Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Wow tauraro a cikin taurari kaina mussaman ne ban taba tunanin kana dariya haka ba, bakaga yadda dariya kemaka kyauba”
Gaba daya suka waiga domin ganin me maganar Hannah ce budurwar dasuka hadu da ita wancan karon, tayi maganar tana karasowa inda suke guri tanema ta zauna
“Jarumin maza meyabaka nishadi kake wannan dariyar haka ka fi ko yaushe kyau ko dan uwan ne yake baka nishadi”
Ta karasa maganar tana kallon Jawwad
“Uban wa yace kizo inda nake, me kike Nema a gurina ne kin uzzuramin kindami rayuwata meye hakane, waima wayagaya miki ina nan da kike bina”?
Wani kasaitaccen murmushi Hannah tayi
“Call me by my name Hannah, or any special name u choose,
Kasan ita zuciyoyin masoya kaman wireless ne, our hearts and souls are always connected, dan hakazuciyarkace tagayawa tawa zuciyar kana nan shiyasa nazo kuma nayi sa’a nasameka zuciyarka kawai nake bukata Jalal, in har kabani zaka huta da nacina, akasin haka kuwa zan cigaba da hanaka sukuni cikin dare ko rana har sekabani abunda nakeso”
Wani wulakan taccen kallo Jalal yai mata ya watsar da ita bece mata komai ba
Jawwad ne ya danyi gyaran murya
“Kinaji Hannah already Jalal akwai wadda takeson Sa kanwarsa ce kuma kinga…..
Dagawa Jawwad hannu Hannah tayi
” haba dan uwan masoyina meye laifina anan dan ina kokarin cikawa zuciyata burinta, kowa iya allonsa ya wanke, tayi nata kokarin nima inyi nawa wadda tai galaba ta kafa soyayyarta a zuciyarasa shikenan, ni Hanna babu macen data isa tayi takara dani akan soyayya,
Jawwad son danakewa dan uwanka ko matansa hudu sena kori biyu ya aureni saboda space din daya yamin kadan,
Kar ace rashin adalcin nawa yayi yawane da se ince seya kori kowa ya aureni saboda shidin nawane ni kadai”
Saroro Jawwad yayi yana kallonta
“In kagama jin tatsuniyar kazo mutafi inada abunyi” Jalal yafada yana mikewa
Hanna ma mikewa tayi tazo gabansa kaman zata shige jikinsa se wani irin fitinannen kamshi take
“Babyna kabani dama ko sau dayane in gwada maka yadda nake sonka mana, kuskurewa bukatata shizesa incigaba da uzzura maka har gidanku nasani zaka iya ganina a kowani lokaci, karkayi mamaki nasanka farin Sani a yadda kake a haka nake sonka, zan iya komai akanka, kagayawa kanwarka ta janye kudirinta na sonka ta barmin kai in bahakaba”
Ta kashe masa ido daya daga nan tai tafiyarta,p babban abunda yabawa Jalal mamaki dayakasa yimata komai
Jawwad ne ya janyo hannunsa suka hau motarsu suka nufi Gida
“Jawwad ka yadda mata matsalane, abunda zuciyarsu ta raya musu kawai shi sukeyi, yanzu ga haukan da wannan tayi min, amma zan dau mataki akai”
“Kabi komai a hankali Jalal, kasan in mutum yana kan ganiyar so makancewa yake so ba karyane ba, ka dena wulakanta Wanda yace yana sonka kai baka san a ya zaka fara taka soyayya ba,
Amma wannan Hannah ka nemi tsari da sharrinta because Dana kalli cikin idonta ya tabbatar da she mean what she said”
Haka suka cigaba tattaunawa har suka iso gida
Bayan sallar isha’i Jawwad yaje part din Abba ya tarar dashi shi ka dai, yagaya masa abunda ya faru jinjina kai Abba yayi
“Hmm Jalila iya rigima, halin mahaifinta ta dakko bata son raini Allah ya kaimu goben, zan San yadda za ayi”
Da asuba Abba ya taho kano be gayawa maama abunda ya faruba ya dai cemata zeyi fitar asuba zashi wani guri

Still wannan Daren ma messages din Hannah suka dinga shigowa wayarsa seda yagaji ya kashe wayar

