Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Ilham se safa da marwa take, a cikin dakinta, ta rasa inda maganganun Jalila suka dosa, tace ita ba son Jalal take ba, amma itama tanada kuduri akansa, kuma inyaci karo da nawa, to tabbas zata rusa nawa, koda tazo nan a tunaninta seda ta zare ido, ta rusa nawa burin saboda nata muradin, to ko ta san menene shirina ne, to amma tayaya zata sani bayan ko Nana bata saniba,
Dakko wayarta tayi, zata kira yaseera, sekuma ta fasa, dole in dau mataki, bazanyi wahalar banza tsawon shekaru ina kallo wata sakarya ta rusamin shirina ba, gara tun yanzu in rusata ita danata shirin, ta mike da sauri ta nufi dakin mummy, tana zuwa ta tura kofar dakin, ta sameta tana waya, taje kusa da ita ta zauna, tana jiranta tagama,
Seda mummy tagama waya, sannan ta kalli Ilham tace
“Ilham ya akayine, naganki wani iri haka kaman mara lafiya”
Fashewa tayi da kuka, ta fada kan cinyar mummy
“Mummy wallahi nakusa mutuwa, in har yaya Jalal be aureni ba, zan iya mutuwa, Mummy ina sonshi, dan Allah asaka ranar aurenmu,”
“Yi shiru kiyi hakuri, kinji nima naga kamatar yin hakan, kila in kika aureshi ma ya shiryu sanadin haka, yanzu kidena kuka, bari daddynku ya dawo, muga me yakamata ayi, amma karki kuma zance zaki mutu saboda shi, aini na miki alkawari, indai ina raye Jalal shine mijinki, indai nina haifeshi baze taba auren wata mace inba keba, kidena kukan nan haka ya isa”
Wata irin nannauyar ajiyar zuciya Ilham tayi, tareda yin murmushi a boye, a fili kuma tace
“dan Allah mummy asaka da wuri, ina tsoron ya auri wata baniba,”
“ki kwantar da hankalinki, shi kinga alamar ma zeyi soyayya da wata, ko kina tunanin akwai wadda zata aureshi a haka, aini kingama min komai da kikeson Jalal a haka, dan haka bari daddyn sa ya dawo, zamuga yaushe yakamata asaka”
Ilham ta riko hannun mummy,
“Nagode sosai, mummy”
“bakomai, kidena kuka”
Hannah zaune akan fararen kujerun dake gurin, fuskarta dauke da wani arnen glass dayake barazanar cinye fiye da rabin fuskarta, ga barima da tasaka a akan dogon hancinta, se tauna chew gum take, tana fuskantar Jeje,
“Hanna daga gurin oga KB nake, kuma yace lallai wannan itace damarmu ta karshe akan Jalal, yazama dole muyi yadda zamuyi mukammala aikin nan,” hannah ta dan nisa ta cire glass din fuskarta, sannan tace
“Idan ban mantaba shekaru uku zuwa hudu muna aikin nan, duj wani salon makirci, da kisisina ba wanda banyi ba, tunda nafara bariki, bantaba ganin dan bala’i ba kamar Jalal, ban taba haduwa da mutum me azabar taurin kai ba kamar Jalal, babbar nasarar dana samu a rayuwa akansa shine, a labarin daka bani, bayan sauyawar Jalal, ina cikin jerin matan daya sake dasu, har yake shiga harkata, amma naiyi iya kokarina alakarmu ta wuce haka amma yaki yadda, ni yanzu bani da wata dabara,
Nagama nawa, bansan meye shirinka ba”
“Hakane Hannah, nasan kinyi mana aiki, kinyi iya yinki kinmana kokari, abaya a koda yaushe ina galaba akan sa amma yan shekarun nan, nafara ganin sauyi a tareda shi, koda nagama aikina akan Jalal, sena tabattar da nayiwa Jawwad babbar illa shima, saboda tsawon wannan shekarun shiya hana cikar burin mu, Jalal yanajin maganar Jawwad fiye data uwar data haifeshi, wadda ita ta haddasa komai, “
” Baka ganin ina aka cutar da Jawwad ba a masa adalci ba, shi meye nasa aciki “
” yana da laifi Hanna kuma dole ya karbi hukunci, yanzu ki tsaya ki saurareni”
“ina jinka”
“a gurin birthday din damuka shirya masa komai ze kare,” hannah ta kalleshi sannan tace
“bangane mekake nufi ba”
“zaki gane ne Hannah, nagama shirya komai, kinsan meze faru?”
“No seka fada”
“kamar yadda muka shirya, shabiyun dare zamu fara gabatar da taron, a cikin cake din dazamu bawa Jalal ke zakiyi wannan aikin, zaki saka kwaya, a dai2 inda za a bashi, saboda sonake ya bugu ya fita hankalinsa yadda baze iya komai ba, za sakama a lemon da zs sha, da zarar ya fita hayyacinsa zamu dauke shi, mu kaishi wani gurin, kekuma zaki gabatar da aikinki”
Dan tsaki Hannah tayi
“Ni gaskiya ba a haka naso aikin yazo ba”
“to ya za ayi se hakuri, tunda shi dan taurin kaine, zamu nuna masa munfishi iya bariki”
Wayarsa ce tafara ringing, jeje ya kalli Hannah “Dan halak shike kirana”
Tai murmushi tace
“Pick it”
Dagawa yayi yasa a hands free
“Allah ya temaki, mazaje, namijin duniya sha gwagwarmaya, namjin damusa bakason raini” Jalal yace
“Kai Jeje ya isa haka, magana nakeson yi maka akan maganar partyn nan”
“ok inajinka”
“Munyi magana da Jawwad, dan haka dole a maida shi eight Jawwad yace baya son ya kai karfe shabiyu in bahakaba baze attending ba, dan haka ina so amaida shi eight pm, saboda inason Jawwad ya kasance a gurin”
What!!!!!!! Jeje yafada da karfi yana mikewa tsaye

