ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Siyama dake sallama a tsakar Gida ta jiyo kukan Jalila da Sauri ta karasa Inda take jin kukan nata
Tana kwance akan gadon Ummi ta hada gumi se kace tayi dambe da zaki ga hawaye a fuskarta,
se jujjuya kai take tana fadin
“A’a nima bazan iyaba Yaya Jawwad bazan iya temaka masaba nima zasu hada dani”
Subhanallah siyama tafada tare da jijjiga Jalila
A firgice Jalila ta farka daga mummunan mafarkin datake tana haki
“Jalila lafiyanki kuwa meyasameki? ina ummi?
Tun dazu na shigo nake sallama ba Wanda ya amsa me yasaki wannan kukan”
“Bakomai”
Tabawa siyama amsa
“Kamarya ba komai kalli fa yadda kika hada gumi ga kuka kinayi”
Siyama tafada tana nunata
Mikewa Jalila tayi ta tafi gaban mudubi
Ta kalli kanta taga yadda ta hada gumi ga hawaye, idonta har yayi ja kaman ta wani tana kuka
Wayarta ta ta dakko ta dawo inda ta tashi ta zauna
“Aminiya waime yake damunki ne akwai matsala ne?”
Girgiza mata kai Jalila tayi tana duba wayarta lamabar Yaya Jawwad tayi dialing bugu biyu ya daga sekuma tayi shiru tarasa mezata CE
Jalal ne ya katse shirun ta hanyar Sa wayar a hands free sannan ya yimata sallama
“Salamu alaikum warahmatullah sisyna yakike ya Ummi”
Ajiyar zuciya tayi
Alhamdilillah yana raye
“Me kikace?”
“Duk Muna lafiya ya maama da Nana”
“Muna lafiya sisyna, ya karatu”
“Yaya Jawwad”
Takira sunansa
“Na’am sisyna ya akayi?”
“Kana inane?”
“Akwai matsalane? yau weekends muna gida ina tare da yayanki Jalal ina ta fama dashi wai se ya tafi Dubai ya barni, in ya tafi kuma wai baze dawoba
Dan karamin tsaki Jalila tayi sannan tace
” to Yaya seme? kabarshi yaita tafiya daga nan har bangon duniya ya tafi ai gara hakama tunda baze karatu ba kaman sauran mutane ba seya tafi yayi abunda ya dace dashi kaima ka nutsu ka maida hankali akan naka karatun”
Cak ya tsaya da hada kayan dayake saboda yanajin duk abinda Jalila take fada saboda Jawwad a hands free yasaka wayar wannan Jarababbiyar yarinyar bazata fasa aibata shiba kenan
Shikam Jawwad saroro yayi yama rasa meze ce
Da kyar Jawwad ya hadiye yawu yayi gyaran murya
“Sisy bana gayamiki addu’arki Jalal yake bukata ba shima fa dan uwanki ne kidena fadan maganganu marasa dadi akansa kinji ko”
“To naji nadena ka gaida maama da Nana”
Haka dai suka gama wayar da Jalila
Jawwad ne ya kalli Jalal sannan ya kira sunansa da nufin yaba shi hakuri akan abinda Jalila take masa
Daga masa hannu Jalal yayi
” gara in bar muku kasar hankalinku ya kwanta hankalin kanwarka ya kwanta kar in lalata ka” yacigaba da abunda yake
“Jalal bahak…..
Daga masa hannu Jalal yayi
” no need to say anything “
“Aminiya wai bazaki gayamin meke faruwa ba”?
Siyama takuma tambayarta
” ke kin isheni nace miki ba komai amma kin isheni kibarni inji da abunda yake damuna!”
Jalila tayi Wa siyama maganar a hasale
Dan zaro ido siyama tayi
“Sorry Allah yabaki hakuri laifina ne danazo inda kike kuma na damu da damuwarki dama zuwa nayi in gayamiki dazu malam babba yace agayamiki akwai musabaka next week insha Allah”
Tana zuwa nan ta tashi tafita tabawa Jalila guri
Sam Jalila jinta take wani iri wannan wane irin mafarkai takeyine akan Jalal
A haka Ummi tadawo ta tarar da ita wani iri kaman Mara lafiya tana nuna mata abubuwan data siyo amma hankalinta baya kanta
“Baby waime ke damunkine?”
