Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

dan jaraba da sassafen nan yana sashen Jawwad daga harabar part din Jawwad akan kujera yanata shan taba, da ganin yanayin shigarsa kaman motsa jiki yagama,
Seda Jalila tazo gifta shi sannan tace
“Dan Jaraba da sassafen nan mutum be karya da komaiba se hayaki”
Ko kallonta beba yacigaba da shan tabar Sa
Cikin palour Jawwad ta kai abincin amma baya palour, bedroom din Jawwad taje ta danyi knocking amma shiru, ta tura kofar bedroom din ta Dan bude zubar ruwa taji a toilet alamun yana wanka
Dan haka ta fito har tazo zata kuma gifta Jalal takoma gaban Jalal sannan tace masa
“In Yaya Jawwad ya fito kace masa ga abincin Sa nan, in yagama ya kirani zan gyara masa daki”
Ko motsi beba balle ya kalleta yacigaba da aikin shan tabarsa, ga kwalin wata tabar da lighter akan table din gabansa
Har zata wuce ta dawo, tasa hannu ta dauke kwalin tabar da lighter ta fizge na hannunsa
“Wai kai wani irin mutum ne, baka San wannan abar illa ce ga lafiyaba da sassafe baka zubawa cikinka komai ba se hayaki, karka kuma shamana wannan abar a cikin gida, inzaka sha ka zauna ka sha a gidanku, dan uwana yafika cutuwa da wannan hayakin dakake busawa ba yau ba gobe”

Turkashi
Share please
More comments more typing……………………
Love you all my fans
❤❤❤❤❤

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:30 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 31