Share please
More Comments More typing………………………..

Akodayaushe kuna raina masoya comments dinku ke bani karfin gwiwa da sani nishadi, amma in naga ba kwa comments sosai, se inji kamar inkoma posting duk sati ????????????????????
Ina godiya da adduoi Allah yabar kauna

????️????️????️????️????️
[9/23, 10:45 PM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  49

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

A har kullum ina jinjina da godiya ga masoya wannan novel nawa, comments dinku da addu oinku ina jin dainsu matuka, ina godiya kwarai dagaske,
Domin sharhi, gyara, kokuma shawara a nemeni ta what’s app akan wannan lambar wayar
07063065680
Ina godiya matuka Allah yabar kauna

Ina amfani da wannan dama, domin mika ta a ziyyata ga yan uwa mutanen zazzau da dukkanin al ummar musulmi, na rashin sarkin zazzau
Alhaji shehu idris, ina fatan Allah ya jikansa yasa mutuwa hutuce, dashi da dukkanin al ummar musulmi da suka gabacemu
Allah ya rahamshesu in tamu tazo Allah yasa mucika da imani

          _My first novel_

Jalila na zuwa dakinsu ta kife akan gadonsu,
“Nikam Jalila nashiga uku, wace kaddara ce ta kawoni kano har nasan Jalal ne, wanda har rayuwarsa take neman hanamin tawa nutsuwar, Ummi dan Allah in kina raye duk inda kike ki dawo, nagaji da zaman nan ina cikin damuwa, Allah ka temakeni, kabani ikon jarraboyina na rayuwa”
Ta karasa maganar tan zubda hawaye, tayi me isarta sannan ta mike ta duba wayarta ta kira Hanan, seda ta kusa katsewa sannan Hanan ta daga, tana dagawa tace
“Tace afuwan ranki ya dade, ina wankane, ya jiki Jalila?
” Da sauki Hanan, ya Baba na dasu Abdallah “
” Baba baya gari yana bauchi, Yaya Abdallah ma haka dagani se mummy, ya jikin kinji sauki”
“jiki Alhamdilillah na warke ganima a gida”
“masha Allah, nakira Jawwad nace ya hadani dake amma se yacemin ba kya kusa, siyama ma takiraki bata shiga ki kirata dan Allah”
“zankirata Insha Allah”
Hanan ta ce
“nikan Jalila meyasameki haka har ya kai ga kisamu stroke ko wani abu na damunki ne?”
Se Jalila taji kaman Hanan ta sosamata inda yake mata kaikayine, batasan lokacin da hawaye yafara fita daga idonta ba
“Hanan ni meye ma baya damuna, ko kinsan cewa a halin yanzu sati biyu kenan, bansan inda ummi takeba ko a raye ko a mace ban saniba”
“Kamar yaya baki saniba, naje gidan fa ranar dazata taho kano, tacemin zatazo kuyi sallama zata wuce garinsu, kuma kice bakisan inda take ba”
“Hanan tunda Ummi ta tafi, mukayi waya da ita, wayanta be kara shiga ba anyi trying har angaji, karshe aka kira Abba aka gayamasa, wai wani me mota ya bigeta, kuma ya dauketa ya tafi da ita, bawanda yasan ina ya kaita, kotana raye kota mutu bamu saniba”
“Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Jalila meyasa baki gayamin ba tunda wuri, kuma angayawa”yan sanda”?
“Hanan Abba yana iya kokarinsa amma har yanzu ba labarin Ummi ni harna hakura na fawwalawa Allah komai”
“kiyi hakuri Jalila, nasan abun da wuya a gurinki, amma mucigaba da addu a, insha Allah za a ganta, in daddy ya dawo zan sanar masa koda wani abu da za a iyayi akan matsalar, kiyi hakuri, Jalila insha Allah ummi tana raye za a ganta”. Hanan ta ke rarrashin Jalila yayinda itama take zubarda hawaye, har cikin zuciyarta takejin matsanancin tausayin Jalila,
“Addu a ina nan inayi hanan, sedai kuma ina bukatar taku adduar”
“Insha Allah zan tayaki addu a, kinji kidena damuwa sosai, kar wani ciwon yakamaki”
“Karki damu kanwata na fawwalawa Allah komai, shi ze bani mafita”
