Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Ya fada cike da kulawa yana basar da zancen Yaya mairo

Maama ta Dan yatsina fuska
“Wace Jalilan kuma bayan wadda na baroku tare a asibiti “

“Maama to ai tun dazu muka dawo baki ganta bane?”

Har Jalila zata fita daga dakin “
Nana tace tsaya mutafi tare karki fadi a hanya”
“Hh Nana kenan yadda nake jina yanzu ko dambe zamuyi ai sena zaneki yi zamanki bari inje”
Dariya Nana tayi lallai kinji sauki

“Hmmm kingani ko dan Allah ji yadda yake wani nuna damuwa akanta jikar arna wallahi in baki wasa ba Zainab, yarinyar nan da uwarta se ta shanye miki ya’ya,
arna ba abun yadda bane karki tona sallar datake ganin idon mutane ne watakila a boye a can inda take ita da uwarta suna zuwa coci”

“Wlh nima bakiga wulakancin da Nana tayimin ba saboda wannan yarinyar hadda in fita in barmata daki”
Sa’ada ta tsoma baki, Sa’ada irin halinsu daya da uwata bata da kunya Sam
Daka ganta zakasan idonta a bude take fuskarta tayi Jawur saboda bleaching

Ran Jawwad ne ya baci matuka
“Haba Anty mairo wane irin cin zarafi ne wannan kuma hada mahaifiyarta wannan…….

” dalla rufemin baki sakarai Wanda besan me rayuwa take ciki ba ina magana kana gayamin wai cin zarafine, Yaya mairo ta katseshi a tsawace
Kingani ko Zainab kinga abinda nake fada miki ko kalli Jawwad ina fada yana fada saboda rashin kunya wallahi ki raba yayanki da waccan Yar arnan in ba hakaba wallahi wataran zaki gansu a church suma

“Kaga Jawwad ta shi kafita jeka”
Maama tafada tana nuna masa hanyar fita

Mikewar nan dazeyi yafita yaga Jalila a tsaye idanunta taf da hawaye alamun taji komai

Girgiza kai yayi yafice zuciyarsa a cunkushe ji yake kaman shi akayiwa wannan cin zarafin

Da gudu Jalila ta dawo daki ta shige bandaki ta rufe kofa
Abin yabawa Nana mamaki meyafaru haka
Kofar bandakin tafara bugawa a hankali
“Jalila meyafaru ne?”
Jalila ta daidaita nutsuwarta tace
“Ina zuwa”

“OK nagane inkin fito ga abincinki nan”
Nana tafada

Itakam Jalila gefen bath ta zauna ta dunga zubarda hawaye masu kona zuciya
Why meyasa akemin wannan cin zarafin nida ummina ake kiranmu arna naga dai ba Wanda zece kaf zuri’arsa tun saga farkonsu har karshensu musulmaine,

Ummi meyasa kika auri abina kika haifeni, tun tasowata dangin mahaifina kemin wannan cin zarafin har yanzu basu dena ba yaushe wannan abun ze kare,

Wasu zafafan hawayene suka cigaba da zuba daga idonta
Bata san tsahon lokacin data dauka a bandakin ba tana wannan kukan har tagaji ta fito,
Ta canza kaya ta dai daita nutsuwarta ta fito palourn,
Yaya mairo basu tafi ba

Nana tana parlour tana karanta wani English novel “the wish”
Maama kuma tana kitchen

Kaman kullum har kasa Jalila ta tsuguna
“Anty ina yuni”
“Lafiya “
Shine abinda ta fada a wulakance
Tashige dakin maama zatayi salla
Jalila kuwa seta nuna ko a jikinta

Nana ta kalleta
“Ashe Allah yayi miki fitowa daga bandakin, sekace me haihuwa kika shiga kikayi tsit”

Murmushi Jalila tayi
“To wayasani ko itan nayi”

Sa’ada kallon Jalila tayi a wulakance
Ta tabe baki
“A gurin arna haihuwar shege a bandaki ai ba sabon abu bane”
Sa’ada tafa da

A fusace Nana ta dago zatayi magana
Jalila ta rigata

“Aikuwa dai ba kunya sukeji ba tunda basa kunyar su raini cikin shege su Haifa su rains
wasu kuwa zubarwa sukeyi
Kinga, gara laifin arna Dana muna musulmi Wanda yasani ya take kodayake wasu ai sunan ana musulin cine ba asan ma’anarsa ba”

Tana gama fadin haka ta shige kitchen gurin maama
“Sannu da Gida maama”
“Yawwa ya jikin “

Maama tafada cike da basarwa
“Naji sauki akwai abinda zan tayaki ne”
“A’a jeki abinki”

A parlour kuwa Nana ce ta dingayiwa Sa’ada dariya tace gobe ma kikuma in baki yasan meze fada besan abinda za a mayar masa ba

