Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

A kwana a tashi malam shehu Allah yayi masa rasuwa, sun shiga matukar damuwa da tashin hankali haka akayi zaman makoki kowa ya watse.
Rayuwa tacigaba a haka malam imam be taba tunanin sunemi wani daga danginsu ba, yana ta kula da yaransa , yakuma siyan gidajen kusa dasu ya hade a cikin gidansu.

Usaman da Aliyu suka girma da matukar kaunar junansu, gasu masu matukar biyayya duk da kasancewar su maza amma daga kan shara gyaran gado wanke² bawanda basu iyabaan Usman yafi Aliyu hakuri, shi
Aliyu akwai kafiya da taurin kai sannan yana da zafi, halin babansu ya dakko, gashi shine karami amma in ya dau zafi sedai Usman ya kyaleshi amma duk da wannan halin nasa kaf kayan gidan nan shi yake wankewa ya goge sannan yana matukar son yayannasa amma wataran in kaga yasa Usman a gaba yana masa fada seka dauka shine babba
(Ashe JALILA ba a banza ta dakko ba)

shidai malam imam kullum zancensa be wuce
” Ku rike junanku Ku rike zumunci, kunga bayan imu IMU bamu da wasu dangi duk sun watse wasu sun mutu Ku rike junanku Ku nemi ilimi ko bayan ba raina karku yada zumunci”

Kwanci tashi asarar rai Usman yagama makarantar secondary ya shiga Jami’a yake karantar engineering,
Bayan ya kammalla jami’a ne aiki be samuba ya dawo Gida ya zauna yake dan bin babansa kasuwa, ana haka ya hadu da wata yarinya Zainab da farko dai suna mutuncine kawai kafin daga baya abin yakoma soyayya,
Lokacin daa malam Imam yasamu labarin Usman yana zuwa tadi gurin yarinyar ya kirashi yayi masa nasiha yace tun wuri in yasan ba aurenta zeyi ba ya dena zuwa gurinta

Shidama Aliyu be tsaya iya karatu ba yana taba kasuwanci
In yafita abinda yasamo se yabawa Dan uwansa yace yafara Tara kayan aure tunda ya fuskanci yana matukar son zainab,
Duk randa Aliyu beje makaranta ba haka zewuni Neman kudi ba abunda zeci a ciki haka ze dauka ya bashi,
Sannan dayake mutane dayawa sun San Aliyu saboda yana da baki ba kaman Usman ba salihi ne kaman mairo, Aliyu ya dinga shiga yana fita domin yaga danuwansa yasamu aiki amma abu yafaskara kai kace shine yake nemawa kansa aikin
Shekarar da Aliyu yasamu admission, babansu ya dauki kudin
Registration ya bashi amma daya tashi se ya hada kudin da Wanda ya dinga Tarawa ya tafi yaje kasuwa Yakama shago aka zuba takalma ya dankawa Dan uwansa yace gashi nan ya dinga juyawa yasamu yayi aure
Dafarko Usman kin amincewa yayi seda yaga Aliyu yadena kulashi, yadena cin abinci tare dashi yayi fushi sosai sannan ya yadda ya karba

Malam imam yace aikuwa badi se dai kanemi naka kudin kashiga makaranta, we da Aliyu yabata shekara biyu be fara makaranta ba saboda yaga kasuwancin da ya kafawa yayansa ya bunkasa

Duk wannan abun baya hana in Usman yayi masa laifi ya zauna ya kare masa masifa, amma beta ba yimasa gori ba.
Shekara ta zagayo Aliyu sannan ya Shiga Jami’a
Usman ya cigaba da kula da shago yasamu Sana’a yafara core ransa saga batun samun aiki

Ahaka har Allah yasa Usman ya auri Zainab aka ware masa bangarensa a cikin gidan yasata a ciki, tana zaune da mairo lafiya saboda ita Sam bata da hayaniya Dan haka Zainab bama Shiga harkarta take ba balle kyautatawa ko akasin haka ya Shiga tsakaninsu.
Allah ya Albarkaci kasuwancin usman, aciki ya dinga tallafawa karatun Aliyu dakuma iyayensu da girma ya cinmmusu,