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa

      -MY FIRST NOVEL-

Dagowa yayi ya kafeta da Jajayen idanuwansa kyar ko kiftawa bayayi
Seda gaban Jalila yafadi tozali da wannan idanuwan na Jalal masu kama da garwashi dagani ransa a bace yake
Dukda ta razana, ta dauka ze mareta ne, ta dake ta juya ta bude dustbin ta watsasu ciki tayi hanyar cikin gida bin bayan Jalila yayi da kallo ya kai makura a tunani bayajin komai tunaninsa yayi zurfi sosai, jiyayi an dafa shi yadaga kai Jawwad yagani a tsaye “
dan uwa zomuje mu karya naga baby takawo abinci”
Girgiza kai Jalal yayi “banaci”
Yafada a takaice tareda mikewa tsaye “kamar ya bakaci Abincin ne beyimakaba kokuwa wani abun Jalila tayi maka”?
Girgiza masa kai Jalal yayi, yana kokarin tafiya, dakatar dashi Jawwad yakumayi
“Haba Jalal kagayamin me akayi maka mana, na lura tunjiya da magariba baka walwala, meyasane”?
Dan kurawa Jawwad ido yayi yaga yadda yadamu
“Calm down ba abunda yake damuna jinayi kawai bana son cin Abincin”
“No Jalal ban yaddaba”
Juyawa Jalal yayi ya tafi, yabar Jawwad a tsaye,
“Ohh God, meyake damunsa ne”
Komawa Jawwad yayi ya duba abincin kunun gyadane da kosai
Mikewa yayi yabi Jalal gidansu, Jalal yakoma gida yaje, ya kwanta akan gadonsa ya lumshe ido
Jawwad ya karasa ya zauna gefen gadon ya dafa Jalal “dan uwana kagayamin meyake damunka?, lokaci daya duk ka canzamin, kagayamin ko Jalila ce tayi maka wani abun” dan bude ido Jalal yayi ya kalli Jawwad, idonsa Yakuma yin Ja girgiza masa kai Jalal yayi
“To yanzu kayi hakuri, kazo muje kaci abinci”
Mikewa zaune jalal yayi “Jawwad ba abunda yake damuna, kaje kaci abinci ni na koshi, karka damu dani banajin cin Abincin nan”
Mikewa Jawwad yayi ya koma gida yana tunanin meyafaru da Jalal,
yaje ya tarar da Jalila a part din Sa tana kokarin gyarawa
yana shigowa Jalila ta kalleshi
“Yaya Jawwad bakaci Abincin ba meyafaru”
“Baby ko kinyiwa Jalal wani abune naga yaki cin Abincin kuma ya tafi gida”
“Cemaka yayi nayi masa wani abun?”
“A a becemin ba amma naga yanayinsa ya canza tun jiya”
“To tunda bayaci kaikaci naka karabu dashi mana”
Dan zaro ido Jawwad yayi
“A a baby bazan iyaba akwai abunda yake damunsa amma yaki gayamin”
“To Allah ya kyauta, dama gyara maka dakin zanyi”
“Ke ba kya gajiyane? Kije ki huta”
“Karka wani damu bawata gajiya gyaran part din naka ai ba wani lokaci ze dauka ba”
“Bani da bakin godiya baby Allah yayi miki Albarka”
“Ameen yayan”
Flask din kunun gayadan da cups ya dauka yayi waje, Jalila ta girgiza kai Abincin ne baze iya Ciba in Jalal baeci ba tab agaida Yaya Jawwad
Nan da nan Jalila ta gyara part din ta kukkuna tiraren wuta se kamshi yake ta rufo ta koma cikin gida Maama ta tarar a palour da nail cutter tana kokarin yanke farce, Nana kuma na kan two seater tana kallo, karasawa tayi gurin Maama ta karbi nail cutter din
“Kawo in yanke mini, inna gama sekice Allah yayi min Albarka”
Ta karba takama hannun Maama ta na kokarin yanke mata farce, kallon Jalila Maama takeyi “wannan wace irin yarinyace dabata San wulakanciba, duk hade mata ran danake taki ta nuna tasan inayi balle taji haushi”
Haka Jalila ta yanke mata farce tsaf, sannan tabar palour
Jawwad da kyar ya lallaba Jalal yaci abincin safe kusan karfe daya na rana, amma dukda haka Jalal baya walwala, daurewa kawai yake ya boye damuwarsa saboda Jawwad,
Kwana biyu Hannah Sam bata ganin Jalal, baya daga kiranta, ta dan shiga damuwa saboda haka ta yanke shawarar kiran Jeje tagaya masa, shima complaints din da yayi mata kusan kwana biyar bega Jalal ga kuma baya daga wayarsa, yaje gidansu baya nan besamu ganinsa ba yarasa meyake damun Jalal
Haka take ma gurin Jawwad kowa yarasa ganewa Jalal abinci se Jawwad ya takura masa sannan zeci, baya walwala yadena shiga gidansu Jawwad sam, Jawwad yarasa dalili, Jalal ya dena zuwa ko ina se zaman daki
Yau kusan satin Jalila biyu a kano amma har yanzu Ummi batayi tafiyar nan ba, tun JALILA tana tambayar Ummi har tagaji ta kyaleta,
