Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jalila ta kai Abinci part din Jawwad kaman dazu yanzuma Jalal yana nan amma bata kulashi ba be kulata ba ta ajiye zata fita, taga wani key holder akan center table da keys na mota a jiki dakuma wasu keys din, key holder din yayi kyau wani Dan Teddy ne a jiki me kyau, kai tsaye Jalila taje ta Sa hannu ta dauka, ta jujjuya shi yayi mata kyau sosai, tafara kokarin cire teddyn jiki, ita a tunaninta na Jawwad ne, Jalal ne yake satar kallonta yaga ikon Allah, seda ta cireshi tsaf daga jiki, tabar keys din haka ta mayar kan center table din ta ajiye, ta dau Dan Teddy zata fito Jawwad ne ya shigo dakin jikinsa a sanyaye sakamakon maganganun da Maama tayi masa
“Kinkawo abincinne”?
“Eh na kawo gashi can”
“Mungode sosai”
Murmushi yayi, hannunta ya kalla, yaga abin key holder din Jalal,
“Baby waya baki wannan”?
“Yaya sonake a jikin keys dinka naganshi”
“To wayace miki nawane?”
“To ai duk abunda yake dakin nan nakane”
“Dagaske”?
” eh mana duk abunda ya shigo cikin dakin nan yazama Naka”
Dariya Jawwad yayi “to na oga ne dafatan kin tambayeshi kafin ki dauka”?
Dan zaro ido Jalila tayi
” waiwa kake nufi”
Da ido ya nuna mata Jalal, Dan bude baki tayi
“Ni cirewa kawai nayi, na dauka nakane”
Kwaikwayonta Jawwad yayi
“Eyya na Yaya Jalal ne a tambaye shi tukuna”
Jalal yana jinsu yayi musu banza ya sakko ya fara kokarin zuba abincinsa salad din data hada ya bude tayi masa wani decoration yayi kyau sosai,, maida hankali yayi yafara zuba abincinsa
“Jeki tambayeshi mana?”
Jawwad ya maimaita, noke kafada tayi,
“Meyasa bazaki tambayeshi ba”
Dan tura baki tayi “ai nakane”
Jawwad ne yadan kalli Jalal yaga shi ta abinci yake, Jalila ta shammaci Jawwad tayi waje abunta da Dan Teddy a hannunta
A parlour ta tarar da Maama tana lissafawa Nana Atamfofi da less
“Yawwa Jalila zomuje tare, kayan nan zan kaiwa mommy Jalal”
“To shikenan Ku gama kirgawa”
Akagama kirgawa suka zuba a manyan leda suka dauka suka nufi gidansu Jalal
Shigarsu yayi dai² da fitowar Mummy daga part dinta, Dan bude baki mummy tayi, “yan mata saukar yaushe?”
Durkusawa Jalila tayi ta gaisheta ta amsa da fara a “kinzo mana Hutu kenan””
Nana tai farat tace”a a mummy ta dawo nan gaba daya”
“Masha Allah hakan yayi kyau, ya Maman naki?”
“Lafiya kalau ta bata amsa”
“Masha Allah toku shigo ciki mana”
suka shiga cikin parlour shima yasha gyara kaman parlour amarya,
kayan suka zube agabanta, dubawa ta shigayi dayake suna business sosai tsakaninsu da Maama
“Kai amma lesses din nan sunyi kyau, kafin akaisu bari Ilham tazo ta zaba, Jalila Dan kirawo Ilham tana dakin ta “
Ba musu JALILA ta tashi ta tafi dakin Ilham, tayi ruf da ciki tana jin music a wayarta, duk tasaka Bluetooth a kunnenta, tana bin wakar a hankali, tayi ruf da ciki tabada attention dinta akan waya shiyasa bataji shigowar Jalila ba
Bakin gadon Jalila ta karasa ta Dan leka wayar Ilham, hotunan Jalal, takewa wannan kallon kurillan,
Jinjina kai Jalila tayi tareda furta
“Yar wahala, kina nan kina shirme yana can yana shagalinsa”
Hannu Jalila ta kai ta girgizata
“To uwar soyayya kije ana kiranki”
Dan dagowa Ilham tayi ta kalleta a wulakance, jitayi kamar hannun Jalila na kamshin turaren Jalal zumbur ta mike tana kallon Jalila
“Meye haka? Kin shigomin ba sallama”
“Kina can kina ibadar dababu lada taya zakisan nazo”
Hannun Jalila ta kalla taga teddyn jikin key holder din Jalal
Kwalalo ido Ilham tayi ta kai hannu kan abun tareda fadin
“Wayabaki wannan aina Jalal ne”
“Kamarya waya bani? Dan na Jalal ne kuma shi kadai akayiwa? Kinji mace kinga ni cewa akayi kawai nakiraki”
“Inba nasa bane ya akai naji kamshinsa, kamshin turaren Jalal ne a jiki fa, kuma tabbas nasane”
“Au Jalal din har wani kamshi yake na daban, banda warin hayaki meyakeyi, kullum cikin zukar hayakin taba har wani kanshi yake”
Mikewa Ilham tayi tsaye tana kallon Jalila sannan ta nunata da yatsa
“Naga wannan karon kin karo wulakanci, kuma wallahi bazan saurara miki ba koni ko ke, tuntuni nagane take² ki, se yanzu nagane inda kika dosa, am ready for you”

Share please
More comments more typing……………………..
