Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“A’a kyaleshi yacigaba da zagina”
Tafada tana zare ido

Jalal ya kalli Jawwad

“a ganinka duk wannan ba kara nayi makaba,
kai kasan in wanine yagayamin haka da wani zancen ake ba wannan ba
Dalla cikani” ya fizge hannunsa yayi waje
Da kyar Maama ta lallaba Yaya mairo ta tafi se zage² takeyi

Yau dai ansha drama a gidansu Jawwad

Jalal kuwa yana zuwa Gida dakinsa ya yatafi
“Mtseww munafukar mata waini ne Dan iska itama fa tanada yan iskan nan amma ta zageni, wallahi badan Jawwad ba da yanzu hakoranta se dai asaka ranar Samata na roba”

Haka yaita surutai shikadai wayarsa ce ta fara ringing
Dagawa tayi yasaka a kunnensa

“To ina zuwa”
shine kawai abinda yafada, ransa duk a bace yake yau, haka ya fito ya nufi cikin gidan

Ilham ce tai sallama ta kaiwa Jalila wayarta da ta Yar a gidansu lokacin data fadi
Sannan taga yamata cewar baban Jalal yana kiranta

“To Allah yasa ba laifi nayi masa ba”
“In munje kya gani”
Ilham tabata amsa

“Nana zo muje ki rakani”

“A’a aiki zatamin sekace za akamaki kije ki dawo”
Maama tayi maganar a takaice

Daddynsa ya tarar da mummy a zaune ba sallama balle gaisuwa fuskar nan ba fara’a
“Daddy gani”

“Yawwa Dan albarka dama magana nakeso muyi, mummynka tace ka dena zuwa makaranta, kuma wai Dubai zaka tafi? Ya akayi ne?”

Wani mugun kallo yai wa mummyn

“Eh hakane Dubai nakeso in tafi”

“Karatun fa mummy tafada a fusace

” bazanba” yabata amsa

“Kaji ko? hakafa nake fama dashi bayajin maganata baya ganin girmana,
Wallahi Jalal kar ka bari ka mutu baka dena abinda kake kana sabamin ba”

Su Jalila tun dazu suka shigo suka tarar ana wannan fafatawar

Mikewa yayi ya nufi hanyar fita yana masifa idonsa Jawur

“Ni akayiwa laifi ni yakamata anemi yafiya kece silar komai amma kin rufe idonki laifina kawai kikegani ni akayiw laifi kuma kece kika jamin duk wata kalar rayuwa Dana keyi”

JALAL Yayi maganar cikin karaji

“Bazaka taba canzawa ba, ba adagawa iyaye murya, ba a sa’insa dasu
Amma kai hakan ba komai ne a gurinka ba, ta Yaya zakaga haske a rayuwarka
Se mutane sunce Baka da tarbiyya kaji haushi, anya kanaso kagama da duniya lafiya?”
( Jalila kenan damusar kwali ga tsoro ga ban tsoro)

Aikuwa gadan² JALAL ya nufi inda take idonsa babu alamar tausayi..

Share please

More comments more typing………..

????️????️????️????️????
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  9

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
What’s https: //chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Is a free book

Ina yinku AbdulJalal novel fans irin???????????? da duk sauran masoya wannan novel ina jin dadin comments dinku love u all ❤❤❤

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

Wannan yarinyar kwai bakar Jarababbiya kome za ayi mata bazata dena magana ba in taga abin magana, kozaka kasheta setayi magana

Kallon ta Jalal ya cigaba dayi yana jinjina bakin taurin kai irin na Jalila

Itakam Jalila dariyarta ta cigaba dayi
“Tab wai akan wannan kike wannan kukan aiki yasamu wata, tab sannufa Ilham kin dorawa kanki wahala wallahi…..”

