BAK'A CE 1-END

BAK’A CE Page 71 to 80 (The End)

Da mamaki ta zaro ido, fitsarinta kuma? A wannan yar robar mai shegen kyau? Me za.a yi da fitsarinta? 

Tsaye ta yi tana dubansa da iyakacin gaskiyarta, sai dai gannin da gaske yake ya sakata fadin” to ka juya mana

Murmushi ya yi ya juya bayansa inda ta samu da sauri ta yi tana kallonsa dan kar ya juyo ya shanmaceta,

Kallonsa take har ya dauka ko kyankyami baya ji, ya ciro dogon abin dake cikin wata yar farar leda mai kabar kabar ya saka kan abin sannan ya dawo kusa da ita ya janyota jikinsa sukai tsaye su duka sunna kallon abin

Ita kallon da take dan ta ga menene? Me kuma zai yi bada da fitsarinta?

Shi kuwa jiran lokaci yake dan gannin result din test din

Bayan minti biyar ya dauko ya duba, 

Radau suka nuna kansu sanda biyu, wanda hakan ke nuna ciki ne jikin Agaishat,

Idannuwansa ya lumshe, can kasan zuciyarsa yake godewa Allah,

Aman kuma wani tsoron ta sani ya darsun masa, yana tsoron kar aje itama bata son haihuwar, dan haka sai ya yi shiru ya kamo hannunta suka fito daga bayin,

Bakin bed ya kwontar da ita, ya rankwafa yana gyara mata gashin kanta, sai wani bibinta da kallo yake fite da da, hakan ya sa du ta tsargu, 

A hankali ya mana mata kis a goshinta, sannan ya kai hannunsa kamar cikinta yake shafa , ya shafo wajen mararta ya saki murmushin da bata san ko na meye ba, sannan ya mike ya fice a dakin bayan ya dauke abin test din, yace da ita yana zuwa….

Kwonci tashi kayan Allah, 

Agaishat wajen wata biyar da aurenta da Wardugu,

Zuwa yanzu, koda sun yi fitinarsu da matarsa baya nuna mata , yakan nuna ya tafi gidan Walyn din da ta koma itama gida ne na gani na fada, sai ta yi baci ya yi zamansa abinsa,

Cikinta kam na tafia cikin nutsuwa, bai yi wani girma sosai ba, ya tasa dai, wanda Zuwan Gaishata garin da ta je ganninta ita take fada mata ciki ne da ita fa? Ta sha mamaki, ita kai, tana gannin cikinta na dan kara girma, bata jin motsin komai kuma, 

Kakarta kam dariya kawai ta yi, tana yiwa Anna tsiyar ta daina jin kunyar nan da take na yayan nata fa, domin su sun jima da sani, Ayya ta fada masu Wardugu ya rangada mata albishir din, a takaive dai ita mai dauke da shi ne bata san da shi ba, kai harta da baba Sofo ashe ya san da maganar, taimakon da yake bata na sha ashe dan cikin ne? (Domin kuwa alhamdulilah, baba Sofo na samun kulawa ta musaman, yana dan ciwoce ciwocensa na jikin tsufa, aman kuma hakan baya hanashi walwala da jin nutsuwar zama tare da wadinnan bayin Allah, ga Agaishat ba.a kwana biyu bata yi kira an bata shi a waya ba, koda bata zo ba, yana jin wani gurbi da ya rasa ya cike masa, yana jin kaunarsu tamkar ciki daya, Gukunni na zuwa ya taya shi zaman fada idan baya aiki, aukan yi shayi su sha, sannan su yi hirar rayuwa, inda Ba sofo ke bashi sirika na tsari)

Itama kunya ce ta ji kamar ta nitse kasa, ya Salam ciki? Cikin mijinta, bangonta, abin alfaharinta, yanzu Ayya ta san tana dauke da ciki take zuwa gidanta ta bararaje abinta?

Yo ita ba laulayi, dan zazabin dare dai take tabawa shima ba wani mai zafi ba, haba gaske idan ta je take samun kayan kwadayi, kuma wardugu na yawan kawo mata kayan kwadayi , 

Kanta kawai ta sada dan tsabar kunya, gashi ana cikin cuwa cuwar auren Mariama da docternta dan Nigeria, Fatimata kuwa da wani dan kasuwa mai sunna Muhamadu,

Walyn, a yanzu lamarinta, zan iya cewa da sauki, domin kuwa tana kare lamarin Ayya tun karfinta, 

Abu daya ne take fama da shi dai kishinta, har yanzu ba zata iya wani kishin kissa ba, gashi wace take haukan dan ita a garin, take zuba kayan, tana zubawa makadan kudin dan sunnanta ya kara dagawa fiye da na kishiyar tata bata ma san tana yi ba, domin kuwa fitar Agaishat fita ce ta idan ta kama, idan ka ganta waje zai kaita gidansu ne, wato gidan kakaninta, ko ya kaita gidansu, wato gidan Ayyanta,