“Masha Allah haka akeso queen muzama masu karbar kaddararmu a duk yadda tazo mana,” domin kokarin kauda damuwar Jalila, se tace mata “nace ya gidannaku, ya mutuminki?”
“waye kuma mutumina?”
“kinfini saninsa Jalal mana”
“Yana gidansu”
“kai queen har yanzu kina masa rashin mutunci ko?”
“ko jiya ma seda mukayi, yau kuma wannan mahaukaciyar kanwar tasa tazo zatamin hauka, wai ita alallai son Jalal nake, wai in ban fita harkar saba seta sani kuka kiji fa,”
Dariya Hanan tayi, sannan tace
“queen J nasanki da kafiya, dan Allah karki bari Ilham tayi nasara, kizama silar shiryuwar Jalal, u can do it, kibata mamaki, kamar yadda kika bani”
“ke nina fara gajiya, gashi jarababbe, ga taurin kai gashi mugu, itakuma gani take sonsa nake ko uwar me zanyi da wannan makakken, dan wahala daga ita harshi”
“A a dai, banda cika baki, daga baya kizo kina zare ido akansa”
“Kut me kike nufi, mezanyi da wannan Allah ya rufamin asiri”
“Oho dai inda rabon an jone ne…. Jalila bata bari takarasa ba ta kashe wayar tareda fadi” ji muguwa zatamin mugun baki, ta Allah ba taki ba”
Daga haka Jalila ta Mike ta fito palour don samun dan abunda zata ci, Maama tana palour a zaune tana kallon Aljazeera,
Jalila tace “Maama sannu da gida”
Kallon Jalila tayi ta dauke kai ba tareda ta amsa mataba, har Jalila zata wuce kitchen, Abba ya shigo, ya dawo da wuri yau, da alamu ko mantuwa yayi, Jalila tace
“Abba sannu da zuwa”
“yawwa Jalila ya jiki ya gidan,”
“lpy qalau Abba”
Maama tacewa Abba “Sannu da zuwa”
Banza yayi mata da nufin shigewa dakinsa, Jalila tai farat tace “Abba, Maama na maka sannu da zuwa fa, bakace komai ba”
Abba ya wayance da “Yawwa maman Yara, yi hakuri banji bane” ya wayance kar Jalila ta gane, sannan yace “Jalila dan kiramin Jawwad, kice ina son ganinsa, a dakina”
“To Abba bari inje”
Jalila ta tafi part din Jawwad, Jalila na fita Abba ya shige part dinsa ya bar Maama a palourn, binsa tayi itama, tana kuka, Abba ya kalleta
“meye haka zaki biyoni kina kuka, se yaranki sunce wani abun nayi miki”
“Meyema bakayimin ba ina tabinka ina baka hakuri amma kaki kulani, sati kusan biyu kana gaba dani, kaki saurarata haba Abban Jawwad, dan Allah kayi hakuri, kadena fushin nan haka”
Kukan dayaga tanayi seta bashi tausayi,
“Zainab, komenayi miki ke kika jawa kanki, nima ba a son raina naimiki hakaba sedan in nunamiki kuskurenki, akan abunda kikayimin,”
“kayi hakuri hakan baze kuma faruwa ba Insha Allah”
“Zainab kenan indai halinki ne ba wanda ban saniba, bana tunanun wannan maganar har cikin zuciyarki”
Jalila tana zuwa part din Jawwad ta tarar suna fada da Jalal,
“JALAL dan me zasu shirya maka wani birthday, dacan ma aibasu suke hada maka ba, bayan kasan mutanan nan bana kirki bane, su kaika wani guri su hada maka birthday kuma ace shabiyun dare haba Jalal kayi tunani mana,”
“Jawwad ya kakeso inyine? Sokake ince musu bana so ko inki zuwa, ko wa akayiwa haka baze ji dadi ba, mene a ciki abu na lokaci daya ayi a watse, basu taba hadamin ba, wannan karon sunmin se ince banaso, kana ganin idannayi hakan na kyauta, shikenan bance kaje dole ba fa, dama zuwa wannan gurin da daddare ai da irina ya dace ba da kai ba”
daga haka Jalal ya juyo fuuu ze fita, da sauri Jalila ta bashi hanya kar ya bigeta, bayan ya fita ta shiga palourn, Jawwad yanemi guri ya zauna yayi shiru
“yaya Jawwad ya dai?
” Bari Jalila, Jalal ne yake neman ya cazamin kwakwalwa, kullum fatana in janyeshi daga jikin wannan miyagun abokannasa shikuma yana kara shige musu, “
