Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Jalila tayi shirin kwanciya Hanan takirata ta dinga yimata surutu amma Sam Jalila sama² take amsamata Dan ba komai take ganewa ba, haka sukayi sallama da Hanan, Jalila wadda a wannan lokacin dazaka tambayeta me sukace a wayar bata saniba Dan hankalinta ba akan wayar yake ba
Haka Nana ma ta isheta da tambayoyin meyake damunta, tarasa amsar dazata bata
Daga karshe tace mata bacci takeji
Sukuku haka Ilham ta wuni tareda tambayoyi fal zuciyarta na son gano, abunda yafaru makircin Jalila ne kokuma wani abu daban, gaba daya tarasa meyake mata dadi
Ta kira yaseera ta gayamata komai ita kanta yaseera kanta ya kulle amma tace ta bari da safe zatazo su hadu
Koda Jalila ta kwanta bacci gagararta yayi, se tunani, da tambayoyi fal zuciyarta, a haka bacci barawo ya saceta
Jalal ta gani a daddaure da sarka a cikin wani daki a galabaice, se a man gudan jini yake, wasu mutane masu bakaken kaya a zagaye dashi se kara matseshi suke da sarkar, JALILA tanata magiya su sakeshi kar ya mutu, daka mata tsawa wani yayi a cikin su
“Ke uwar shishsigi!!!! Kinfara mana katsalandan a cikin aikinmu damukayi shekaru munayi, kishiga hankalinki, inba hakaba kema zaki shiga cikin aikin Dan bazamu bari ki rusamana aiki ba”
Daga can taga Ilham ta shigo dakin ta zare wata wuka ta nufi Jalal
“Ilham me zakiyi haka, Dan uwankine fa in kika kasheshi fa”

Share please
More comments more typing……………………..

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:30 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 38

