Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

To kome ze kasance in ummi ta koma garinsu?
Wace rayuwa Jalila zatayi a kano?
Ya makomar rayuwar Jalal?
Waye Jalal ?
Meze faru da Jalila zamanta a kano?
Meye alakar Jalila da Hanan da suke kama?
Tskanin Jeje dasu Ilham suwa ke nasara akan Jalal
Dama sauran tarin tambayoyinku Ku cigaba da bina sannu a hankali domin samun amsoshinku
Daga alkalamin (daddy’s girl)

Share please
More comments more typing……………….

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  29

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
Ummu hanif really enjoy u comments and prayers Allah yaraya mana hanif ya bar kauna ????????????

         -my first Novel-

Tsayawa Jalila tayi daga inda take a tsakanin flowers tana kallon su Jawwad Ilham ce takarasa shigowa gidan
Su Jalal ke kokarin shiga mota Ilham ta danyi sauri ta je gabansu
“Yaya Jalal ina zaka ne?, inason zamuyi magana da kai”
Dama tunda tafara suspecting Jalila ke son Jalal ta dena kula Jawwad, yarasa me yayi mata

“Yaushe kika zama uwata dazaki ce kina son magana dani, kokuma yaushe kikazama ISP da kike tuhumata ina zani”
Jalal ya tamvayeta
Dan tabe baki tayi sannan tafara magana cikin shagwaba “two minutes kawai Dan Allah”
Bude mota yayi ya shige ya batta a gurin kaman gunki
Jawwad ne ya kalleshi, “haba bros Dan Allah fa tace, ka saurareta mana kasan mezata gaya maka”
“Indai wannan yarinyar ce babu wani abu me amfani dazata fada, komai nata daga shirme se hauka, bawani abun hankali a lamuranta”
Ya karasa shigewa motar ya kulle kofa ya batta a tsaye
Jalila daga inda take tana jin abunda suke cewa mamakine yacika Jalila tun wancan lokacin har yanzu Ilham ba ta dena son Jalal ba kuma har yanzu yana wulakanta ta amma tana manne dashi, tirkashi Allah kayi mana tsari da wahalalliyar soyayya dama wani mutumin arzikin ne takeso da da sauki amma Jalal wannan Dan wulakancin uban shaye²
Wayar da Jalila ta tabaji Ilham tayi a wancan zuwan nata ta tuna
“” ZANCIGABA DA HAKURI HAR LOKACIN DA BURINMU ZE CIKA AKAN JALAL DA MOMMYNSA””
Jalila bata manta ba wannan sune abunda taji Ilham tafada shekaru biyu dasuka wuce,
“Lallai akwai wani abu a kasa ba a banza Ilham take jure wannan wahalalliyar soyayya ba”
Ringing din wayarta ne ya fargar da ita daga dogon tunanin data tafi, lambar Siyama ce da sauri ta daga seda suka sha hira, takira Ummi ma suka gaisa sannan ta mike ta koma cikin Gida
Dakinsu ta nufa don aje wayarta tana shiga ta tarar da Ilham da Nana suna hira kuma dai ga dukkan alamu hirar akan Jalal ne, cikin dakin ta shiga tana fadin
“Juliet ta Romeo kokuma ince laila majnun, ya labarin soyayyar takune, domin labarin soyayyar nan akwai kayatarwa”
Jalila ta karasa maganar tana zama a gaban Ilham tareda yimata murmushi
Hade rai Ilham tayi kaman taga mutuwarta tareda tsurawa Jalila ido na wani lokaci, JALILA ma kallonta take kafin daga baya tace
“Manyan yan mata a cikin garin kano wannan kallon fa”
Wani mugun kishine ya tokarewa Ilham ganin Jalila takuma girma ta kara kyau, maganarta ma gwanin burgewa, Nana ce tai farat tace “Ilham Jalila fa ta dawo kano da zama, tabar garin Kaduna, anan zata cigaba da zama damu”
