Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Abun duniya duk ya ishi Ilham tarasa abunda yake mata dadi gaba daya wani mugun kishine yake damunta akan Jalal, se yanzu take tabbatarwa kanta tafada soyayyar Jalal fiye da yadda take tunani,
Dan haka bayan an tashi daga makaranta gidansu ta wuce taje tasakawa maminta kuka ta gaya mata abunda ke faruwa
“To kekam meye na damuwa duk kin daga hankalinki kalli yadda kika rame fa, naga dai Soyayyar ta wucin gadi ce burinmu na cika shikenan”
Mami a gurinki ce soyayyar dan lokaci ce se yanzu nagane dagaske soyayyar Jalal ta Huda zuciyata bana tunanin zan iya rabuwa da shi ILHAM tai maganar a zuciyarta
A fili kuma tace
“Mami duk da soyayyar wucin gadi ce amma kuma in shirinmu ya rushe fa?”
“Inkinga shirinmu ya rushe to sakacinkine, indai kika dage komai zezo dai² da yadda muka tsara, kedai kicigaba da amfani da magungunan danake karbo miki, sannan duk abunda zemiki na wulakanci kidena fushi kici gaba da binsa,
Randa ya shigo hannunmu kuma”
Bata karasaba se wani Murmushi da mamin tayi
“Kiyi kokari ki gane wadda take turamasa sakonnin, itama zamuyi maganinta”
gyada kai Ilham tayi cike da kwarin gwiwa, Aranta tace “da kaina zanyi maganin ko wace, Jalila kinyi gangancin fara soyayya da abunda nakeso zakiga tsiya”(nikam nace Allah sarki Jalila bata San anayi ba)
Haka Ilham ta shirya ta nufo hanyar gida, harta wuce part din Jalal kawai ta dawo ta nufi hanyar part dinsa tana zuwa kofar bedroom dinsa ta tsaya tana tunanin me yakamata tayi

Shikam Jalal Yana kashe wayar Jawwad shikuma tasa wayar tafara ringing lamba ce amma ba suna dan haka beyi tunanin komai ba ya dauka

“Oughhh baby tun safe banji muryarka ba ina kewarka sosai
A ina zamu hadu ne please, am missing you so badly, said something please, ko muryarka inji mana”
“Waike wace irin mace ce Mara kamun Kaine? Ki rabu dani nagaya miki meyasa kike min shishshigi ne bana son yi miki rashin mutunci fa”
Wani murmushi Hannah tayi cike da kissa ta kara kashe murya cikin shagwaba tace
“Babyna komai zaka kirani dashi fa bazanji haushi ba, ni komai naka burgeni yake, ko da zakamin duka ne a gaban jama’a, I wish halinku daya Da Jawwad da komai yazomin da sauki, nasan da shine ze tausayamin halin danake cikin amma a yanzu ma karkayi tunanin zan karaya, yanzu ko ka fadamin inda kake ko inkira Jawwad in tambayeshi, kuma ko inane biyoka zanyi”
“Karki fara Jawwad daban ni daban, Jawwad ne yake lallabaki, kuma shi yahana tun farko in nuna miki waye Jalal, kishiga hankalinki, wannan shine gargadina dake na karshe
Ilham dake bakin kofa kuwa daskarewa tayi
Ya tabbata Jalila ce Wato dama Jalila ce kenan, itace take son Jalal take turo masa messages haka, gashi yana cewa yana kyaleta saboda Jawwad, lallai Jawwad ma munafiki ne
Wani baking kishine ya ciwota Bata San lokacin data karasa dakin ba tasa hannu ta fizge wayar daga hannun Jalal tayi jifa da ita tana wani irin huci wayar ta tarwatse a gurin

Share please
More comments more typing………………

My group members inajin dadin comments dinku da addoinku nagode sosai Allah yabar kauna
????????????????
Kuna comments ina muku typing????????????
Kuna bari ina lalaci ????????????????????