Love you all my fans really appreciate your comments and prayers
❤❤❤❤

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 30

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa

      -MY FIRST NOVEL-

Yatsan da Ilham ta nuna Jalila dashi, Jalila tasa hannu ta sauke yatsan Ilham
“Dukda Ban gane inda kalamanki suka dosaba, banga abunda nayi miki kike tada jijiyoyin wuya hakaba, sedai bansaniba ko kema Jalal yafara baki giyar saboda naga alama daga wannan maganganun naki, yanzu dai kije matar gidan tana kiranki”
Jalila na zuwa nan a zancenta tasaki hannun Ilham, tayi waje abunta
“Ina Ilham din?”
Mummy ta tambaya “nagaya mata amma naga kaman batajin dadine amma nagaya mata”
“Bata jin dadi kuma? “Meyasameta dazun nan fa tabar palour”
Ita dai Jalila shiru tayi,
Jalila na fita Ilham ta koma kan gadon ta zauna kanta kaman ya fashe ta rike kanta lallai ma wato Jalal har yayi sakewar da abunsa ze shiga hannun Jalila,
Wato Jalila tayi galabar fara soyayya da Jalal, kuma kalli yadda takemin kamar bata San metayiba to ni ina me hakan yake shirin faruwa impossible Ilham tafada da karfi
Muryar mummy taji tana kiran sunanta Dan haka da sauri ta kwanta akan gadonta ta rufe ido, cikin dakin Ilham mummy ta shigo ta ganta a kwance “ke Ilham meyasa meki”
Bata juyoba bata bude Ido ba tabata amsa
“Kaina kemin ciwo”
“To bazaki sha magani ba, se kizo ki kwanta”
“Nasha fa”
“To Allah ya sawwake, in bedena ba kiyi magana akaiki Asibiti dama kaya aka kawo nakeso ki dauka bari insa abarsu anan in kinji sauki seki duba ki zaba”
“to”
Shine abinda Ilham itace, mummy ta juya zata fita Ilham taraka bayan mummy da harara tareda yin kwafa, tana fita ta mike taje ta kulle kofarta tasa key ta dawo kan gadonta ta zauna “munafukan banza zanga bayanku daya bayan daya, gara in fara kauda wannan banzar yarinyar gefe tukuna, naga zakewarta tayi yawa inna bari tayi galaba, abunda ake gudu yafaru to shirinmu gaba daya ya rushe,”
Mummy ce tafito tace musu subar mata kayan anan zata aiko da Wanda ba a siyaba suka mike suka fito
Itakam Jalila mamakine ya cikata metayiwa Ilham takemata wannan maganganun harata na wani zatayi maganinta, lallai bata sanni ba kafin tayi maganina zanyi maganinta idan na gano metake kullawa
Nana ce ta Dan kalli JALILA
“Baby wai ko kunyi fadan da kuka saba ne naga da fara a kika shiga gurin Ilham amma kin fito wani iri ko akwai matsalane?”