A kwana a tashi ba wuya a gurin Allah, matar Usman ta haihu ta haifi da namiji, aka sakamasa sunan Aliyu suke cemasa Jawwad, Zainab taji haushi ga mahaifinta memakon ayi mata kara a saka sunanshi se a wani saka sunan Aliyu
Aliyu yayi murna da haihuwar JAWWAD dakuma karar da dan uwansa yayi masa kullum yana tare da Jawwad, yaronma yana matukar kaunar Aliyu Jawwad, soyayyar da Aliyu yakema Usman Yakoma kan Jawwad,
Jawwad yana da shekaru biyar cif, Aka tura Aliyu bautar kasa kwara state yaji babu dadi sakamakon rabuwar dazeyi da gida gakuma dansa JAWWAD dayake matukar kauna

Haka Aliyu yayi shirin tafiya yayi sallama da mutan gida iyayensa sun masa nasiha sosai akan ya kula da Kansa da addininsa, Usman beji dadi ba ya Shiga damuwa sosai, saboda shi lokacin da yayi NASA bautar kasar a kano yayi beyi nisa da Gida ba.

Haka Aliyu ya shirya ya tafi kwara, wani babban kamfani aka turashi kamfanin yakasance mallakin masarautar garin Wanda ya kasance na construction ne na gine² dakuma tituna

Aliyu yaga mutane daban² wanda suke da banbancin addini da al’adu da zaman takewa na rayuwa

Aliyu ya hadu da wani bayerabe a kamfanin me suna Abiola Wanda ya kasance kuma hadimi ne a cikin masarautar garin dukda banbancin addininsu amma tasu tazo daya shiyake zagawa da shi gurare a cikin garin

In Baku manta ba kusan halin Aliyu da shige²
Dan haka yace yana so abiyola ya Shiga dashi gidan sarautar yaga yanda take, haka akayi ya dauke shi ya Shiga da shi cikin masarautar ya dinga nuna masa abubuwa, haka ya dinga kallonsu wasu iri saboda yanayin saraautarsu yayi daban da masarautar kano

Wasu abubuwan sun kayatar dashi wasu kuma sun bashi haushi haka abiola ya dinga bashi labarin
masarautar da abubuwan data kunsa ciki kuwa hada labarin shalelen masarautar wadda akan a batamata rai gara abatawa sarkin saboda tsananin kaunar da sarkin yake mata

Sarki yana matukar kaunar yarinya nan, shikam Aliyu duk surutun nan da abiola yake besan me yake cewa ba saboda ya shagala da kallon abubuwan kayatarwa da suke a masarautar,
Wani part suka karaso kai bakace a Nigeria ne ba ya hadu karshen haduwa an kawata shi da abubuwan zamani da kawatuwa
“Nan kuma inane?”
“Ai nan shine bangaren yarinyar danake gaya maka jikar sarki ce, bangaren shalelen gidan ne”

“Ehenn mushiga inga mene a ciki mana”
Zaro ido abiola yayi “sokake in kwana a kurkuku baza ja min wahala ba iyakacin mu nan”

“To meye a ciki gani fa kawai zanyi”
“Dan Allah kabari ka zo mutafi kaga akwai masu tsaronta Dan haka kazo mu tafi”
Da kyar abiola ya shawo kan Aliyu ya yadda suka tafi.
Abiola ne durkushe a gabanta, ta hakimce tana cin kayan marmari
Tayiwa hadimanta umarnin sutafi subata guri
Sannan ta mike zaune sosai
“Abiola”
Takira sunan shi
Ya Dan kalleta ya maida kansa kasa

“Waye wannan Wanda kuka shigo da shi dazu?”
Gabansa ne yayi mummunar faduwa ya tsorata, nan da nan gumi ya rufe shi ya kama in’ina
“Abiola bafa abu me wahala na tambayeka ba kawai na tambayeka waye shine
Ina kallonku dazu ta saman bene kuna jayayya waye shi? Daga ina yake? Mekuma ya zo yi nan”?

Da kyar abiola ya hadiye wani yawu ya daidaita nutsuwarsa Ya dan suka da Kansa yace
” your royal Highness Dan bautar kasane an turoshi kamfani domin yayi aiki sunanshi Aliyu daga kano state yazo nan”
A kidime ta kalleshi kana nufin musulmine
“Eh bahaushe ne kuma musulmi”
Gigicewa ta danyi tare da bashi umarnin ya tafi seta nemeshi
Nan ta Shiga sintiri a gurin
Da karfi tai shouting
“Impossible!!!!!!”
Wanda ya janyo hankalin masu yi mata hidima ,kafin su an kara……..

Wata sabuwa

Share please
More comments more typing……………

Love u all Abdul jalal novel fans
????????????

????️????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  12

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button