Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Allah ya kiyaye ya tsareni, dazama irinka bazan taba zama irinka ba Mara tarbiyya…
” ohoh wait ashefa Ke kin tsaida sallolinki biyar a rana hada nafila nikuma banayi shiyasa Ke ba irirna bace,”
Nima bani na saiwa kaina ba amma zanyi meyuwuwa inga kinzama Irina tunda jiya kinfara ki rubuta ki aje sauraanki giya da kwayoyi zaki zamaa abar kwatance kaman ABDULJALAL sha³ jahila, I hate u”

“God forbid, over my death body kwatance in dai bana Alkhairiba indai irinnaka ne Allah ya kiyaye kuma niba Jahila bace wallahi”

Hannu yasaka a aljihunsa ya dakko taba da lighter
“naga kaman ta jiya bata isheki ba sokike in kara miki wata”

girgiza kai tashigayi tana zare ido

“Mara kunyar karya kawai”

Yafada tare da maidasu aljihunsa

Ya mike ze koma kujerar da ya taso kawai yaji muryarta tana fading

“Kuma wallahi Allah ya isa abinda kamin jiya kodayake bakasan ma’anarta ba kona maka bazaka damu ba amma ban yafe wallahi azzalumi kawai me kama da yan daba”

Ohh God yarinyar nan ba zata canza ba,

Dawowa yayi inda take har gaban gadonta yasa yatsunsa biyu a side din kumatunta ya matsa da karfi

Wani uban ihu tasaka saboda zafi jitayi kaman ze Huda mata kumatu da yatsunsa nan da nan hawaye ya shigo zubowa daga idonta wani nabin wani sedayaga fuskarta tayi jawur hawaye na ambaliya a fuskarta

Sannan ya cikata Yakoma inda yake zaune da farko yana danna waya
Jawwad ne yayi sallama tare da nurse
Kallonta Jawwad yayi
“lafiya kuwa sisy kukan me kikeyi?”

Seda ta kalli inda Jalal yake amma ba ita yake kallo ba
“Ni Kaduna zankoma gurin Ummi'”
Tai maganar tanakuma fashewa da kuka

Se da Jalal yayi murmushi mugunta

“Haba Jalila dama hayanzu kina wannan rikicin naki kiyi hakuri in muka koma Gida mayi wannan maganar”
Kai kawai ta gyada masa

Nurse din takarasa mata abinda yakamata aka sallemesu.

Har suka Shiga mota suka kama hanyar Gida kuka takeyi shikuma
Jawwad se aikin rarrashi yake

Shikam Jalal Jawwad yafi bashi haushi se wani lallabata yake

Itakuwa ita kadai tasan zugin da fuskarta takeyi ga kirjinta hayanzu ba dadi saboda wahalar yin numfashi da tayi
(Nikam nace in rashin kunya abinyine gobe maki kara)

Maama da Nana suka iso Gida Nana wanka tayi ta kwanta saboda batasamu tayi bacci sosai ba Daren jiya
Maama kam datayi wanka seta shiga kitchen da niyyar Dora sanwar rana
Sallama taji a parlour Dan haka ta aje abinda take ta domin ganin me sallamar
Wata matace mekama da maama sekuma wata budurwa da batafi sa’ar su Nana ba

“Yaya mairo sannu da zuwa yanzu kuke Tafe da ranar nan”

Wadda takira da Yaya mairo tace

“eh mune ai munzo tunsafe bakowa a gidan narasa INA kuka tafi da safe haka gashi ni ba waya a hannuna tasamu matsala,
Kukuma makota kowa gate a rufe sekace marasa gaskiya”

“Wallahi kinga Jalila ce tazo mana hutu se kuma ta yanke jiki tafadi jiya,
A Asibiti muka kwana sedazu muka dawo, mun baro za a sallamata Jawwad ze taho da ita”

Wani mugun kallo Yaya mairo tayi mata

Sun iso gida lafiya sukayi parking
Jalila fuska duk hawaye amma se cewa tayi “Yaya JAWWAD an kira azahar ka tsaya a masallaci kai salla
Kasan sallar jam’i tafi lada akan sallar mutum daya kodayake garama Wanda yakeyi shika dai wanima bayayi”
Jawwad ne ya kalleta da mamaki da nufin yayi magana

Ta bude kofa tafice da Sauri

Shiko Jalal yasan dashi take sarai haka halinta yake bazata canza ba amma seyayi kaman beji me tace ba shi dariya ma taso bashi ganin fuskarta duk hawaye amma Neman magana take

Ta nufi cikin gida abinta har yanzu jikinta babu kwari sosai, tana shiga ta nufi dakin maama domin ta Sanar da ita ta dawo an sallameta
takama handle din kofar da nufin ta shiga
amma maganganun datajine
Suka Sa ta daskare a tsaye zuciyarta ta fara bugawa da karfi

“Gaskiya zainabu baki da hankali yanzu har asibiti kikaje jiyyarta kika barota da danki, dangin arna ababen kyama kika bari tana mu’amala da yayanki hartazo miki Gida Hutu koda take musulma ai daga tsatson arna tafito!!!”””