” Meya farune? “
” Wai an hada masa birthday, se sha biyun dare zasu fara har gari ya waye, kuma a baya tare muke hadewa muyi dashi kuma a gida amma wannan karon wai su suka shirya masa, nasan kwana zasuyi shan giya, nace kar yaje kuma yana neman yayi fushi, seyaje yai tayi ai, am tired da halin Jalal”
Sosai taji tausayin yayan nata, taga kokarinsa ma tsawon wannan lokacin yana tareda Jalal, duk da miyagun halayensa, ga shi da wuyar sha’ani amma haka Jawwad yake tare dashi, kuma tasan wannan fushin na dan lokacine, dole se daya ya nemi daya, ta numfasa tace
“Yaya Jawwad ai be kamata kayi fushi ba fa, tunani yakamata kayi, tsawon shekaru suna tareda shi basu taba cewa zasu shiryamasa birthday ba se wannan karon, kuma ma wai se tsakiyar dare zasu fara, baka tunanin wani abun suka shirya akansa? Bakayi tunanin suna da manufar yin hakan ba? Kn kayi fushi kace yaje yaitayi, kaga sunyi galaba zasu kara janyeshi, shikenan yazama nasu gabadaya”
Shiru Jawwad yai yana kallon Jalila
Taci gaba da cewa “Kayi tunani yaya na, dan uwanka ne fa, u have to think”
Ajiyar zuciya yayi “Hakane baby kema kinyi magana, amma yanzu me yakamata inyi”
Jalila aranta tace yawwa, nima ga dama ta samu,
A fili tace, “Yaya dole ka shiga cikin lamarin nan, kawai ka yadda da maganar birthday din nan, ka lallabashi kasashi a maida partyn kaman daga karfe ta kwas zuwa goma, sannan dolenka ka halarci gurin domin sakamasa ido, in takama har abokanan ku da yanuwa ku gayyata, hakan ze hana faruwar wasu abubuwan, karfe goma nayi, ka janyeshi daga gurin, yanzu kayi hakuri ka sakko, har ya gaya maka shirye2 da sukeyi, kaima seka san shirin dazakayi, amma inka barshi ya tafi shi kadai jikina na bani akwai dalilin dayasa suka shirya hakan, sun san babu wani dan uwansa daze yadda ya bishi guri irin wannan karfe shabiyun dare”
Murmushi Jawwad yayi, tareda yiwa Jalila salute
“Gaskiya baby kina da tunani me zurfi, hankalina be kai kan hakan ba ni, gaskiya nagode, zan jarraba insha Allah”
Murmushi Jalila tayi
“nifa aikoni akayi, Abba yace kazo yanzu”
“To shikenan ina zuwa”
A ranar bayan Jawwad yaje kiran Abba, ya je yanemi Jalal suka shirya, yace masa ya yadda, zeje birthday dinsa amma gaskiya zasu gayyaci mutane, dan haka sedai a canza lokacin daga shabiyun dare zuwa karfe takwas, Jalal yace ya yadda.
“Jeje wannan ce dama ta karshe dazan baka, a wannan karon banason asamu kuskure, dukda tsawon shekarun nan kayi aiki tareda ni, kamin duk abunda nake bukata to wannan karon, sonake komai ya kare, sonake a wannan lokacin komai yazo karshe, karka bari wannan shirin ya rushe, “
” Oga kb baka da matsala, munyi iya kokarinmu gurin ganin hanyoyin dazamubi domin gabatar da aikin cikin shiri, burinka ze cika, a wannan ranar zamuyi yadda zamuyi muga mun karasa wargaza rayuwarsa, “
Wanda aka kira da oga KB ya gyara tsayuwa yai ajiyar zuciya
” shikenan ina jira zan saka ido inga kokarin ka, a wannan karon, aje acigaba da shiri,”
” Shikenan oga, wannan karon komai zezo karshe”
Daga haka sukayi sallama,
Hannah na gaban dressing mirror tana kwalliya, Jeje ya kirata, seda ya kira sau uku tana kallon wayar sannan ta dauka
“Hannah ina kika shiga ne inata kiran wayarki, ya za ayi mu hadu ne?”
“mu hadu kuma, akwai matsala ne?”
“eh haduwar tamu tanada mahimmanci sosai, akan shirunmune, yanzu haka daga gurin oga KB nake, akwai bukatar mu hadu”
“To zanzo, muhadu inda muka saba”
“To shikenan sekinzo”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button