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys ❤❤❤❤❤

      -MY FIRST NOVEL-

Jalila na zuwa daidai nan a mafarkinta tai firgigit ta tashi zaune tana gumi, Ta juya ta kalli Nana tana ta baccinta, ita kuwa se maida numfashi take kamar wadda tayi dambe, tanata jujjuya mafarkin nan datayi
“Tabbas akwai wani abu a boye amma ta Yaya zan Sani, taya zan gane,” gani tayi zaman tunani baze mata magani ba
Mikewa tayi ta dauro Alwala ta koma kan gadon ta zauna tafara karanta Qur’ani a hankali, a haka har bacci yakuma dauketa wayewar garin yau da Nana da Jalila tareda Ilham sunata hada² shirya abinci domin bakin dazasuzo wato su hanan, suna cikin aikinne, Naja’atu tazo Naja kanwar Sa’ada ce wato “ya’yan Yaya mairo, yayar Maama, daka ganta kasan kanwar Sa’ada ce saboda kamar dasukeyi,
Da Halima ta fara clashing a parlour, ” ke ina Maama take da sauran mutanen gidan naga bakowa?”
“Sunana Halima”
“Bazance Haliman ba, ke zance, kina Yar karere Yar aiki, zan tambayeki, kicemin wani sunanki Halima, koma wace, matsiyaciya kawai mara galihu” Halima tayi saroro tana kallonta, daga baya kuma tace
“Allah yabki hakuri, hajiya tana bangaren Alhaji, sauran mutan gidan kuma suna dakin girki”
Jalila ce tafito daga kitchen da roba a hannunta
“Ya dai nakejin hayaniya, leemart meya faru”
“Bakomai bakuwa akayi”
Jalila tana kallon Naja, taga kamanin Sa’ada, tasan Yar uwarsu ce seda gaban Jalila ya fadi
“Sannu da zuwa, bari akira maaman”
“Kekuma daga ina, tambayarki nayi ko gurinki nazo”?,
Jalila ta dan murmusa
“ai banyi kalarkiba dama balle kice zakizo gurina”
Halima a ranta tace yawwa uwar dakina shiyasa kike burgeni, Jalila ta kalli Halima
“Leemart ga robar ki debo sugar a cikin”
Daga nan suka watse sukabar Naja a parlour, Naja tai kwafa lallai
“Yan aiki har sun fara samun wannan damar haka a gidan nan”
Dakin Maama Naja taje amma bata ciki, Dan haka tanemi guri ta zauna, bata dadeba Sega Maama tazo
“Naja saukar yaushe,?”
“Tun dazu nazo”
“Amma ban saniba, meyasa Nana bata kirawoniba”?
” oho ni ina na ganta, masu aiki nagani, sukamin rashin kunya a parlour, Maama yaushe yan aikinki suka samu wannan damar,”
” yan aiki kuma? Ai Halima ce kawai Yar aiki “
“A a hadda wata, tanemi tazageni danni bansanta ba, wata Mara mutunci”
” Ke ba Yar aiki bace ba, Yar kanin megidan nan ce Jalila ce fa”
“Wai itace ta girma tazama haka,? Har tanemi ta zageni”
“Ai indai wannan yarinyar ce zatayi fiye da haka”
“To me ta keyi a gidan nan”?
” hmm ta dawo nan da zama”
“Aikuwa zan saita miki ita kafina in tafi, bari inje kitchen din in karemata kallo”
Duk sun maida hankalinsu akan aikin dasukeyi sunayi suna tana hira, Naja ta shigo kitchen din ba ko sallama
“Nana aiki kuke haka”
Waigowa Nana tayi
“Naja yaushe kikazo,”
“Tun dazu nazo, masu aikinku sukayimin rashin mutunci”
“Suwa kenan?”
Nana ta tambayeta, saboda wulakanci seta nuna Jalila, Jalila a ranta tace “wato hali zanen dutse, yadda mahaifiyarsu Sa’ada ta tsenata har y’ayanta haka suke mata wannan tsanar
Nana ta kalli Naja, lallai ma Naja, Jalila tayi miki kalar masu aiki? To Yar masu gidace me cikakken iko”
“Yar masu Gida kuma?, to ai ya’yan masu Gida mutum biyu nasani, yaushe kuma wannan tazama Yar masu Gida”
Jalila kam tayi kaman bata San da mutum a gurin ba, Nana a hasale tace
“Kai Naja Wai baki gane JALILA bane”?
Saboda iya gulma secewatayi
” ke haba itace tazama haka, tai wannan kilewar, Yar gidan kiristan nan ko?”
“Kekam Naja wallahi keda Yaya Sa’ada ban San wadda tafi wata rashin hankali ba”
Duk yadda Naja taso Jalila ta tankamata taki, dan ita yanzu bata ita take ba abubuwan dasuka dameta ma sun isheta, sema karatun Qur’ani data fara a fili, cikin
kira arta me dadin sauraro (???????? Jalila Yar duniyace wato ta maida Naja shaidan, gara tanemi tsari da ita)
Karfe sha biyu da rabi suka kammala, shirya abincikan dasuka yi,
Sukaje sukayi wanka suka canza kaya

Yaseera da Ilham sun kule a daki suna tattaunawa, Ilham fuskarta cike da damuwa take magana
“Wallahi yaseera kaina ya kulle nakasa gane ma meyake faruwa, kullum abu kara hargitsewa yakeyi, babu cigaba, kinga rashin mutuncin da yayimin, wai yayi bakuwa namata rashin mutunci namasa krya, waikuma ranan ankkirashi a waya na daga na zagi wadda takirashi, ni abun tambayar wacece, haka hardayake kumfar baki akanta, iya sanina baya shiga sabgar mata, nakasa gane wace ce, da nayi tunanin ko Jalila ce amma kuma naga itama yana kokarin yimata rashin mutunci da kyar nasamu na gudu, Dan rashin mutuncin da nayi masa jiya daya kamani seya kusa kasheni”
Yaseera ta nisa sannan tace
“Abun da daure kai Ilham, amma fa seta yiwu wani makircin Jalila ta hada”
“Anya kuwa Jalila ce tunanina yafara bani ko wata ce daban”
“Ke bar mutum kawai Ilham yanzu abunda ze faru, kama ta yayi mu bigi cikin Jalila maybe mugane wani abu”
“Ta Yaya? Wannan me mugun wayon”
“Da hikima zamuyi ai bada fadaba, amma sekin boye wannan fushin naki, sannan abu na karshe da zamuyi shine, duk yadda za ayi kawai, ayi Auren nan a wuce gurin”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button