A hankali ta ci gaba da rainon cikinta, sannan ta ci gaba da fuskantar lamarin mijinta, wani lokacin daga waje za.a kuno shi ya zo ya yi ta neman fitina, wai danma ciki ne a jikinta ya yi ta jajensa sai ta yi masa gum, idannuwansa su kade masifa kawai yake nema idan ta ki kula shi sai ya shiga mota ya bi cikin gari ko ya tarda walyn , ita kuwa har yanzu ta kasa gane lamarinsa sai ta biye masa ko ta hanyar korafin ita dan ya tsaneta ne yake mata haka, ko kuwa sakma ta mike ta maida martani, wani lokacin ya tumurmusheta wani lokacin ya mayar da ita tamkar doki ba abinda ya dame shi,

Cikinta na da wata shida aka yi auren su Mu.azam, nanma an sha darga domin cewa ya yi bata yi masa barka ba ko ta ji haushin Mu.azam ya yi aure?

Murmushi kawai ta yi masa sannan ta mike ta bara masa wajen, bafa wani laushi ko a kanta, danma tana cin albarkacin cikin jikinta sam baya gigin taba lafiarta ko ya yi mata fadan da zai sakata kuka

A haka aka yi auren yan matan Anna biyu, inda Ayya ta zama aminiya kuma kirjin biki, domin kuwa ita ta sada Mariama har garin iyayen mijinta kafin su daga ta damka amanarta, inda Agaishat ta yi ta fushin ba.a tafi da ita ba, harda kukanta, aman lokacin sai aka yi ta rarashinta domin kuwa ciki ya tsufa sai fitintinun masu ciki kala kala,

Cikinta nada wata tara da sati daya wani yamacin alhamiss suna tafiya da Wardugu a tsakar tankamemen gidanta ya rike hannunta suna dan takawa dan kafafuwanta su rage kumburi, da kuma yanda docter tace da ita su ringa tafiar kafa idan haihuwar ta kusa zata samu saukin nakuda,

Sanye take da irin kayan indiyawan nan riga da wando blue, manya ne sosai domin ba daidai da ita bane, tunda cikinta ua taufa suka zama suturarta , ciki take bulmuya ta yi ta yawa abinta, 

Hannunta rike da kasar da take sha a boye tana so ta sha tana tsoron ya gane abinda take boyewar su casu a wajen nan, ta ji ciwon bayan dake sandarta sai kara yawa yake,

Dan dakatawa take dan yi idan ya lafa sai kuma su ci gaba da tafia, yana mata labarin abin dariyar da yake gannin na dariya ne, wanda ita kuwa binsa dai take ta yi dariyar dan kuwa du abin wani fadansa ne da wani, wani rikici da suka yi dai da sauransu, du ba wani abin dariya saima abin tsoro da mamakin irin yanda fada ke saka shi nishadi da take,

Ji ta yi wani irin das das das tun daga bayanta yake sarawa har ya sauka kafafuwanta sannan lokaci guda cikinta ya wani irin hautsina ya rikide da wani irin ciwo tsakurw tsakure gefe gefe kafin ya garwaye ta rasa takamaiman indama zata ce yanai mata ciwon.

Da sauri ta tsaya, tana son dukawa aman ina, wani yawu ta ji a  bakinta na wuya mai wani taste daban, sannan wata zufa ta karyo mata,

Da sauri ta damko hannunsa da wani irin riko mai karfin gaske, hakan ya saka shi juyowa da dan sauri yana dubanta,

Yanda ya ga tana faman kaiwa gurfane ne ya saka shi tarota jikinsa yana mai tambayarta lafia? Menene??

Da kyar ta iya juyar da kanta ta ce” Wardugu , zan mutu, zan mutu,

Ido ya firfito mata kafin ya ce” ke, ba zaki mutu ba, …..

Yana fada yana dabarar yanda zai dauketa ne kar ya ji mata kuma kar ya jiwa abinda ke cikinta,

Da kyar ya sungumeta ya nufi motar da ta fi kusa inda yake ihun a bashi kys a bude masa gida,

Kanta kawai take juyawa, domin abin wani tashin lokaci guda ne ya yi mata, daga ya dan lafa sai ya kuma tashi, hakan ya sa a fili take fadin *ALLAHUMA LA SAHLA, ILAMA JA.ALTAHU SAHLA, WA ANTA TAJ.ANUL HAZNA, IZA SHI.ITA SAHLA* (ALLAH KA SAUKAR MIN KAWAR KWARAI AMINIYA SAMIRA LAFIYA , AMEN YA RAB),

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button