“Bakomai me zatamin daze Sani bacin rai aitayi kadan”
“Nikam narasa meyasa ba kwa jituwa da ita”
Murmushi Jalila tayi
“Niba abunda yahadamu da ita kawai dai tanada saurin fushi ne”
“Kekuma kinada tsokana ba”
Nana tafada a tare sukayi dariya suka shiga Gida Jalal ne yazo ya giftasu yana waya,
“Bazan fito ba dan uwa yace, kar in sake in fito, dan haka yau ina gida kayi hakuri”
Dan shiru yayi sannan ya cigaba
“Wani mamaki zaka bani, nayiwa Jawwad rakiya duk nagaji,
Wai dole yau kakeso in zo abari se gobe zanzo kwana zanyi a gurin”
Jalila ce ta Dan tsaya yayinda Nana take kokarin Janta su tafi dan kwace hannunta tayi daga na Nana
“Yi gaba zan amsa wayane”
“Waya kuma waya kiraki a waya? Anfara kiran sallar magariba ki zo mu shiga basekiyi wayar a ciki ba”
“Ke dai kiyi gaba yanzu zan karaso,”
Wucewa Nana tayi abinta, yayinda Jalila tabi bayan Jalal, ta tsaya nesa kadan dashi amma tana jin meyake cewa
“Hannah kuma, Hanna ta fiye rigima, mezatayi a gurin nan da daddare in dai zata gurin nan bazanzo ba, dazu naga kiranta ban dauka ba, muna tareda Jawwad indai zata ganni a guri seta fitineni, nikuma banason shirme”
Shiru ya dan kumayi Jalila batajin me ake cewa daga daya bangaren
“Waiku meyasa kuka takura lallai senazo, taya zan taho karfe biyu na dare, ina laifin afara ten agama one
Anyway zanyi kokari in fito”
Karfe biyun dare mezeje yayi karfe biyu a wani guri shikadai
JALILA tai maganar a zuciyarta gyaran murya tayi Wanda hakan yasashi waigowa dukda duhu yafara amma yagane Jalila ce,
“Karfe biyun dareko zaka fita, Allah yatemake ka kafita, kai ko tausayin iyayenka bakayi, ga dan uwana kullum bashi da cikakken kwanciyar hankali saboda kai, yakamata ka tausaya masa”
Ta karaso inda yake ta miko masa dan teddy nan
“Ungo abunka kanwarka zatamin hauka dan taga wannan abun banzan a hannuna,”
Dan kurawa Jalila ido yayi, na yan sakanni bece komai ba kawai ya juya ya fita
“Yan wahala kai da kanwartaka Allah yayiwa Yaya Jawwad tsari da kai da fitinarka, dan kai Jarrabawane a rayuwarsa, ba dangin iya ba na Baba amma kullum hankalinsa ba akwanceba saboda kai kuma ko tausayinsa bakaji, wallahi in kaje gurin nan aka maka wani abu Alhakin Yaya Jawwad base barkaba”
Cak Jalal ya tsaya jiyayi kaman Jalila ta soka masa mashi a zuciyarsa
Girgiza kai yayi ya nufi hanyar gate,
“Allah yasa kar ya FIta”
Jalila tafada a fili son jikinta nabata wannan fitar ba alheri bace akwai abunda aka shirya yi masa
Ta wuce cikin gida ta tarar da Halima a zaune a palour tana kallo “Anty Haleema kallo ake haka anyi sallar magariba fa”
“Wallahi inkikacemin Anty kunya kike bani”
“Kunya kuma saboda me nake baki kunya”
“Ina aiki a gidanku, kumafa watakila kin girmeni amma kidinga cemin Anty”
Dariya JALILA tayi “haba leemart har aure fa kikayi kuma kin haihu kin cancanci a girmamaki”
“Wannan sunan yan gayunfa dakikace yanzu”
“Ya miki dadine?”
“Eh wallahi”
“To shikenan, bari inje inyi salla kema kije kiyi, inzo kibani labarin kauye”
“To shikenan bari intashi”
Jalila taje ta tarar da Nana tana salla dan haka ta ajiye wayarta itama taje tayi alwala zata tada salla tana kallin Nana tana idar da salla ba Azkar ba komai ta shafa fuskarta, taja gefe ta dau wayarta ta kama sana’ar tata ta chatting
Har Jalila ta idar da sallah tayi Azkar dinta, sannan ta waigo ta kalli Nana “waini Nana mekike a cikin wayar nan haka ne ke idonki baya miki ciwo”
Dariya Nana tayi “lallaima wani irin ciwo kuma ba wani ciwo”
Gyda kai Jalila tayi ta tashi ta tafi dakin halima itama ta idar da sallar tana ninkin kaya
“Yawwa gani nazo zo kibani labarin kauye”
“Kekam Jalila meyasa kikeson kauye”