Jalila kuwa daga kitchen din nan harabar gidan ta fito ta dauki kujera ta tafi gaban flowers ta zauna,,
Tanata tunani zuciyarta sam ba dadi, ga wani Abu da ya tokaremata a kirji Wanda tasan Bacin Raine, gashi rabonta da abinci tun Wanda taci da safe a asibiti Wanda Nana takawo mata dazu bataci ba ko yunwar bataji, saboda Bacin rai

taga hakan baze fishsheta ba dan haka tafara rera karatun Qur’ani cikin sauti me dadi

A hankali taji zuciyarta tana sanyi yanayin yayi mata dadi ga yammaci ga flowers din na dauke da furanni masu kyau Dan haka taci gaba da karatun cike da jin dadi da kwarin gwiwa

A hankali take jin taku ana tahowa inda take bata waigaba kuma bata dena karatunta ba

“Masha Allah “

Taji muryar Jawwad yafada seda ta kai karshen ayar sannan ta tsaya
Ko ba a gayamata ba tasan tare yake da mayennasa wato Jalal saboda taji kamshin turarensa
Gabanta ya zagayo ya tsugunna

“Dafatan ban katseki ba ya sayyada?”
Jawwad yafada
“A’a yayana, sannu dazuwa”
” cigaba da karatunki”

“Ai na idar dama Abeena nakewa Allah ya kaimasa ladan kabarinsa,
Babban abinda zamuyi idan iyayenmu na Raye shine muyi musu biyayya kar mu yadda muyi sa’insa dasu ko mudaga musu murya,
Fushinsu masifa ne a rayuwar mu, tunda bamu ISA mu biyasu ba dawainiyar dasukayi damu ba, in sun rasu kuma muyi musu addu’a saboda bamu da tamkarsu”

“Wannan gaskiyane sister lyk no other ina alfahari dake”

Lallai yarinyar nan kullum in muka hadu seta gayamin bakaken magana waini zatayiwa wa’azi
Kijira zakiga yanda zanyi maganinki a karo na gaba
Jalal yayi wannan maganar a zuciyarsa

“Jalila nasan kinji abinda Yaya mairo tafada amma Dan Allah………
” shhhh ni banji komai ba Yaya kamanta kawai” Jalila tayi maganar tana murmushi

“Kai ni nagaji malam Kasan banason jira ka ta shi muje kabani abinda zakabani in tafi seka dawo ka cigaba da shirmen”

Hakan yayi dai² da fitowar su Yaya mairo Maama tayo musu rakiya

“Zainab Dan Allah dubi danki kalleshi ga yadda ya gurfana a gabanta, kaman zata masa gafara wannan shegiyar yarinyar in baki da mataki akanta ba setasaki kika,
Wannan yaronnaki yadda yake rawar kai akanta seta dilmiya shi”

Jiki a sanyaye Jawwad ya mike ita kam Jalila sunkuyar da kai tayi
“Bahaka bane Anty mairo ina mata sannune”
“Ubanka kake mata ba sannu ba wadda kayi mata a asibitin bata isa ba sakarai kawai ka wani gurfana a gaban ta sekace uwarka”
Shikam Jalal tuni ransa ya gama baci yana kuma jinjina hakurin Jawwad da shine wallahi babu matar daze tsaya tana masa masifa haka

“Dan Allah Jawwad kaje kabani in tafi nagaji Kasan bana son tsayuwa kuma wannan matar tazo tanawa mutane hayaniya da shirme aka zata sawa mutane ciwon kai
????????????????
JALAL yayi maganar cike da masifa

“JALAL itama mahaifiya tace fa yayar maama ce”

Sakin baki Yaya mairo tayi tana kallon ikon Allah

Itakam Sa’ada ganin JALAL seda gabanta tayi mummunar faduwa

Maama tayi shiru saboda bata shiga shirgin abotar su tasan halin JALAL sarai

“To ni Ina ruwana kai ka taba ganin me uwa biyu
Dalla ka tsaya ana zaginka haifarka tayi meye na zaginka dan tana yar mamanka haka akeyi?”

“Wannan Dan iskan fa daga ina”
Yaya mairo tafada tana kallon Jawwad
“Emm da…

” magana nake maka kana kame² nace wannan Dan iskan yaron Mara mutunci daga ina Zainab magana nake kunyi shiru kuna kallona”

Itakam Jalila silalewa tayi tabar gurin

JALAL yazo gaban Yaya mairo yatsaya “
fadi da kyau ni dan iska ne Mara mutunci, amma kinfini kama dasu tunda kema kin haifi dan iskan boye da bakowa yasan shiba

Dafa kafadarsa Jawwad tayi
“Bros Dan girman Allah kayi shiru mana Yayar uwata ai uwace ai yakamata kaimin kara” yafada jikinsa a sanyaye

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button