NOVELS

WATA ALKARYAR COMPLETE NOVEL

Mai_Dambu

3/2/22, 12:24 – My Mtn Number: 52

“Sannan taya ma za a ce za ayi bikin baki wurin, don Allah ki tausaya min ki tausayawa rayuwar mu, karki sanya mu fara tsanar junan mu, don Allah ki tawo ayi kome dake, haka ne sai saka mu fahimci girman adalcin da kika mana” ta fada cikin matsanancin kuka.

    Tasan duk Yaranta daga Rahmah babu wata me zurfin hakuri kamar ta, kuma tunda ta iya rokonta ba makawa tana bukatar hakan ne.
“Ki bar kuka zan je nace” share kwalla tayi tana murmushin farin cikin, kafin ta ce mata.
“Mun gode Ammyn, ya ce zai zo shi da abokin shi, kuma za a turo kayan”

“Hmm! Za a turo kayan auren ki”shiru tayi bata ce kome ba, har dai ta gama gajiya da kunya ta fita ta wanke hannun ta.

  Bayan kwana biyu,
Sai ga kaya amma shi bai samu zuwa ba, daga Jama’are aka wuce da shi DaÆ™ayyawa, har da ita Ammyn inda ta sauka gidan Liman ana take gaya mishi an fasa auren Jamilah ga abinda ya faru. Shiru yayi kafin ya ce mata.
“Kiyi hakuri, shi yasa lokacin da aka zo niman auren Rahmah ni na musu iso zuwa wurin mai gari shi kuma ya saka aka nimo Badamasi aka yi maganar auren da shi.

   Alhamdulillahi suma iyayen Yaron dattawan arziki ne, koda suka zo sun yi abin ya kamata duk me hankali yayi sannan sun bukaci a basu auren basu buÆ™atar kome ita  Yarinyar suke bukata.”

    Kasa Ammyn tayi da kanta, hawaye na zuba mata, wannan wacce irin karamci ne haka daga Hajiya Atikah? Tayi imani da Allah aikin tane, taya ma zata dauki Yarinya ta kai musu babu kayan kome, kwanan su biyu a Daƙayyawa suka dawo bayan ta bawa Hajiya Zakiya kudi me yawa tace ayi duk abinda ya dace ayi dashi.

Sun koma Jama’are ranar laraba, ranar Juma’a,  Faisal yazo shi daya dan ya bar Bilal bai da lafiya sosai. Sun gaisa yake tambayar shi.
“Ina abokin ka?”
“Yana gida bai da lafiya.”
“Allah ya bashi lafiya”
“Amin Ya Allah”
Shiru suka yi kafin ya ce mata,
“Amma ba a Lagos zamu tare ba, naji Ance kuna komawa zaki mai da hankali akan karatu ne dan nan da sati goma sha biyu zaku yi exam, shine na cewa Ummin mu ayi bikin tunda saura kwanaki ne, idan yaso bayan bikin sai ki tare amma zaki zauna a can Abuja ne, Bilal ya saya min wani gida a kusa makarantarta ku”

   Sunkuyar da kai tayi tana wasa da kasa, kafin ta ce mishi.
“Toh Allah ya kai mu”
“Amin” haka suka yi ta hira, kafin ya kalli agogon hannun shi, ya ce mata.
“Ki dauki sakon Lubna yana bayan motar”
A hankali ya bude motar ta dauki kayan masu kyau, tun bata bude ba.
“Kinsan bikin biyu ne, Layinah Autar mu har da ita za ayi bikin”
“Alhamdullahi Allah ya nuna mana lokacin” ta fada a kunya ce,
“Rahmah” d’ago kai tayi ta Kalle shi a sace kafin ta dauke kanta.
“Don Allah wancan ranar a airport kin ga wani abu ne”  a firgice ta Kalle shi kafin ya juya zata koma cikin gidan.
“Idan baki ga kome ba me yasa kike jin kunya ta?”
Cak ta tsaya, ta lura Faisal bai da kunya, fita yayi a motar ya biyo har zauren gidan.
“Gaya min don Allah kin ganni ko?” Kura mishi ido tayi kafin ta ce mishi.
“Ban ga kome ba”

“Gaya min gaskiya” kamar kasa ta zage ta shige cikin shi, baki daya ya haifar mata da mugun kunyar shi.
“Ban ga kome ba wallahi” dan dole ya hakura, ya barta sannan yayi mata sallama, ta ce ya jirata abincin da aka musu,dama ba wani girki bane kayan snacks ne sai dambun nama, da sauran su haka ta juye mishi. Ya tafi da shi,

   **
JF Hospital.

Bargo Ummin ta lulluba mishi, cikin rawan sanyi ya ce mata.
“Ummi kara min” daidai shigowar Namir Adamu Abbas Jikamshi.

