Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Ya mutsa fuska Jalila tayi
“Ke kullum zancenki aure²”
“To ai shine cikar mutuncin ya mace nidai fatana kirike mutun cinki a rayuwa Jalila kizama ya tagari abar Alfahari, kuma kizama garkuwa ga mijin dazaki aura ko ya yake,”

“Insha Allah ummina bazan baki kunya ba”
Ummi ta cigaba da cewa
“sannan kirike zumunci da yan uwanki Jalila kar abunda mahaifiyarsu da danginta kemana yasa ki gujesu wannan shine abinda mahaifinki yaita gayamin kan ya rasu”

“Naji amma bazan kuma zuwa kano ba in sun damu dani su suzo inda nake”
Dan zaro ido Ummi tayi
“Meyasa?”

“daf nake da wataran in wankawa Yaya Mairon nan mari wallahi,”
“Jalila ni ban koya miki wannan tarbiyyar ba, duk abinda hakuri bebaka ba rashinsa baze Baka ba”
“To Ummi tuba nake”
Ta fada tana mikewa tsaye

” ga wannan azzalumin shima Dan giya yadda ya dinga cin zalina bazan kuma zuwa kano ba”
Tayi maganar a hankali
“Me kikace ?”
“Ba komai Ummi, cewa nayi siyama bata zo nemana ba tunda na tafi bamuyi waya ba”
Tafa Dan kar Ummi ta gane me tace
“Tazo amma jiya da safe kafin Ku iso seda takuma zuwa nace mata baki dawo ba”
Murmushi Jalila tayi tareda cewa
“Allah sarki Aminiya”
Jalila tafada tana murmushi

Allah sarki babyna kin makara komawarki kano yazama dole Ummi tayi maganar a zuciyarta

Sallama akayi Ummi ta amsa Jalila kam bata tsaya ba data ji me sallamar ta fito da gudu daga dakin suka rungume juna dame sallamar
“Aminiyata nayi missing dinki”
Tureta siyama tayi ta Dan hade rai
“eh shiyasa naga kullum semunyi waya, nakiraki ba kya dagawa duk cikin missing din nawane”
A hankali Jalila tai mata magana
“Sorry aminiya Akwai labari”

Gyda kai siyama tayi ta Shiga suka gaisa da Ummi sannna ta fito suka koma dakin Jalila,
Dakin da dashi da babu kusan daya a gurin Jalila Dan komai Nata yana dakin Ummi se dai in sunyi fada seta koma dakinta kokuma in kawayenta sunzo

Suka shiga suka samu guri gefen katifar dakin suka zauna
“Bari Azumi baki San meyafaru bane amma ni kaina nayi missing dinki”
“Wallahi kika kuma cemin Azumi tashi zanyi in tafiyata ya za ayi a samun siyama ki dinga wani cemin Azumi kamar wata tsohuwa”
“Yi hakuri aminiya siyama na dena”

“Kin temaki kanki, wato kikaje kano kika tare kin manta da batun haddar islamiyya, gashi baki ba da uzurinki ba kinsan malam nazeeru ba afuwa
Waima ya akayi kika dawo Ummi tace min se hutun school ya kare zaki dawo”

Jalila ta nisa
“Kinga yanzu bar batun malam Nazeeru nasan yadda zanyi dashi”
Jalila ta kwashe kaf abunda yafaru zamanta a kano ta gayawa siyama ciki hada dramar su da Jalal,
Jin siyama take kamar Yar uwata ta jini basa boyewa juna komai
Jalila tacigaba da cewa

“Siyama bazan kuma zuwa kano ba,”
Jalila ta fada in a serious tone

” aikuwa ke zuwa kano ya kama zaman Kaduna banaki bane”
Siyama ta bata amsa

“Azumi ki kiyayeni dagaske nake bani ba kano”

” kina kuma cemin Azumi zan dinga cemiki matar Jalal”

“Allah ya kiyaye, ya za ayi in gayamiki magana kina Neman jamin bala’i Dan giyane fa, naji bazan kuma cemiki Azumi ba amma meyasa kikace dole in koma kano”
“Yanzu a ce yaya Jawwad ne yake abinda Jalal yake kikaji abinda Ilham tace zuba ido zakiyi kenan??”

“Allah ya kiyaye Yaya na ba irinsa bane bahaka muke ba
Narasa dalilin dayasa ya mannewa Yaya Jawwad”

“Aminiya babu Wanda yafi karfin kaddara”

“Siyama abinda Jalal yake ba kaddara bane son zuciya ne”.

