Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

” kashedi nawa nayi maka game da Jalal, kai kake kara hure masa kunne meyasa kake bibiyarsa haka?
Why? “

“Bani yakamata in baka wannann amsan ba kajira lokaci”
Daga haka jeje yasa kai yai ficewarsa

Jawwad kuwa ransa a bace yashiga bedroom din, Jalal ya tarar yana ta bacci, hade da surutai cike da maye
Girgiza kai kawai Jawwad yayi Allah ka shiryi bawanka Allah ka nunamin Jalal yazama mutumin Arziki.

Washe gari da safe iyalan gidan sun hadu a palour suna karyawa, kowa ya maida kai yanacin abinci amma banda Jalila wadda taketa juya cokali tana cakalar abincin JAWWAD ne ya kalleta

“Lafiya kuwa sisy ba kyacin abincin fa ko akwai damuwane?”
Jawwad yafada cike da kulawa

“Nima na lura da hakan bros tun jiya naga bata walwala”
Nana ta fada tana kallon Jalila

Maama kaam Dan kallonta yayi ta tabe baki ta cigaba da cin abincinta

“Duk Ku tsaya Yar albarka gayamin meke faruwa ne”?
Abba yafada cike da kula yana kallon Jalila

Hawaye ne yazu bo mata Wanda bata San zasu zubo ba,

” subhanallah Jalila meyafaru, me akayi miki”
Suka shiga hero mata tambayoyi

Jimin munafukar yarinya wayamata wani abu dazata kama yiwa mutane kuka kalli yadda duk suka bats attention lallai maganar Yaya mairo akwai kamshin gaskiya
maama tayi zancen a zuciyarta

Gaba daya attention dinsu ya dawo kanta suna mata tambayoyi

“Abba ni Gida nake so in koma”
Tafada a hankali

“Wani abun mukayi mikine?”
Nana tafada kaman zatayi kuka

“Kunga Ku tsaya, Jalila anyimiki wani laifinne in wani abun mukayi miki kigaya mana”
Jawwad yayi maganar yana kallon cikin idon Jalila
Abba yayi gyaran murya yace

“Yarinyar kirki meyasa kikeso kikoma Gida? ko mune ba kyasan zama damu”

Girgiza kai tayi
“a’a Abba ni ba abinda kuka yimin kawai ina kewar ummi ne, sonake inkoma gurinta”

Maama ji tayi kaman ta kwashe Jalila da mari saboda gulma Dan kawai tanaso takoma Gida shine zata yiwa mutane kuka salon ace wani Abu sukayi mata

(Wato maama taji zigar yaya mairo)

“To shikenan yarinyar kirki yaushe kikeso ki koma gidan?
Tunda kin gaji da zama damu”

“A’a Abba ba gajiya nai da zama daku ba, ba abinda kukayi min,
Gobe nakeso in koma”
Tafada tana sunkuyar da kai

“To kibari ranar juma’a insha Allah se Jawwad ya maida ke gida hakan yayi miki?”

Murmushi Jalila tayi tare da gyada kai

“Shagwababbiya kawai shine seki mana kuka Dan kina kewar Ummi?”
Jalal yafada cikin zolaya

Maama dai batace uffan ba
Haka dai suka kammala breakfast din

Suna komawa daki Nana ta kalli Jalila
“Jalila me mukayi miki zaki tafi kibarni
, hutu fa be Kareba
Naji dadin zuwanki meyasa zaki tafi ki barni”?
“Haba Nanancy na nifa bukuyi min komai ba kawai inaso in komane”

“To yaushe zaki kuma zuwa”?
“Zan kuma zuwa Nana karki damu”
“To shikenan zanyi missing dinki”

Nana ko zan kuma zuwa gidanku se bayan dogon lokaci, idan nacigaba da rabar Ku kiyayyar da mahaifiyarku kemin zata fito fili
Ga wannan azzalumin makocin naku abokin Jawwad

Amma a zahiri se ta rungume Nana
Karki damu Yar uwata I will miss you too

Ran Alhamis da daddare Shirin komawa Gida sosai Jalila takeyi ta hada kayanta cif ji take kaman ba itaba zata koma Gida gurin umminta