“Mazan fama kai ne a gadon Asibiti? Ummin mu ya jikin shi”
“Da sauki gashi nan zazzaÉ“i yake fama da shi”
“Jiya kaman likita ya gan shi ko?”
“Eh ga sakamakon gwaji da akayi” amsa yayi, yana kallon takardun. Zama yayi tare da cewa.
“Bilal me ke damun ka? Ko matsalar su Abbana ne?  Kasan yadda jinin ka ta haura? Zuciyarka tana gab da matsala fa”

“Babu abinda yake damu ba” ya fada tsabar yana rawan sanyi.

   Haka ya shiga duba shi, ya mishi allurai tare da saka mishi wasu a drip,  bayan ya saka mishi ya kara lullube shi.
“Zuwa an jima zazzabin zai sauka, Insha Allah da kan shi zai bukaci ya sha iska”

  “Toh Allah yasa”
“Amin”

Haka ya fita, cikin rashin kuzari yake tafiya har office din shi, yana shiga ya samu mahaifin shi, dauke kai yayi tare da É—aukar kayan shi yana had’awa.
“Namir ba zaka yi hakuri ba?”
Murmushi yayi tare da cigaba da aikin shi.
“Kayi hakuri mana, domin mutuncin ka da nawa nayi haka fa, idan yan jarida suka samu labarin daga baya kasan me zai zame min? Zai iya zame mana scandal fa”

“Scandal kace?  Abin kunya ko? TOH ina ruwana da shi? Ita nake so, ba wani abun ta ba.  Ita nake bukata ba rayuwar ta na baya ba, duk abu ne muhimmanci bana Manta shi me yasa ba zaka gane ita din abu ce da raina ke so? Yayi kyau”

Daga haka ya fita ya bar dakin office din shi,. Domin ba zai iya kula zantuttukar mahaifin shi ba.  Dan haka ya bar asibitin, ya tafi mashayan da yake zuwa shan barasa,  yana zaune, Zuhairah Kabir Tambuwal, ta zauna a gefen shi, kallon juna suka yi kafin kowa ya kama abinda yake.
“Me kike yi anan?”
“Kai Meye ya kawo ka?”
“Nazo shan Beer ne”
“Me too” ta fada tare da d’aga kwalba, yana lura da ita kamar ba yau ta fara sha ba, dauke kai yayi tare da  sha abinda yake gabansa.

    Yana lura da yadda take daukar caji, dan haka bai bi ta kanta ba, sai can wajen karfe tara na dare, lokacin ta bugu sosai, kama hannunta yayi dan shima ya bugu, amma ba kamar ita ba, ya fito da ita ya shigar da ita motar shi ya saka jakarta a bayan motar, ya dauke ta sai gidan shi, tun a motar take mishi iskanci. Bai kulata ba sai basarwa da yake yana shiga cikin gidan, nan ne fa yarinyar nan ta Haukace mishi.

   Dakyar ya shige da ita cikin gidan, tun a falon take kokarin had’e bakin su, ganin gata yarinya gata a buge bai taba kaiwa can ba, duk iskancin shi yana iya waje ne bai taba shi ba, sannan koda suke tare da Jamilah, tana barin shi ya latsata sosai, har sai sun tabbatar da sun nutsu, amma bai tab’a kai hannun shi ko saman maran ta ba, amma kirjin ta kan da bakinta sun san tsiyar da akayi da su.

      Yau kuma banza ta fado mishi, kuma yana da yakinin, har da Mahaifiyar ta akan hana shi auren Jamilah, dan yasan kome akan su. Dan haka ya d’aga short gown din jikinta, karo yayi da kyawawan cinyarta, zuwa saman cikin ta, kafin  ya dira akan kirjinta, anan ya shiga shagalin shi. Sosai itama duk da tana buge sai da ta biye mishi, suka shiga aikata masha’a.

    Sai da yayi yadda yake so da ita,kafin  ya fara ƙoƙarin isa kasanta, wani abu ne ya tsaya akan shi, dan haka ga fara gwada hannun shi, dake likita ne,.yana kaiwa wurin yayi maza ya ciro hannun, ya koma gefen ta yana kallonta, idanunta da suka bugu ta juya akan shi. Tana wani irin motsi. Share ya yayi tare da barin falon, bai ga dalilin da zai saka ya ci abinda wani yaci da gangan ba,.yasan na Jamilah kaddara ce, ba son zuciya ba. Zuhairah kan yasan halin su da son zuciya Yaran basu da hankali.

Karshe ban daki ya shiga yayi wanka tare da aman gidan da ya masa kabe-kabe a cikin shi.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button