Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Harta yunkura zata tashi
“Maryaman Aliyu”
Ya kira sunanta dawowa tayi ta zauna ta kuma riko hannunsa

“Dan Allah ko bayan raina kar abinda matar usaman take miki yasa ki raba zumuncin dake tsakanin yayanmu”
Gyada masa kai tayi sannaan
Ta mike jiki a sanyaye ta nufi kofar fita,
Usman yana waje a bakin kofa yanajin duk hirarsu gwanin ban tausayi, haka usman ya dinga share hawaye kaman karamin yaro
Jiki a sanyaye Tafito daga dakin Usman ya nuna mata dakin da aka kwantar da inna
Usman ya koma dakin da Aliyu yake yaje gaban gadon Aliyu ya zauna ya riko hannunsa

“Dan uwana ya jikin naka ya kake ji yanzu”
“Yayana mutuwa zanyi bazan rayuba inaso in barmaka amana ne da duk duniya bame rikemin se kai”
Aliyu ya fada yana Jan numfashi da kyar
Yacigaba da cewa

“Dan Allah karkabari babyna tai kukan maraici, ko aure maryam tayi ban yadda ta tafi da yata agolanci ba, inason baby tayi karatu me zurfi, na addini Dana zamani
idan ta isa Shiga Jami a inaso takoma hannunka kasan tarbiyar ya mace seda tsayayyen namiji,”

Yayi tari jini yana fitowa daga bakinsa
Usman ne yake share masa jinin yana masa sannu,
Sannan ya cigaba da cewa

“Kar kayi yinkurin raba baby da maryam yanzu, seta isa shiga Jami a nakeso takoma hannunka, sannan ka tabbatar in baby ta girma maryam takoma garinsu tanemi yafiyar iyayenta, nasan kafin nan sun huce daga fushin dasuke da ita baby taga dangin mahaifiyar ta
Tunda kaga mu kenan bamu dayawa,
Yayana bana so iyalina suyi maraicina in baby na ta isa aure kazaba mata miji nagari karka manta ka rike alkawarinmu dan uwana,
Kacewa innarmu ta yafemin, kagayawa maryam da diyata da soyayyarsu zan koma ga Allah”
Ya kalli Usman dake ta zubarda hawaye INA kaunarka Dan uwana”
Tarine yakuma sarke Aliyu yana numfashi da kyar
Kalmar shahada ya dinga nana tawa, sekuma yayi shiru jikinsa ya saki
Usman rungume gawar Aliyu yayi ya fashe da kuka seda yayi me isarsa sannan ya mike ya nufi dakin da aka kwantar da inna mairo, maryam ya gani a gabanta tana bata ruwa tana shan ruwan da kyar wani yana dawowa

Yana shigowa inna ta dago kai ta kalleshi tare da fadin ya mutu ko Usman, Aliyu na shima ya tafi,”
Ta fashe da kuka tacigaba da fadin
” Allah ya karbi bakuncinka Aliyu na yafe maka duniya da lahira
Maryam kikula da kanki ki rike mana Jalila kaima Usman kakula da amanar da Dan uwanka ya bar maka, maryama karki manta da abunda nagaya miki inna mairo tayi maganar tana kuka tare da numfar fashi.

Lokacin da Aliyu yayi hatsarin aka kawoshi asibitin da inna take, an turota a wheel chair ta dubashi,, tunda ta Ganshi taga halin da dannata yake ciki ta karaya jikinta ya kuma rikicewa,

Duk abin naan da ake Zainab bata taka kafarta Asibiti ta duba jikin inna Mairo ba balle Aliyu da ba Sa shiri

Da gudu maryam ta fita ta koma dakin da Aliyu yake ta tarar da shi an rufeshi da bargo dagaske dai Aliyun ta ya mutu
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un maryam ta dinga maimaitawa tare da silalewa kasa sumammiya
Kafin akawo motar daza a dau gawar Aliyu inna mairoma ta cika


Ummi na zuwa nan a duniyar  tunani ta fashe da wani matsanancin kuka tare da furta Allah ya jikanka Aliyu na"

ta fada hankali.
“Ummina kiyi hakuri idan magana ta ce tabata miki rai kiyi hakuri banyi Dan in bata miki rai ba “
Jalila tayi maganar daga inda take kwance ba tare da ta juyo ba Ummi bata CE mata komai ba taci gaba da kukanta daga karshe ma ta fita ta dauro alwalaa ta tada salla

Washe gari da safe Jalila ta fuskanci still umminta bata walwala fuskarta ta kumbura saboda kuka
Jalila aikace² kawai take ba tare da ta kula ummin na ta ba seda tagama komai ta hado musu breakfast ta shiga dakin ta tarar da Ummi ta baje hotuna a gabanta tarike guda daya tanata kuka
Ajiye tray din hannunta tayi ta karasa gaban Ummi ta Sa hannu ta zare hoton da yake hannun ummin nata ta duba
Hotonta ne ita da Aliyu sun kalli juna suna dariya
Jalila ta dago ta kalli umminta, “

