Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Haka nan take tafiyar kaman wadda kwai ya fashewa a ciki, haka takarasa gidansu siyama.
makeken Gida ne Wanda yayi matukar haduwa da tsaruwa baban siyama yana da kudi sosai custom ne daga shi har Maman siyama mutane ne masu saukin kai kuma sun yaba da hankalin Jalila shiyasa suka kyale kawancen nasu
Siyama Sam bata da girman kai a makarantar boko suka hadu da Jalila tun primary suke tare makarantar ‘yay’an masu kudi ita Jalila takeyi saboda Jajircewa da rikon amana na baban su Jawwad
Kawancensu har tsakanin iyayensu mata Wanda yakai har kasuwanci sukeyi tare, umman Siyama ta San komai game da rayuwar ummin Jalila ta dauketa kaman Yar uwatta ummin Jalila bata fiye shiga harkar mutane ba amma tana mu’amala sosai da umman Siyama

A tangamemen parlour Jalila ta tarar da Umma (mahaifiyar siyama)
“Hajiya Umma brk da rana”
“Anya Jalila zan amsa gaisuwar nan taki, kinyi tafiya ba sallama kin dawoma bakizo mun gaisa ba balle insa ran tsaraba to ni nayi fushi”
Umman tafada cikin zolaya
“Haba Umma tuba nake yau ai gani Nazo”
“Bawani kinzo dai gurin Siyama sekije tana daki,
Nikuma zamu gauraya dake naganki wani iri ko baki laafiya ne”?
“Hajiya Umma kenan, lafiyata kalau, bari inje gurin siyama, Ummi tana gaisheki “
“Ina amsawa”

Jalila ta mike ta haura sama dakin siyama
Siyama ce kwance akan katafaren gadonta tayi rub da ciki tana game a waya,
Sallama Jalila tayi, siyama ta amsamata ba tare data daga kai ta kalleta ba
“Aminiya gurinki nazo akwai matsala”
Banza siyama tayimata tacigaba da abinda take
“Aminiya magana fa nake kika min banza”
Jalila ta maimaita
“Ni a wa zan San matsalarki, ni na isa ko kin manta wulakancin dakika yimin A gidanku”
Siyama ta bata amsa ba tare da ta dago ba
“Ohh God am sorry aminiya lokacin ina cikin tashin hankaline, Dan Allah kimin afuwa ki saurareni, right now ma a cikin wata matsalar nake siyama jinake kaman zanyi hauka, yanzu haka zuciyata bikiji bugun data keyi ba”
A razane siyama ta mike zaune tana kallon Jalila
“Kaman Yaya? Meyafaru?”
Ajiyar zuciya Jalila tayi sannan ta labarta mata duk halin da ake ciki
“Ni yanzu babban tashin hankalina aminiya ni bansan ta Yaya zan hana shi tafiyar nan ba yana kano ina Kaduna,
Tunda na fara mafarkan nan bana nutsuwa se inji kaman zan haukace”
“Easy, don’t said that again please karki kuma batun hauka
Kinga maganata ce fito dama nagaya miki zaman Kaduna bana kibane inkika temake shi kanki kikayiwa kamar kin temaki Jawwad ne”
“Kinga ni ba wannan surutun ba kigaya min mafita siyama kaina ya kulle”
“Aikuwa dole kibude shi, shi tunanin naki, yaya Jawwad zaki kira ki zigashi akan kar yabarshi ya tafi saboda besan meze faruba in ya tafi zuciyar Yaya Jawwad zzaki karya yadda zaki ingiza shi ya hana shi tafiya”
“Siyama bana tunanin hakan me yiwuwa ne, nasan Yaya Jawwad zeyi iya yinsa kan yahana shi tafiya tunda kika ga ya hakura to abun yafi karfinsa,
Dama da ganin idon nan na Jalal zeyi azababben taurin kai”
“A’a Jalila ki dai gwada kigani, kema ai taurin kan yana damunki”

Mummy ce take ta rusa kuka
“Yanzu Jalal dagaske tsallakewa zakayi kabarni, kai kana ganin hakan shine dai² a rayuwarka bani da kowa se kai zaka Sa k’afa ka tafi, har kana fadin inka tafi bazaka kuma dawowa ba”
“Idan na tafi hutun mune ni dake gaba daya ki huta dasaki bacin rai danakeyi”

Ilham ce tafito tazo gabansa
“Haba Yaya Jalal yanzu in…
” ke!!!!! Kikasake kika Sa min baki sena tattakaki ina ruwanki dani mayya kawai”
Ya fice daga parlour lambar Jeje yakira
“Karka manta fa kazama cikin shiri karfe hudu insha Allah jirginmu ze tashi”
Ya katse wayar ya tafi dakinsa

“To siyama bari in jarraba amma nikam na karaya Allah kabani iko “
“Ameen don’t waste time yi sauri”
Siyama ta fada a gaggauce