“Wallahi inaso inje amma bantaba zuwa ba kauye yana birgeni”
“Tab kinemi tsari da rayuwar kauye, yanada dadi in kayi dace da mutanen kirki a garin
Amma kinganni nasha wahalar zaman kauye ga maraici ga rashin gata, ina Jss 2 akamin auren dole da dan hakimi ga jarabar kishiyoyi da yayansu, uwargidansa ma takusa Sa ar kakata”
“Zaro ido Jalila tayi Sa ar kakarki, keko waya aura mikishi”
“Kanin mahaifina Jalila, matan mutumin nan su hadu sumin duka, shi kansa jibgata yake a haka nasamu ciki ga laulayi, amma babu tausayi ranar aikina senayi, wanke² ma kawai na gidan nan bala’i ne balle girki”
“Subhanallah kuma kanin mahaifin naki yasan halin dakike ciki”
Jalila tayi maganar kaman tayi kuka
“Wallahi yasani Jalila, an azabtar dani a rayuwata maraici babu dadi, danginmu suna kallo amma babu me iyayi masa magana”
Jalila kaman ta fashe da kuka saboda tausayin halima, nan Takara jinjina rikon Amana irin na abban Jawwad ko mahaifinta yana raye tasan iyakar dawainiyar daze da ita kenan, bata taba kukan rasa wani abuba saboda maraici”
Tana wannann tunanin JAWWAD ya kirata
“Baby atemaka da coffee please”
“To Yaya ban yan mintuna”
“To shikenan”
Ta kashe wayar ta kalli halima “leemarta bari inje in hadawa Yaya coffee, amma zan dawo, ko in taho miki dashi” girgiza kai halima tayi
“A a ni ban iya wannan ciye² yan gayun ba, kedai sekin dawo”
Murmushi Jalila tayi ta fita
Murmushi halima tayi itama gaskiya Jalila tanada kirki yadda take sakin jiki da ita bata ISA ta zauna Inda Nana takeba mussaman insuna tareda Ilham, taita zigata tayi mata rashin mutunci,
Kokuma taita sakata aiki kaman baiwa
Jalila tahada coffee ta tafi ta kaiwa Jawwad, wannan karon shikadaine a parlour
“Yawwa sisy nagode sosai, dama Jalal ne ya kirani yacemin yanaso shiyasa nasaki, nagode”
“Kutmelesi JALAL nema ze sha, wallahi Dana San shine bazan hada ba” Jalila tayi maganar a zuciyarta a fili kuma hanyar fita tayi ta koma cikin gida
Jawwad ya kaiwa Jalal coffee din jiyayi yafi na ko yaushe dadi
“Waya hada tea din nan?”
“Jalila ce, ita nasa ta hada maka, kasan Nana in batasa kanta abu ba se a hankali, JALILA ce komai kasata ba kyuya zatayi maka a nutse”
Jalal be kuma cewa komaiba yacigaba da shan coffee dinsa, seda ya kammalla tukuna sannan Jawwad ya dauki flask din ze fita, har yayi hanyar fita ya dawo,
“Jalal dan Allah karka fita ko INA yau kazauna ka hutawa ranka karkaje gurin shan giyar nan yau dan Allah”
Yakarasa maganar da sigar rarrashi, tausayinsa ne Yakama Jalal gaskiyar kanwarsa datace ba dangin iya ba na baba amma kullum hankalinsa a tashe saboda ni
Ajiyar zuciya yayi, “ba inda zanje insha Allah, ina gida”
“Are you sure” Jawwad ya tambayeshi, murmushi Jalal yayi masa “am sure, bros ba inda zan fita yau”
“Thank you very much, Allah ya tashemu lafiya”
“Ameen” Jalal ya amsa, sannan Jawwad ya fita ya koma gida
Bayan fitar Jawwad ne, Jalal yafada tunani,
Tabbas Jawwad ya dade yana dawainiya dashi, kullum bashi da kwanciyar hankali saboda shi, abokansu da Dama suna kyamarsa basa mu’amala dashi saboda halinsa, iyaye dayawa sunyiwa yayan su Katanga tsakaninsu da Jalal saboda miyagun halayensa, amma Jawwad be guje shiba tabbas wani abu yasamu rayuwarsa hakkin Jawwad baze barshiba
“Mummy why kalli halin da danki yakeciki, ga rayuwar danakeyi mummy saboda ke ga yadda ake kyamata mummy why meyasa kika aikata haka a rayuwarki, abun Yakoma kaina”.
Haka Jalal ya dinga surutai hawaye nafita daga idonsa, ” Thank you very much Jawwad bazan iya biyanka wannan kaunar ba”
Ya furta a hankali
Jalila bayan takoma cikin gida bata koma gurin halima ba Ummi takira a waya suka sha hira take tambayar Ummi yaushe zatayi tafiyar ne?