Jalila tana rayuwa a kano ba yabo ba fallasa, Jawwad da Nana da Abbansu suna kaunarta, yayinda Maama Sam babu ruwanta da ita, bata shiga sabgar Jalila kwata² hakan bayamata dadi amma bayadda ta iya
Tun ranar da Jalila suka samu wannan sabanin da Ilham bata kuma haduwa da ita ba
Jalila tana zaune a palour tana chatting da Hanan, Halima ta fito sanye da hijabi Jalila ta Dan dubeta
“Anty halima ina zuwa haka?”
“Kinga Hajiya ce ta aikeni zan kai kayan nan, gidan wata kawarta”
“Bari in tambayeta se in rakaki”
“To shikenan tambayota semuje”
Dakin Maama Jalila taje ta ganta tana waya ta jirata tagama sannan tace
“Maama naga kin aiki halima zan rakata Dan Allah”
Kallonta Maama tayi a wulakance ta dauke kai
“Ba a karkashina kike zaune ba yadda kika gadama kiyi”
Kallonta Jalila tayi ta Dan girgiza kai, ta mike ta bar dakin ta fito ta tarar da halima,
“Bari insaka mayafi in rakaki”
“To ina jiranki”
Jalila taje ta dakko gyalenta tayi rolling ta fito
Ba karamin kyau Jalila tayi ba doguwar Riga tasa baka tayi rolling da Jan mayafi suna shirin fita Nana suka shigo ita da Ilham
“Wow looking so masha Allah sister kina wuta kinga kyan da kikayi kuwa, ina zuwa haka”?
Murmushi Jalila tayi ” bana son zolaya Nana, Halima zanyiwa rakiya”
Banda aikin harar Jalila da kallon banza ba abunda Ilham takeyiwa Jalila
“Gaskiya kinyi kyau, sekun dawo, amma gaskiya ayi a hankali karki hada go slow a hanya”
Nana ta fada tana kashemata ido
“Nana kenan ba kya rabo da tsokana”
Jalila ta Dan kalli Ilham
“Kawata Ilham ba fada me yakawo gaba, fatan kina lafiya”
“Nakasa kika gani a jikina kokuma, a kwance kika ganni kike tambaya ina lafiya”
“Ba ko daya na dai ga kaman u are psychologically abnormal”
Tana zuwa nan a zancenta tanufi hanyar waje, tabar ILHAM a tsaye sororo, tama rasa mezatayi,
Halima tabi bayan Jalila, Nana kam gimtse dariyarta tayi ta kalli Ilham
“Don’t mind her please, muje ciki”
“Wallahi Nana badan ina jin kunyarki ba da na Dade da ketawa Jalila rashin mutunci, nizata kalla tace am looking psychologically abnormal”
“Yi hakuri, nidai bazan gaji da Baku hakuri ba, sannan kidena nuna mata kinji haushi
Yanzu dai bar batun Jalila ban labari meyake faruwa ne”
“Mtseww meyema be faru ba kwana hudu kenan banga yaya Jalal ba, idan naje part dinsa a kulle duk na damu, ko yau mukayi aure da Yaya Jalal na azabtu Nana”
“Calm down, Jalal ba karamin yaro bane, maybe yana tare da Yaya Jawwad, sannan tunda ba wata budurwar CE dashi ba ki kwantar da hankalinki, a hankali komai ze wuce, kinsman yanada gaddama”
“Wani irin hakurine banyiba, narasa meyake damunsa, kullum shine tension dina, kina batun bashi da budurwa to yanada ita kuma nasanta indai na haifu senasata tayi danasanin Sanin Jalal da tayi”
Dan zare ido Nana tayi
“Are you serious Jalal yanada budurwa, Dan Allah wace wannan”?
“Ai ba sonta yakeba ita take masa shishshigi, da zarginta nake yanzu na tabbatar da wacece, zan dau mataki na karshe, daze kawo karshen komai”
“Wani mataki kenan?”
Nana ta fada a tsorace
“Just watch, bari inkoma Gida anjima zanzo in tambayi Yaya Jawwad ko yasan Inda yake”
Tana gama fadin haka ta mike tayi waje da sauri
Jawwad be fushi ba yakoma gurin Jalal amma ya tarar ya rufe kofar palour Sa Jawwad yayi iya kokarinsa da rarrashi amma JALAL yaki budewa, gashi tun safiyar ranar beci komai ba haka Jawwad yagaji yakoma gida
Shikuwa Jalal yana ciki yanajin Jawwad yaki bude kofar tabbas Jalila tayi gaskiya yakamata ya bar Jawwad ya huta haka tsawon shekaru yana fama dashi da matsalolinsa
“Wai meyasa nake hakane, meyasa bazan yi rayuwa kaman sauran mutane ba”
Jiyayi zuciyarsa tana tafasa, kaman zata tsga kirjinsa ga wani nauyi da kansa yayi kaman ya fashe yai jifa da Wayne cups din kan karamin table din dakinsa, ya dinga jifa da duk abunda yaci karo da shi ya dinga jifa da abubuwa, da kwalaben giyar da ya shanye
Yakoma ya zauna idonsa suka kara Ja, ya runtse idonsa yanajin kansa yana juyawa
Mikewa yayi zumbur yabi takan fasassun kwalaben nan ya dauki keys din motarsa ya fito a sukwane, motarsa ya nufa ya Shiga ya fisgeta da gudu yayi waje

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button