????️????️????️????️????️
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  25

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Gaskiya comments nakeso ba sticker ba kokuma Just thanks in bahaka ba zan dena typing kullum
Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
Dama dukkan masoya wannan novel ina alfahari daku ❤❤❤

    -My First Novel-

Not Edited

Kallonta Jalal yayi da mamaki ya kalli inda Ilham ta tarwatsa masa waya ya dawo da dubansa kanta
“Baze yiwu ba Yaya Jalal, kana wahal dani kana garani kawai dan nace inasonka amma kalli yadda wata take bayyana maka soyayyarta baka dau wani mataki ba amma ni kalli yadda kake wulakantani sau daya baka taba kallona da idon tausayiba
Meye laifina dan nace ina Sonka?”
Shi mamakima ya hana shi magana be ce mata kala ba ya durkusa yana tattara pieces din wayarasa, ya tattara ya nufi waje ze bata guri tazo ta sha gabansa
“Magana fa nake maka Yaya Jalal, let me tell you something wallahi kai nawane ni kadai babu wata Jaka data isa tayi takara dani wallahi kowace sena kauda ita gefe”
Hawayene ke fitowa daga Idonta wani irin kallon baki da hankali yayi mata ya kuma zagayeta da niyyar ya fita
Janyo shi tayi takuma tsayawa a gabansa ta kalleshi ido cikin ido cikin masifa tace
“Jalal baka isaba ina magana ka maidani mahaukaciya zaka tafi ka barni, I mean what I said wallahi, zan iya komai akan cinma burina, gara tun wuri ka gargadi zuciyarka kattayi gangancin fara soyayya kaidin nawane”
Bata rufe baki ba ya sauke mata maruka biyu masu kyau,
“Har kin isa ki tsaya a gabana kina gayamin maganganun dakika ga Dama, kin fasamin waya na kyaleki be isheki ba shine zaki tsaya a gabana kina gayamin abunda kika gadama ko yaushe ma nafara wasa dake, da kika iya tsayawa kina gayamin wannan haukan,”
“Wallahi kozaka kasheni na dena boye soyayyata a gareka koni ko ita wallahi”
Hannu yadaga ze kuma marinta
“Jalal meye haka kakeyi”
Jawwad ya karaso da sauri ya rike shi
“Haba Jawwad ba girmanka bane dukan mace, me tayi maka haka, kake dukanta”
Dawo da kallonsa yayi kan Ilham
“Ilham koma cikin Gida yi hakuri banni da shi tashi kikoma Gida”
Wani mugun kallo tayiwa Jawwad a ranta tace munafiki ai kasan komai amma a zahiri ta mike ta nufi cikin Gida tana kuka
“Haba Jalal me kayi hakane abunda kakewa Ilham yafara yawa gaskiya, koba komai kanwarka ce kuma mace ce, kadena dukanta hakan baze canza komai ba Fa”
Nunawa Jawwad wayarsa yayi
“Kalli abunda tayimin be isheta ba, ta tsaya a gabana tanamin hauka”
“Dukda haka kadinga hakuri, halin mata sekana hakuri, kasan shi so makahone waima tukuna, waima ya akayi wayarka taje hannunta har hakan tafaru?”
“Mtseww manta kawai”
Shine abunda Jalal ya fada kawai ya bi hanyar fita waje
Itakuwa Ilham tana zuwa cikin gida taga mummy a palour jikin mummy tafada tana kuka
“Ilham lafiyarki kuwa me akayi miki kike kuka,?”
“Mummy Yaya ne baya sona kwata² ya tsaneni, ni kadai nake sonshi mummy kiyi wani abu akai Dan Allah, zuciyata zata fashe”
Tausayinta ne Yakama mummy
“Is OK my dear, yi hakuri kidena kukan, Insha Allah Jalal bashi da matar data wuceki insha Allah, komai ze wuce”
“Mummy me nayiwa Yaya Jalal ne dabaya kaunata baya so naje inda yake”
“Bikiyi masa komai ba Ilham, haka dai halinsa yake na rashin son mutane, ya za ayi yace baya son mace kamarki, karya yakeyi, kidena kukan haka kar kanki yayi ciwo”
Haka mummy tai ta kwantarwa da Ilham Hankali

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button