Washe gari da safe Jalila ta shirya ta tafi makaranta, Daren ranar addu a ta kwana tanayi
Ba wai Allah ya sassauta fitinar da ta dakko ba, se dai Allah yasa kar Ummi ta korata kano
A hanyar makaranta ta hadu da yayan lubabatu data tsokana ranar akayi Sa a ya ganeta, ta Ganshi sarai amma taki guduwa tacigaba da tafiya a hankali,
Zuwa yayi ya sha gabanta
“Ke karamar Mara mutunci ni kika zaga ranan ko waike Yar iska”
“Wallahi kasake ka tabani sena tara maka jama’a nace zaka lalata ni shekara goma sha hudu ce zakayi a gidan yari bayawa”
“Au tunaninki barazanar ki zata hanani in casaki senaga uban da ya tsaya miki”
“Bari kaji in gaya maka idan kana shan kwayarka tagaya maka karya kayiwa mutane hauka, to karkayi gangancin gwada kwayarka akaina,
Dan wallahi sena kulla maka sharrin dazaka kare rayuwarka a prison”
Kafin kace meye wannan Jalila ta ware murya ta fara ihu iya karfinta hankalin jama’a ne yafara dawowa Kansu ana fara taruwa ta silale ta gudu ta nufi makaranta
Abunda yasa ta guduma gudun kar takuma shiga wata cakwakiyar bata fita daga wadda take ciki ba ga Ummi tace zata maida ita gidan su Jawwad da setasaka anmasa duka
Tana zuwa ajinsu ta tafi taje gurin zamanta ta hakimce ba tareda ta kula kowaba, “Allah ya biya Queen J Dama tunda yarinyar nan tazo kanta yake hayaki, se wani takama take, malamai ma kaman wani tsoronta sukeji segashi kinyi maganinta”
Haka dai seatmates dinta suka dinga zigata ita dai Jalila hankalinta yana kan batun Ummi
Bayan anfita break an dawo ba dadewa Hanan ta shigo ajin tana kallon kowa a wulakance ga malami a ajin amma Hanan batabi takan malamin ba ta tako
Tazo gaban Jalila
“Sannu uwar rashin kunya, dama na miki alkawarin kawo karshen rashin kunyarki,
Yau zakigane kin taba Yar gidan bullet kizo office bullet yazo da kansa”
“Amma kin bani kunya da kikazo da bullet kawai, ai na dauka barikin zaki dakko gaba daya su taho da egwa yadda in sun markadeni baza ageneniba dan dai bullet, ai bullet yayi kadan aga bayana dashi”
Jalila takarasa maganar hade da tsaki”nonsense “
Mikewa Jalila tayi tai gaba ta wuce hanan
Wato Jalila Yar bala’ice babu alamar risina a tare da ita tun tasowar Hanan take taka Wanda taga dama take jefa tsoro a zukatan duk Wanda yai kuskuren shiga hanyarta saboda takamar ubanta wani ne amma yau ta hadu da wadda tafita rashin mutunci
Haka ta bi bayan Jalila suna zuwa harabar ofishin director Jalila sukayi clashing da malama ramatu aikuwa Jalila ta tsaya
“Ita wutar munafiki ko tana karkashin jahannama ne,
Kekam baki dace da malamar makaranta me bada tarbiyya ba kema kina bukatar me baki”
Jalila ta gayawa malama ramatu sannan tai gaba abinta

Tana shiga office din director ta tarar da mutane ba Wanda ta kula kuma bata kalli suwaye a ciki ba ta shige

Share please
More comments more typing………….

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  20&21

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

    -My First Novel-

“Meyasa kikace kar ya sha”
“Nidai kawai kahana shi sha kar ya sha tea din nan”
Jawwad ji yayi gaba daya ta firgice masa
“Amma meyasa kikace kar ya sha?”
Sekuma tarasa mezata ce masa
“Am…emm.. Idan ya sha ze iya yin amai gara kaimasa tofi na ayoyin Qurani ya sha kafin kabashi abinci in Bahaka ba, ze iya bashi matsala eh..m.. In…nima malaminmu ne yafada mana a Islamiyya”
Da Jawwad yaji haka da sauri yasa hannu ya karbi cup din tea
Daga hannun Jalal
Jalal ne ya kalleshi
“Meye haka kuma?”
“Kanwarka tace karka sha tukuna, Dan huta ina zuwa”
“Kaga ni bani yunwa fa nakeji yaushe zan tsaya biye maka yarinya Karama tana juya ka”
ya yunkura ze karbi cup din tea daga hannun Jawwad yaji kansa ya kara nauyi dan haka ya koma ya zauna yana jujjuya kan
“Sannu bros”
Jinjina kai kawai Jalal yayi
Kamar yadda Jalila ta gayawa Jawwad yaje fridge ya dakko ruwa ya karanta ayoyin Qurani ya busa masa a ruwan yazo ya tsiyayo a cup ya bashi
Hannu yasa ya karba ya shanye ya ajiye kofin, ko minti biyar beyi da shan ruwan ba ya mike ya tafi bandaki ya dinga wani irin bakin amai
Jawwad ne ya bishi yana masa sannu ya kwashi mintuna yana amayar da wani bakin abu
Seda Jawwad ya Dan tsorata

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button