Nana ce ta raka Jalila gidansu Jalal domin tai musu sallama,

Ilham suka Tatar tana shirya abinci a palour
Kaman kullum Ilham se hararan Jalila takeyi kuma har Jalila tai kwanciyar Asibiti bata taba cemata ya jiki ba

“Gurin mummy mukazo ba gurin Jalal ba naga kina hararata”

Jalila tafada da sigar Neman magana
“In ma gurin nasa kikazo biki isheshi kallo ba Dan ba macen dayake gani bayan Ilham”
Ilham tai maganar cike da tsiwa dakuma gadara

Aikuwa Jalila tafara dariya
“Shi Jalal dinko, yanzu akansa kike wannan abun hh wani jan idonsa kaman ansa masa tear gas”
Jalila tai maganar tana dariya

Iya kuluwa Ilham ta kulu amma kafin tayi maganar Nana tace
“Dan Allah kuyi hakuri wannan wasannaku karshensa fadane
Ina mummy? gurinta mukazo”

Haka Ilham ta kaisu part din daddy Dan mummyn tana can
Itakuma tadawo palour

Jalila tayi musu sallama cewa gobe in Allah ya yadda zata tafi
Daddy yace to ta gaida mamanta yayi mata addu’a kuma insha Allah zemata aike haka sukayi sallama da mummy ma

Suna fitowa daga part din Daddy kaman kullum wata dramar ake

JALAL da Ilham se masifa yake zazzaga mata kaman ze dake ta tana bashi hakuri kaman wani ubanta

“Kina abu kaman wata dabba kinfiye naci wallahi inkina da zuciya karki kara zuwa inda nake kokice zaki dafa wani abu kibani, bana so ko ana dolene?”
Idon Ilham taf hawaye
“Dan Allah kayi hakuri Yaya bazan iya dena zuwa inda kake ba”

Aikuwa dariya Jalila ta kwashe da ita
“Tab laila majnun amma gaskiya iska tana wahalar dame kayan kara”

Wannan wace irin mayyar yarinyace tantiriya me bakin naci

Share please

Nasan kunada Tarin tambayoyi but keep following me amsoshin suna nan tafe cikin littafin
ABDUL JALAL (2020)

More comments more typing……………

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  11

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
What’s https: //chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Is a free book

Ina yinku AbdulJalal novel fans irin???????????? da duk sauran masoya wannan novel ina jin dadin comments dinku love u all ❤❤❤

I want comments not stickers or just thanks????????????????
Your comments give me courage

     -my first Novel-

Kafin su Ankara takuma yi musu wani shouting din
“Ku tafi kubani guri”
Sun² suka fice su ka bar gurin dakinta ta koma ta cigaba da sintiri to yanzu ya zatayi meye mafita washe gari takuma sawa aka nemo mata
Abiola da yarabanci sukayi magana wannan karon

(kunsan dai ni ba yarabanci nake ji ba Dan haka bansan me suka ce ba)

Naga Abiola ya daga kai ya kalleta a razane

“Ko bazakayi ba”
ta tambayeshi

“Zanyi yanda kikece”
Ya fada Kansa a kasa

“Mark u idan maganar nan ta fita wani yajita hukuncinka shine..
Tai taku biyu
” life imprisoned!!! “
Ya dago da sauri ya kalleta

“Yes ” tafada tana kallonsa “you can leave”

Da la’asar har camp Abiola yaje ya lallabo Aliyu ya fito da shi kan cewar za suje yawon shakatawa ne,

Wani hadadden lambu ya kai Aliyu, an kawata lambun da kayan itatuwa masu matukar kyau gurin yayiwa Aliyu kyau matuka,

“Gaskiya gurin nan yayi kyau so cool”
Aliyu yayi maganar yana murmushi tare da shafa Kansa

“Dagaske gurin yayi maka kyau”
Sukaji muryar mace a bayansu
Abiola yasan muryar wace dan haka yakara nutsuwa tare da sunkuyar da kai

Aliyu ne ya waigo yaga me maganar sanye take da riga da skirts na atamfa kanta ba Dan kwali
matashiyar budurwace bazata fi shekara goma sha takwas ba ba dai fara ce ba amma tana da kyau black beauty ce

Takuma maimaita abinda tace
“dagaske gurin nan yai maka kyau”
Tafada tana murmushi, Wanda seda dimples dinta ya lotsa ta kara kyau
Shima Aliyu murmushi yayi mata

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button