Ras!Ras!!Ra’s!!! Ilham taji gabanta ya fadi
“Ta dawo kano da zama?”
“Eh mana munkara yawa”
Dagawa Ilham gira Jalila tayi
“Ko ba kya farinciki da zuwana in koma”
(Mhmm kaman ba Jalila data gama kuka akan zuwa kano ba kunga harta ware tafara sana ar Neman magana ????????)
Wani matsiyacin kallo Ilham takewa Jalila aranta take fadin
“Lallai yarinyar nan muguwar Yar rainin hankali ce ga yadda take pretending kaman ba wani abu a ranta game da Jalal”
A zahiri kuma cewa Nana tayi
“Kinga mubar zancen nan mayi wataran, in mun sake haduwa”
Tai maganar tana yinkurin tashi tsaye riketa Jalila tayi
“No baza ayi hakaba ina lefin kice in baku guri, sha zamanki ai Jalila ba bakuwar zafi bace”
Jalila ta tashi tsaye ta bar musu dakin
Ta koma Kitchen tayi wanke² ta gyara kitchen din ta dawo parlour tana gyarawa, sallama akayi ta amsa wata budurwa ce wadda bata fi Sa arsu ba dauke da bagcco a hannu ta
amsawa Jalila tayi tareda yimata sannu da zuwa, yarinyar
Ta kalli Jalila tace “ina mutan gidan ne?”
“Suna ciki wani abunne?”
Jalila ta tambayeta
“A a dama dawowa nayi”
“Kokece Halima”
“Eh nice”
“Allah sarki sannu da zuwa karasa suna ciki”
“To nagode”
Dakinta halima ta nufa taje ta aje kayanta ta fito domin fara aikace² taga kusan an gama komai
Jalila ta kalleta “kije ki huta mana dagani kinyo tafiya”
“A a kaida ba Hutu kazo ba ina batun Hutu”
“Jikin Dan Adam yana bukatar hutu, ni nagama komai na dauke miki aikin yau”
Suna cikin haka Nana ta fito ita da Ilham, Nana ce ta kalli halima “sarkin biki, suna, ko mutuwa, se yau kinje kinyi zamanki a kauye ko”
“Wallahi bahaka bane Nana ni dince na danyi jinya”
“Haka dai kika iya kin barni aikin Gida kaman ya kasheni”
“Kai Nana Dan Allah wani irin aiki kaman ya kasheki ina aikin anan”
Jalila tafada tana hararan Nana
“Kenima wallahi in Yar aikin mummy ta tafi bana iya wannan wahalan tuni nake sawa a sallamesu a canza wata bana son shirme”
Ilham tayi maganar tanayiwa Halima kallon banza
Jalila kuwa kwashewa tayi da dariya a ranta tace kaga Yar masu Gida hada sawa a kori me aikin a fili kuwa cewa tayi
“Halima kyalesu na dauke miki aikin yau jeki sha zamanki”
“Mtseww shirme kawai”
Inji Ilham, “nice ma ke, akan shirme” Jalila ta bata amsa
“Enough please narasa wannan rashin jituwa a tsakaninku, Ku indai zaku hadu sekunyi fada, wuce muje”
Nana tafada tana tura Ilham
“Muje zuwa zangane abinda kike kullawa ne Ilham narasa inda kika dosa,”
Jalila tayi maganar a zuciyarta ta nufi dakin maama, da sallama ta shiga Maama ta amsa mata da kyar amma dayake Jalila ta iya siyasa se ta nuna kaman bata San abinda Maama take mata ba, ta karasa kusa da ita ta zauna “Hajiya Maama hutawa kike? Me za a dafa miki yau”
“Kinga ban saki ba balle Abbansu Jawwad yace daga zuwaanki an fara takura miki”
“Haba Maama wani irin takura, aikin Gida ai dolene ga ya mace ba batun takura”
“Kinga ga kitchen din nan jeki abinda kika gadama”
Maama ta karasa maganar cikin kosawa”