Jalal kallon Jalila yayi cike da takaici
Jalal girgiza kai kawai yayi ya fice saboda ya fuskanci in yacigaba da biyewa maganganun yarinyar nan to tabbas bakin ciki ze iya masa illa

“Jalila meye hakane wai ina ruwanki dasu taho mu tafi”
Nana tai maganar tana janyo hannunta

“Munafukar banza kawai se tsabar shishshigi da Sa ido aikin banza kawai”
Ilham ta fada tana jujjuya Ido

Saboda cusa takaici se Jalila takara tuntsurewa da dariya

“Allah ya temaki matar Dan giya wannan soyayyar kaman a Bollywood ke kinga wani hawaye kaman ta tsaya agaban director hh mrs. Jalal”

“Na shiga uku nikam Jalila meye haka wai dama haka kike ba dadi fa
Ni dai taho mu tafi”
Nana ta fada tana kuma Jan hannun Jalila

Ilham kam rasa bakin magana tayi kamewa tayi tarasa abin cewa

Suna fitowa Nana ta kalli Jalila cike da damuwa
“Haba Jalila why? Abinda kikayiwa Ilham be dace ba wallahi bazataji dadi ba”

“Lallai Nana ke bakiga wulakancin da tayimn da farko ba har munafuka tacemin fa”

” haba Jalila da baki kulasu da bazata gaya miki ba “
“Sorry Nanancy kinsan bana gani inyi shirune kawai, in ta kwantar da hankalinta gobe insha Allah zan bar garin nan”
“Jalila dena tunamin banason tuna gobe in Allah ya kaimu zaki tafi duk se inji na damu”
Nana ta fada a sanyaye
“Nima banason barinku amma very soon zan dawo insha Allah”
“Allah yasa da gaske kike”
“Da gaske mana”

Dayake me Hali baya fasa halinsa sukaga Jalal a harabar Gidan yana kokarin bude motarsa

“Wai akan wannan ake kuka, Allah ya kyauta, har ake Neman a zageni gaskiya Ilham Yar wahala CE”

“Na shiga uku ni Nana, Jalila haka kike dama?”
“Ai ni nafi haka ma duk abinda nasan ba a so ko akemin gadara akansa to nikuma shi nakeyi”

Jalal da ya riga ya shiga mota yana jinsu dayake suna daf dashi tayi maganar shiru yayi bece uffan ba
Sema kokarin tada motarsa da yake

Washe gari da safe Jalila ji take kaman za asa ta a Aljanna yau zata koma gida gurin umminta,
Kuma zata rabu da wannan mugun, kuma se yaya mairo taganta zata kuma cin zarafinta,

se shirinta takeyi amma lokacin kanta yana mata ciwo tunda Jalal ya mareta kanta kemata ciwo

Nana tana wanka Jalila ta hada kayan ta cif Jawwad

ya shigo dakin yasameta tana kallon akwatin ta

“Yar gidan Ummi kingama shirin kenan?”
Jawwad yafada yana zama a gefen gado
“Eh Yaya nagama”
“To insha Allah in an sakko daga masallaci zamu tafi kizama cikin shiri in ma dawo zamu tafi”
“Aini ko yanzu kace mu tafi na shirya,”

“Eh kyace haka saboda kin gaji da zama damu ko?”
“A’a nifa nace muku bahaka bane”
Ta fada a shagwabe

“To shikenan naji kar kimin kuka”
Jawwad yayi maganar da sigar tsokana
Daga nan ya tashi ya tafi

Bayan fitarsa da ba dadewa Ilham ta shigo hannunta dauke da ledar bagco, ta tarar da Nana da Jalila su suna cin abinci suna hira

Jalila tana ganinta ta sunkuyar da kai tana dariya kasa²
“Mtseww”
Nana taja uban tsaki ta direwa Jalila bagcon a gabanta “gashi nan Inji mummy, sakon daddy ma yana ciki”
Ta fada tare da juyawa zata tafi

“Haba Ilham kya tsaya kuyi sallama fa yau zata tafi”
“Ta sauka lafiya “
Shine abinda kawai Ilham tafada tai ficewarta

Itakam Jalila ta kudure a ranta seta tsokani Ilham amma tasan in tayi a gaban Nana mita zatayi mata Dan haka se cewa tayi
“Nana ina zuwa”
“Ina zaki?”
“2mint yanzu zan dawo”
Ta biyo bayan Ilham se ta hangeta ta tsaya tana waya a wajen flowers din gidan
Seta nufi inda Ilham take amma kafin takarasa taji tana waya

“Wallahi mami nafara gajiya wulakancin yau daban na gobe daban Sam Hankalinsa baya kaina jiyama bakiga wulakancin da yayimi ba am tired wallahi”
Jalila Batajin me akace daga daya bangaren

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button