 Jalal ne kwance akan wani makeken gado ya tada kai da hannunsa yana ta baccinsa cikin nutsuwa fuskarsa tayi fes kaman Wanda yake jinya, gashi ya rame sosai

Wata matace da Wasu mutane a bayanta suka shigo dakin da Jalal yake kwance, suka zagaye gadon da yake duk sun rufe fuskokin, su matar tasaka kaya tundaga sama har kasa ta rufe ko ina da bakaken kaya
Hannunta ta mika baya daya daga cikin mutanen dasuka zo tare ya mikomata wata zukekiyar wuka se kyalli takeyi
Ta zo kan Jalal ta saita cikinshi da tsinin wukar nan ta daga wukar sama

Share please

More comments more typing………………..

Proud of u my fans wannan page din barka da salla ne

????️????️????️????️????️
️[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  14

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

     -my first Novel-

“Karki caka masa, dan Allah
Innalillahi wa inna ilaihi raji’un!!!”

Shine abinda Jalila tafada da karfi ta farka daga mummunan mafarkin da take Wanda ya kasance tsakiyar dare
Da gudu Ummi ta yanke sallar da take ta taho kan gadon ta dago Jalila
“Lafiya me yasameki Jalila,?”
“Bakomai Ummi mafarki nayi”
“Kinyi adduar kwanciya bacci?”
Gyada kai Jalila tayi alamar eh
“Alwala fa”
“Itama nayi Ummi”
“Jeki sake alwalar sekizo ki kwanta”
Mikewa Jalila tayi taje ta yo alwala ta dawo ta kwanta tayi shiru tana kuma tunanin mafarkin da tayi
A hankali Ummi ta zo ta rungume Jalila tana mata
addu a, amma har yanzu kirjin Jalila bugawa yakeyi da sauri²
Washe gari da safe suna karyawa, amma hankalin Jalila yana kan mafarkin da tayi jiya Ummi ta lura da ita dan haka, ta yanke shawarar tambayar Jalila mafarkin da tayi take ihu cikin dare

“Jalila mafarkin me yasaki ihu cikin dare jiya”?
“Ba komai”
Jalila tabata amsa

“Kaman ya ba komai kin firgitani”
“Ummi ni dai nasan nayi mafarkin tsoro amma na manta me nagani”
Kallonta Ummi ta yi
“Baby kenan adinga addu’a dai”
“Inayi ai Ummi amma zan kara insha Allah”
“Yayi kyau kici abinci kidena wannan tunanin”
Gyada kai Jalila tayi ta Dan cakali abincin ta bari
Uniform din islamiyyarta ta dakko tana gogewa, amma duk kokarin ta, ta cigaba da harkokinta tana tuna mafarkin nan se gabanta yayi mummunar faduwa
“Subhanallah”
Shine abinda Jalila take fada in ta tuna mafarkin, haka ta karasa gugar tasaka uniform din islamiyya tana zaman jiran siyama ta karaso su tafi islamiyya
Qur’anin da Daddyn Jalal yabata ta je ta dakko tasamu guri tazauna tana kallonsa tana shafawa se jujjuya shi take a hannunta
Sallamar Siyama ta ji amma bats motsa daga inda take ba Siyama suka gaisa da Ummi a tsakar gida
“Ummi ina Jalilan take?”

“Tana cikin dakinta yau narasa meyake damunta yau tun safe tana daki”
“To Ummi bari ingani kinsan ta wani lokacin se a hankali”
“Aikam halin Jalila ai se hakuri”

Dakin Jalila ta shiga ta tarar da ita tana ta jujjuya Qur’ani a hannunta
“Aminiya lafiya dai yau kuwa,wannan Qur’anin fa me kyau, kice har babban guzuri kika taho mana da shi”

Ita dai Jalila ba tace mata komai ba ta mika mata
“Masha Allah gaskiya yayi kyau box din da yake ciki ma gwanin sha awa bari in sashi a Jaka mutafi da shi Islamiyya munyi sabon Al Qur’ani

“Bani”
Jalila tasaka hannu ta karbe Al Qur’anin daga hannunta Jalila

“wannan ba na zuwa islamiyya bane kallonsa kawai zan dinga yi”
“Kamar ya “?
” kamar yadda nagaya miki”
“Allah yabaki hakuri naga yau tambotsai kikeji”
Jalila bata kuma kulata ba ta dauki hijjabinta ta saka ta maida Qur’anin cikin cover dinsa ta adana shi
Suka fito
“Ummi zamu tafi”
Siyama tayi maganar tana risinawa
“To adawo lafiya Allah yayi Albarka”
“Ameen Ummi”
duk wannan maganar da ake Jalila batace uffan ba
Har sunkusa fita Ummi tace
“Ke madiga ina taki Jakar makarantar?”
“Ban gan taba sena dawo zan duba”
Tafada tana sunkuyar da kai
Girgiza kai kawai Ummi tayi sukuma suka tafi

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button