“Ummina soyayyar ce ta motsa kika Sa hoton abeena a gaba kina kuka,?”
Jalila tai maganar tana dan murmushi wanda iyakacinsa lebenta, saboda in da Sabo Jalila tasaba da ganin umminta ta dau hoton abeenta tasa agaba tana kuka, kokuma hoton family ta

Jalila ta cigaba da cewa

“haba ummina idan ina ganin karaya a fuskarki me kike tsammani daga gareni duk lokacin danaga hawaye a idonki karaya nakeyi ummina bana son ganin hawayenki kaddararmu kenan semu karbeta a haka muciga ba da hakuri Allah shiyasan abunda yake boye”

Jalila Tafada jikinta a sanyaye tana sharewa Ummi hawaye yayinda itama take zubda hawayen
Dukda karancin shekarun Jalila, in tana magana tana tsara zance daki² dukda tarin kuruciya dake dawainiya da ita wani lokacin tana tunani irin na manya

Riko hannun Jalila Ummi tayi tare da ajiyar zuciya,

“babyna Kidena kuka nima na dena ina tuna abubuwan dasuka wuce ne a baya Jalila bazan manta da halaccin mahaifinki ba a gareni, da kakaninki sunmin halacci ina miki fatan samun managarcin miji me kaunarki kaman mahaifinki sukuma Allah ya kai rahama kabarinsu”

“Ameen Ummi”
Sukayi breakfast bayan sungama ne Jalila takuma Cuban umminta tace

“ummina amma meyasa ba kyason muje garinku, nifa nagaji da cin zarafin da akemin akan danginki ni ko Yaya suke ina so nagansu a haka ko basu da addini ina sonsu ummi”

Jalila Ummi takira sunanta
Jalila ta dago ta kalleta ba tare da ta amsa ba

“Meyasa kika dawo gida hutunku be kare ba nasan akwai damuwa me ya faru”?
Turo baki Jalila tayi

“To ni Ummi meye be faru ba, wannan Yaya mairon tazo tana cin zarafina, tun ina yarinya bana gane kyamar da take min har na girma nagane ba ta dena ba why?”

Ajiyar zuciya Ummi tayi
“Nasan abun da matukar wuya amma kiyi hakuri, kaman yadda kikace qaddararmu ce haka”

“To Ummi su mutane basu San kaddara bane dan mutum ya musulinta daga baya se yazama laifi yazama aabin kyama, wannan wane irin abune
Ummi ni mukoma danginki ya fiye min wannan cin zarafin Indai zasu bari muyi addinin mu, gara mu zauna a cikinsu da hujja insan ni jikar kiristoci ce, a fada da hujja tun INA zanin goyo bansan komai ba Ummi mutane ke nunamin kyama saboda kawai daga baya kika tuba, ina kema a da musulma ce uminna enough is enough am tired asarar hawayen damuke yayi yawa”
Ummi kallonta kawai takeyi gaba daya setaga Jalila ta juye takoma mata Aliyu sak irin halinsu daya Jalila akwai saukin kai ita dai batta da Neman magana tana da kawaici amma bata iya fushi ba gaba daya hargitsewa take sekace Aliyu
Janyota Ummi tayi jikinta ta zaro wani hoto
“Baby na kinga hoton ki kina Jaririya kamanki daya da kakarki, wani lokacin kuma in kikai abu senaga kaman mahaifiyata”
“Haba Ummi yakike kokarin basar da maganar damukeyi, Ummi I mean what I said fa tun kafin ki haifeni kike fuskantar wannan matsalar, Ummi irin wannan cin mutunci da hausawa keyiwa Wanda suka musulinta daga baya har ina”
“A’a Jalila yan adamne mu in an mana ba dai² ba se muduba Alkhairan mutum kinsan wani Abu, baby na Alkhairan mahaifinki Dan uwansa da kakaninki gareni se in manta da laifin da wasu daga cikin hausawa maraasa fahimta suke min kinemi yardar Allah bana mutum ba
Kiduba tunda mahaifinki ya rasu dan uwansa yake dawainiya damu bamu taba kukan babu ba, a garin nan kalli yadda Mike zaune da kowa lafiyaa, indai bazaki dinga duba alkhairan mutane ba se sharri to bazaki taba yi musu adalci ba”
Nannauyar Ajiyar zuciya JALILA ta sauke
“Am proud of u ummina kinsa jikina yayi sanyi, to shikenan amma meyasa ba kyason zuwa Gida?”
“JALILA inason zuwa amma sekinyi aure in muka je yanzu bazasu kara bari in taho ba nikuma nafiso sekin yi aure semuje ki gansu, tsawon lokacin danayi ba tare dasu ba zuciyata na tare da su, nafiso koni zasu rikeni ke yazamana kina dakin mijinki shizesa hankalina ya kwanta”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button