Mikewa Jalila tayi ta fito ta bata guri, ta nufi kitchen, ta tarar da halima tana kokarin dora abinci tare sukayi komai da Jalila sukayi girkin suka gama suka gyara kitchen din Jalila tanayiwa Halima gyare² a wasu abubuwan
Yayinda Nana tana daki a kwance tana chatting Jalila ce ta shigo ta sameta “Nana gaskiya mijinki ze sha fama”
Dan kallonta Nana tayi
“Kaman ya?” “Kallifa tunda garin Allah ya waye daga chatting se bacci haba Nanancy gaba fa akeji ba yanzu ba”
“Jalila kenan in Allah ya nufi ka huta kawai ka huta, kema ke kikasa kanki, wannan wahalar shikenan mutum baze huta ba”
“To naji tashi ki kaiwa Yaya Jawwad Abincinsa, in munyi salla se muci namu”
“Ba inda zani, in yanason ci in sun dawo daga yawon yazo ya dauka”
“Kai Nana Yaya Jawwad din?”
“Eh shidin, ina zuwa ze fara Sani aiki yana min masifa, bakiyi kazaba, wannan ba dai² bane, ga Yaya Jalal ma yaitawa mutum wani gani² mistake kadan seyace bazeci abincin ba, kuma in beciba Yaya Jawwad ma baze Ciba, shiyasa Halima ce take kaimasa itama haliman in basu gadama ba in ta kai bazasu Ciba, Yaya Jalal yafi kowa wannan tsirfan, kokuma yanzu susaki dafa wani abincin, shiyasa ko yazo ya dauka da kansa,ko halima ta kaimusu, bana son wahala”
“Tabdijan indai Yaya Jawwad ne meye a ciki se in masa amma Jalal kam yayikadan”
Dariya sosai Nana tayi,
“Tab cakwakiya Ashe kuwa zakuiyi fada da Yaya Jawwad”
“Ke ni bari in wanka in yazo se ya shigo ya dauka,abincin”
“Kin temaki kanki kema seki huta”
Se bayan sallar la’asar sannan su Jawwad suka dawo ko ina sukaje? Oho nima bansaniba Jalila tana tareda halima sunata hira, Jalila ta sha mamaki da halima tace mata ta taba aure amma tasha wahala gashi auren dole akayi mata, tanata bata labarin kauye
Yaya Jawwad ne ya shigo ya tarar dasu a parlour, cikin grimamawa halima ta gaida Jawwad ya amsa mata a mutunce sannan ya kalli Jalila
“Baby mun dawo, atemaki cikin gayu, munajin yunwa”
“To babban Yaya yanzu kuwa bari in kai”
“God bless you my sister”
“Ameen Yaya Jawwad”
“Bari in shiga in duba Maama”
“To Yaya a fito lafiya”
Ta mike ta nufi kitchen ta shirya kayan abincin akan tray ta dauka tayi hanyar waje
A kashingide ya tarar da Maama tana waya Dan haka yajira ta gama sannan ya Dan dubeta
“Maama mun dawo”
“To sannunku, ina fatan komai lafiya?”
“Komai normal Maama, kayan ma suna boot”
“To shikenan Bari zan tura Nana ta kai musu”
“To shikenan Maama nasa JALILA ta kaimana abinci mun debo yunwa”
Yafada yana mikewa
“Yawwa dawo ka zauna zamuyi magana”
Guri ya nema ya zauna ya bata attention dinsa
“Ba kaga yarinyar nan ta dawo gidan nan ba, bana son shishshige mata daka keyi, wannan rawar kan da kake akanta kana wani janta a jiki duk banaso, ga Yar uwaka nan cikinku daya ta isheka bana son yayime² da cusa kai kanajina ko?”
Mamakine ya cika Jawwad wai Jalila ce yayime² Allah sarki Jalila itama Yar uwassu ce ai suke nan ba yawane dasu ba amma meyasa Maama har yanzu batason alakar my da Jalila, ya numfasa sannan yace
“To Maama za ayi yadda kika ce, insha Allah za a kiyaye”
“Gara dai itama Nana zan mata magana naga zakewar taku tayi yawa, Tashi kabani guri” mikewa yayi ya fito, jikinsa a sanyaye

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button