“Ummi marata ce take ciwo kuma na sha magani”
Dayake tana cikin period ta wayance da hakan
“Allah ya sawwake”
“Ameen”
Ummi ce tayi musu girkin dare
“Wai har yanzu marar ce tashi kici abinci ki kuma shan magani”
“Ummi na koshi da abincin”
“Baby kin fiye taurin kai shiyasa bana son rashin lafiyarki kin fiye gaddama tashi ko tea kisha”
Tea din kawai ta sha ta nemi guri ta nema ta kwanta amma fargabar yin baccin take saboda bata San mezata kuma gani ba
Se jujjuya mafarkan da tayi takeyi a zuciyarta dayake bacci barawone haka yayi awon gaba da ita dukda tarin fargabar da take ranta
“Karki bari Jalal yayi tafiyar nan in har yayi tafiyar nan rayuwarsa zata lalace fiye da da burinsu ze cika, Wanda abun ze iya shafar rayuwar Jawwad , ze lalace fiye da baya kiyi wani abu a kai Jalila kar ki bari Jalal ya tafi………..
TURKASHI
MORE COMMENTS MORE TYPING………
YAYINDA COMMENTS DINKU YAYI KASA ZAN DENA TYPING KULLUM
KUNA COMMENTS INA JIN DADI INA MUKU TYPING
????????????
KUNA BARI INA LALACI
LOVE U ALL
❤❤❤❤❤
INA ALFAHARI DAKU MASOYA NA INA GODIYA
❤❤❤????????????????????
????️????️????️????️????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????
_ABDUL JALAL_
(2020)
_WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)
PAGE- 15
PART 1
_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi
Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.
Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar
07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din
????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL
I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage
Aimin afuwa the page is not edited
-my first Novel-
Ni bazan iyaba wallahi, idan suka kashe nifa, niba abunda zan iya yatafi ina ruwana
“Ke Jalila wai meye hakane
Ba magana nake miki ba”
Tashi Ummi tayi taje ta jijjigata a firgice ta tashi tana rarraba ido
“Wai meyake damunki a yan kwanakin nan kusan kullum sekin tayar min da hankali in dare yayi ko dai gamo kikayi da Aljanu”
“Niba wasu aljanu kawai tsorata nake”
Jalila tafada tana ya mutsa fuska
“Au tsoratanne kawai, to tunda kawai ne kika kuma min kuka a cikin bacci bulala zan saka in zaneki ta shi kije kiyo alwala kiyi salla ki dau Qurani ki karanta Allah yasa kina Azkar”
“Ummi bana salla”
“To jekiyo Alwala kibiya Wanda kika haddace”
Ba musu taje tayo alwala tazo taita bitar Qurani da ka bacci kam gagararta yayi se dai juye²
Yauma kamar kullum haka ta tashi jikinta kaman Mara lafiya ko abincin kirki takasa ci ga idonta daya kumbura saboda rashin bacci Ummi kallonta kawai take dakinta ta koma ta nemi guri ta kwanta tayi shiru
(Karki bari Jalal yayi tafiyar nan in har yayi tafiyar nan rayuwarsa zata lalace fiye da da burinsu ze cika, Wanda abun ze iya shafar rayuwar Jawwad , ze lalace fiye da baya kiyi wani abu a kai Jalila kar ki bari Jalal ya tafi!!!)
Tas kalaman da akayi mata a mafarki suke dawo mata kwakwalwarta Wanda yayi dai² da wani mugun bugawa da zuciyarta tayi da karfi, kanta ya Sara
“Nashiga uku ni Jalila wannan wani irin bala’i ne meye hadina da wannan mutumin ake tsoratani akanshi wani tsautsayin ne ya kaini kano wanannan wani irin jarabane ana nema a haukatani why?”
Tafada tareda yin jifa da pillows din kan katifar ta yage bedsheet din kan gadon ta kifa kanta akan katifar
“Dan Allah ji abinda nake kamar mahaukaciya Ta Yaya zan hanashi tafiya ina nan yana can how? Be duba amincinsu da Yaya Jawwad yafasa tafiyar ba se ni da bama shiri to ni ya zanyi?
Kawai shirmen mafarkine kimanta kicigaba da harkokinki
Wani bangare na zuciyarta ya gayamata,
aikam ta yadda da abinda zuciyarta ta gayamata na ta manta shirmen mafarkine
Ga bacci a idonta kanta har ciwo yake amma bazata iya ba saboda fargabar inta kwanta me zata gani
Duk yadda taso ta manta takasa zuciyarta se bugawa take da sauri² hankalinta yaki kwanciya
” Nashiga uku ni Jalila meke shirin faruwa dani haka ya zanyine?
Ko ingaya Ummi me
Karki kuskura hakan be dace ba mussaman intaji abinda yayi miki bazataji dadi ba, wani sashi na zuciyarta ya gargadeta
Siyama ce ta fadomata a rai, dan haka da sauri ta mike taje ta wanke fuskarta tasaka hijjabi ta fito, ta tarar da Ummi tana saka a dakinta
“Ummi inaso zanje gurin siyama”
“Adawo lafiya kigaidamin da ummanta saura ki dade inkika dade kin kori gaba kinsan halina”
Gyada kai Jalila tayi ta fita ta nufi hanyar gidansu siyama