Lambar Jawwad Jalila ta kira
Aikuwa tayi sa’a ya dauka

“Barka da rana yayana”
“Yawwa autar Ummi ya ummina ya Gida”
“Lafiya kalau, amma yanaji muryarka wani iri ko duk Dan tafiyar Yaya Jalal dinne”

“Kedai bari sisy na Daren Jiya banyi bacci ba Jalal ya kafe wannan karon tun tasaowata tare muke dashi jinsa nake wani bangare na zuciyata amma ze tafi ya barni gani nake Lamar da wasa yake”
Ajiyar zuciya Jalila tayi

“Ya tafinne?”
Jalila ta tambaya
“A’a jirgin karfe hudu zebi yau zetafi”
Cikin Jalila ne yayi wata kara ta kalli agogo karfe daya da rabi
“Yaukuma ?”

Tafada a tsorace
Siyama ce ta kalleta ta girgiza mata kai alamar kwarin gwiwa

“Eh yau sisy haka dai yacemin, yau ban yi tsammanin Dan uwa zetafi ya barni ba”
Jalila ta numfasa tace
“To waime yasa ze tafine?”
“Cewa yayi gara ya tafi mummy ta dena ganinsa, yadena sata bacin rai”

“Allah sarki mummy ko yazataji idan ya tafi, ya daddynsa zeji in ya bude ido yaga baya kusa dashi,
Yaya Jawwad abokinka bashi da tausayi baka tunanin me ze faru Idan ya tafi kasar da babu me Sa shi babu me hanashi,
Baka tunanin wasu abokai ze hadu dasu a can,
Allah sarki nasan dole mummy ta zubda hawaye inya tafi, kuma Kasan hawayenta matsalane a rayuwarsa, Yaya yakamata kahana shi tafiyar nan, ka temakawa rayuwarsa daga masifar hawayen uwa
Yanzun ma karkayi mamaki abokanan banzarsa ne suka ziga shi shine zeyi tafiyar”

Da sauri Jawwad ya tashi zaune tare da furta
“Abokanan banza Jeje”

“Mekace Yaya”
“No bakomai zanyi kokari inkuma jarraba hanashi tafiya nagode sosai da gudunmuwarki kanwata, da na hakura amma kin tunatar dani wani abu me mahimmanci nagode”
Sukayi sallama
Jalila tayi ajiyar zuciya
“Good dear kinyi yadda yakamata sekace Jarumar film”
“Hmm ba wannan ba aminiya Allah yasa ya yadda kar yayi tafiyar nan”
“Ameen insha Allah bazeyiba Addu’a zamuyi tayi”
“Allah ya amsa amma nakaraya saura awa biyu ya tafi fa”
“Ba komai calm down mucigaba da addu’a Allah ya bawa Yaya Jawwad sa’ar hanashi tafiya”
“Ameen”
Jalila ta amsa a sanyaye

Da sauri Jawwad ya tashi ya nufi gidansu Jalal kai tsaye part din Jalal ya nufa yaje ya tarar yashiga wanka
Gefe ga katuwan trolley dinshi ya hada ta tsaf
A hankali Jawwad ya shafa trolley yayi ajiyar zuciya, ya nemi guri ya zauna yana jiran fitowarsa ya shafe akalla mintuna sha biyar yana jiransa sannan ya fito daga wankan

“Kana nan banji shigo warkaba ai”
JALAL ya fada yana goge jikinsa da Dan karamin towel

“Jalal”
Jawwad yakira sunansa da dan sauri Jalal ya kalleshi saboda da wuya ya ambaci sunansa

“Baka saba yimin karya ba yanzun ma bana fatan kayimin kaida wa zaku tafi dubai”?

Jalal ya danyi shiru sannan ya yi magana
” nida Jeje ne”?
Da sauri Jawwad ya kalleshi Jeje fa kace Jalal
“Jalal kasan me kake cewa kuwa yanzu kaida shi zaku tafi,
Ka fifita tafiya kabar iyayenka saboda wannan Dan iskan Mara mutuncin
Kazabi ka tsallake kawai katafi garin da banaka ba, ka zauna,
Dama nasani he is behind all what u are doing”

“No Jawwad don’t blame him u know who is behind all this kasani kasan komai karka Dora masa, nan da wani dan lokaci shi jeje ze dawo nizanyi zamana a can in karatun Yakama in cigaba a can”

“Jalal kasani ba kaunarka yake ba, baze bari kayi kyakykyawa rayuwa ba kullum burinsa ya kuma rusaka”

“Ouhhh don’t mind me bros, kabani gudunmuwa a rayuwata bazan mantaba, bana tunanin ko ciki daya muka fito da kai zansamu fiye da haka ,
Amma gara in barka kaima ka huta, kanwarka bata son mu’amalarka dani banaso mutane sucigaba damin kallon zan bata maka rayuwa kamar yadda tawa tasamu illa,
Banason mutane sucigaba da kyamata da miyagun halayena
Gara inje rayuwar da naga dama Inda ba Wanda yasanni balle ya damu dani”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button