Tirkashi wasa farin girki

Please share

More comments more typing……

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  5

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

I want comments not stickers????????????????
Comments dinku shine kwarin gwiwata

   _My first novel_

Haka ta tsaya daga inda take ta dinga caccaka masa maganganu son ranta maganganu masu ciwo ciki harda Kalmar dayafi tsana Mara tarbiyya sabida tasan baze iya cinmata ba

“Inda zuciya kadena shaye shaye kazama mutumin kirki kacigaba da abota da yayana in ba zuciya kuma kacigaba da zuwa kana like masa cingam ko kuma ince
Salansa sarkin hayaki “”

Ta juya takoma cikin Gida abinta kaman batayi komai ba
Maama ta tarar a palour tana tsifa

“Maama kawo in tayaki naga tsifar dayawa “
“To karbi kibiyar”

Hmm yarinyar nan akwai shiga rai ba ruwanta dukda tasan abinda ke tsakanina da mahaifiyarta amma ko a fuskarta ban taba ganiba,
inma dai salon wani makircinne duk zan iya daku d’a na ne dai ba a isa a hada min zuri a da wadda take da raunin nasaba ba, tayi wannan zancen a zuciyarta.

 Shikam tsayawa yai cak kaman an dasa shi, yama rasa wani mataki ze dauka, fasa zuwa gurin Jawwad yayi ya koma gida ya shige dakinsa, ya dinga tuttulawa cikinsa giya seda yayi mankas sannan ya zube a gurin yana bacci.

"Nana gaskiya abinda Yar uwarki tamin ya mugun bata min rai, ya dace tafadamin haka agabana taci zarafin Dan uwana, wallahi taci albarkacinki dasena shukamata rashin mutunci wallahi"

Itakuma tsayawa zatayi tana kallonki ba bakisan wannan uwarkice a fitsara ba kina ganinta haka shi kansa uban gayyar ina tsoron randa ze danketa (Jalal)Nana tayi maganar a zuciyarta a fili kuma Se cewa tayi

“Nasani Ilham bata kyauta ba amma zanmata magana haka halinta yake bata boye abu a ranta komene ne zata fada a gabanka amma kiyi hakuri insha Allah hakan baze kuma faruwa ba”

“Kinga ni tafiya zanyi bansamu biyan bukatana sema karamin takaici da kukayi”

“Naface kiyi hakuri Dan Allah ki gaida mommy”

Banza tayi mata tai tafiyarta
a palour taga Jalila nayiwa Maama tsifa harara ta wurgawa Jalila amma me ita seta maida mata da murmushi

“Kigaida Gida sister Ilham agaida mummy da yayanmu” tafada dauke da murmushi a fuskarta

Maama CE

“Ilham kicewa mummynku in ankawo lesunan tamin magana zan turosu su zaba”

“To zangaya mata”

shine abinda ta iya fada saboda Jalila takawota iya wuya.

Tana zuwa Gida dakinta ta wuce ta nemi guri ta kwanta maganganu Jalila suka shiga dawo mata

{“Sedai in akwai wani sirri da kike
boyewa Wanda bakowa yasani ba”!!}

To ya akayi tasani, taga a iya tunaninta babu Wanda ta taba wannan zancen dashi balle ya gayawa Jalila
To ya akayi tagane akwai wani abu a ranta haka taita tunane²
Har bacci yayi awon gaba da ita

Se banyan isha’i sannan giyar da yasaha tasake shi ya farka daga nannauyan baccin da yayi, ji.yayi kansa yayi mugun nauyi kaman ba a jikinsa yake ba haka ya tashi yana rarraba hanya ya shiga toilet yayo wanka tare da alwala

Ya fito palour ya shimfida sallaya yayi azhar yayi la’asar ya dauke sallayar

(Nikam nace magariba da ishan fa?)

Cikin gida ya shiga ya tarar mummy na waya, ya kai minti biyar yana jira amma wayar taki karewa har ya kosa yagaji da zama yafara tsaki

“To Dan sarkin Mara kunya tsakin me kake” mummy tafada bayan ta kammala wayar

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button