“Se nan da wani dan lokaci, akwai shirye² danakeyi sonake sena gama”
“Ummi wani shirye² kuma, nifa sonake kije ki dawo, in dawo gida mucigaba da zama tare”
“Hmm Jalila kenan in na tashi tafiya kafin in tafi zanzo kano muyi sallama”
“Yawwa Ummina har naji dadi wallahi dama inkinzo ki daukeni mutafi tare”
“Mutafi ina, bana son rigima, ai bahaka mukayi dakeba senaje na dawo tukuna semuje tare”
“To shikenan ummi, Allah ya kaimu lokacin”
“Ameen ya Allah, ki gaida mutan gidan naku”
“To ummi zasuji insha Allah”
Haka sukayi ta hira da Ummi kaman bazasu dena ba kafin daga baya sukayi sallama, Nana ce ta shigo da kwano a hannunta
“Babyn ummi dawa kike wayane?”
“Nida ummine wallahi”
“Au ai na dauka da wani gayen kike waya”
Dan zare ido Jalila tayi “rufamin asiri gaye kuma”
“Eh mana karya kike dai kice baki da saurayi”
Hararta Jalila tayi “au tambayata ma kike”
“Au tuba nake ai namanta, na dauka an masa kishiyane”
“Nana kinfiye shirme, mekike da kwano haka”
“Abinci zanci”
“To aci lafiya ni kwanciya zanyi”
Jalila ta bude akwatinta ta dakko kayan bacci, Nana ta kalleta
“Jalila nayiwa Abba magana za acanza mana wardrobe, semu maida kayanmu ciki, naga kayannaki dayawa”
“Kin doramasa nauyi, dakin bari se inbar wasu a akwatin ba ai duk dayane”
“Hmm Jalila kenan kome zakice nidai nagaya masa”
Jalila tasamu guri ta kwanta,
Bacci ya gagari Jalal se tunani yake, Jeje ya kirashi a waya ta dinga ringing amma yaki dagawa
Ya kalli wayar yaga yadda sunan Jeje ke yawo akan screen din wayarsa,
Yasan batun party nan ze masa tsaki yayi
“Kaine mafarin komai”
Yayi tsaki ya kashe wayarsa gaba daya ya zame ya dan kashingida ya runtse idonsa yana tunanin abubuwa da dama dasuka wuce a haka bacci barawo ya dauke shi
Washe gari da asuba bayan Jalila ta idar da sallar asuba, tanaso ta danyi tilawa amma taga Nana na kokarin komawa bacci dan haka saboda karta takuramata seta koma palour ta fara karatunta cikin sautin muryarta me dadi, seda gari yayi haske sosai sannan ta tashi da nufin shiga kitchen Halimace ta fito ta kalli Jalila
“Barka da safiya sayyada Jalila”
“Rufamin asiri inani ina zama sayyada Jalila dai”
“Haba wannan karatu haka, kuma daka fa kikayi dama nice na iya”
“Kema zaki iya in kinaso”
Halima ta dan zaro ido “dagaske?”
“Dagaske mana”
“To ta yaya?”
“Yanzu dai bari mu kammalla aikin gida semuyi maganar”
“To shikenan bari inje in fara gyara kitchen din kafin kifito”
“To shikenan bari in maida sallayar nan daki”
Yadda ta tabar Nana haka ta dawo ta tarar da ita, a dukunkune tana bacci a cikin bargo, dan girgiza kai Jalila tayi ta aje hijjabin ta da sallayar ta fito palour, a kitchen suka hade da halima suka cigaba da aikin breakfast dinsu suna hira, koko da kosai sukayi
“Anya mutan gidan nan za suci koko da kosai, ko kowa zeci wannan abokin Jawwad din, me Suma a tsartsaye, gashi duk yayiwa gashinsa kala, gashi jarababbe da kyar yaci wallahi dan ya fiye iyayi,”
Halima tayi maganar tana kallon Jalila
“Wai Jalal kike nufi?”
“Eh shi wallahi, jarababbe ne, har fargabar kaimusu abinci nake”
“Aikuwa sedai kar yaci din, yatafi gidansu mana yaci, ai naga gidansu ma akwai abincin”
Dan zare ido halima tayi
“Tab ba ruwana,”
Haka suka gama girki suka gyara ko ina
Se bayan karfe Tara na safe mutan gidan suka dinga tashi daya bayan daya
Sunyi farinciki da ganin abincin da akayi kowa yacika cikinsa suna murnar wannan sakakken abincin da Jalila tayi musu
Karfe taran nan ta nufi part din Jawwad kai Abinci amma seta kai na mutum daya iya na Jawwad banda Jalal

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button