba, na daure na shirya kallon kayan jikina nayi ina ji kamar kar na tafi, haka na daure na shirya na nufi waje na gayawa Umma zan tafi Rehab.

      Yoona ya kai ni, asibitin har muka isa. Koda na nufi dakin ta, murmushi nayi mata sannan na ja kujera na zauna ina kallon ta.
“Ya jikin?” Murmushi tayi sannan ta ce min.
“Da sauki yar akuya ya É—an tauren mu?” Murmushi nayi na Kalle ta daga dama har kasa, na tab’e baki ban bata amsa ba na ce mata.
“Da fatan kina jin dadin jikin ki?”
“Dan Ubanki da bana jin dadi zan ki ganni haka?
“Kuma haka ne tinkiya uwar tabele” na fada zan mike ta taso min dukar kafarta nayi, ta fadi zaune riko gashin kanta nayi tare da cewa.
“Don make me angry domin zan karya ki na zuba a kwandon shara lusara” na daket kanta nayi ficcewa ta, bin bayanta tayi da mugun kallo. Sai ta saka Rabi’ah kuka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button