Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

“Tabdijan kice abun babba ne ai in gaya miki dana ganshi a dakin bayan ya fita nakoma gurin Yaya Jawwad nai masa magana akan ya rabu da Jalal bashi da tarbiyya Ashe yadawo daukar wayarsa yaji duk abinda nafada bakiga kallon da yayi min ba”
Dan zaro ido Nana tayi
“Are u serious”
“Wlh dagaske nake yaji me nace bakiga mugun kallon da ya dingamin ba”
“Tabdijan Jalila garin Yaya haka tafaru aikuwa kinci sa a Yaya Jawwad yana gurin da wallahi inaga seya kusa sumar dake”
“To dai Allah ya rufamin asiri
Bari in Dan kwanta in huta”
“Sarkin bacci ko gajiya ba kyayi Allah ya kiyaye haduwarki dashi”
“Shi wa?”
“Kinfini Sani”
Murmushi kawai tayi ta hau gadon ta kwanta.
Nana kuma tacigaba da ninke kayanta,
Befi 10 minutes da kwanciyar Jalila ba
Ilham tayi sallama

“Mutuniyar kinji gori kenan yau se gashi kinzo anya makuwa bawani abun yakawoki ba” Nana tafada cikeda zolaya

“Hmmm ke dai bari Nana akwai magana ne,
sister dinki bacci takene?”

“Eh bacci takeyi meyafaru”
Cike da damuwa ta kalli Nana
“Nana Yaya Jalal ne”

“Wani abunne yasameshi?”
Nana ta tambaya
“Aa Nana kin San dai zancen, ta tsuniyar gizo bata wuce koki hankalin yaya Jalal Sam baya kaina wlh ko kallo ban isheshi ba komai nayi bana birgeshi ke mukwana gida daya mu tashi amma semu shafe kwanaki ko kallon inda nake beba
Abun yana damuna Nana ina matukar kaunarshi amma shiko a jikinsa ni ban San meyake damun saba kaman ba mutum ba”
Nana ta dan dafata da sigar rarrashi
“Ilham inso cutane hakuri maganine kicigaba da hakuri kina addu’a insha Allah komai zezo karshe”

“Nana in ba ya Jalal na aura ba bazan iya zaman aure ba, dashi nake so na rayu yazama uban yayana ,
nifa ko karatu bazan iya cigaba ba sonake munayin SSCE ya aureni narasa yadda zanyi gashi mummy ma ba jin maganarta yake ba itama tayi kokarinta amma yaki saurarona
Dama daddy ba a maganarsa don baze taba tursasa shi ba Ina cikin damuwa”
Daga inda Jalila take kwance ta tashi zaune Dan taji hirar dasuke ba bacci take ba, dannan waya take,
“Aikuwa kina tattare da nasani a rayuwarki damuwa yanzu kikafara muddun kika zabi dan giya a matsayin uban yayanki karki biyewa son zuciya ki cutar da yayan dazaki Haifa a nan gaba auren Jalal babu abinda zaki kwasa bayan bacin rai da dunbin danasani”

Kallonta Ilham tayi tana nanata Kalmar Dan giya aranta lallai Jalila bata da mutunci a gabanta take kiran Jalal Dan giya banda shishshigi da munafurci wayasakota a ciki
Lallai bata sanniba akan Yaya Jalal banki imbata da kowace ce ba
Ta kalli Jalila rai a bace

“Kekuma wayasa dake a gabana kike cin zarafin Dan uwana kuma masoyina Dan giya wannan ba magana bace at least yana abokin yayanki ya cancan ci ki mutuntashi”

“Taya kike tunanin in girmama Wanda be girmama mahaifiyarsa ba, Sam Jalal ba abin girmamawa bane, kema zuciya yace take rudarki, kokuma akwai wani sirri a ranki da kike boyewa, Wanda bakowa yasani ba
in bahakaba babu macen dazatayi sha’awar rayuwar aure da Wanda bayajin maganar iyayensa inba kema irinsa bace fitinanniya””

Da sauri Ilham ta kalli Jalila,

Jalila ta Dan daga mata gira
“Nayi karyane”

Gaban Ilham ne yafadi akwai wani abu danake boyewa da bakowa yasani ba ya akai tasan hakan???

“Ba abin mamaki ko tuhuma a maganata, shawarace kawai tun wuri kisake tunani kinemi hanya me bullewa wannan shshashan be cancanci zama miji ba balle uba in bahakaba seyasaki kukan da kekanki bazaki iya hana kanki ba” cewar Jalila

“Enough please meyasa baki da ta ido kinacin zarafin dan uwana kina kiransa da dan giya agabana!!” Ilham tafada cikin shouting

“Hold on madam ba ayimin shouting” Jalila ta katseta

“Haba mene haka kukeyine bafa yarane kuba wannan be kamata ba we are all sisters”

Tabe baki Jalila tayi tace
“Ilham nasan zakiji ba dadi amma gaskiya nagaya miki”
Bari inje waje in Baku guri ina bukatar recharge card zani insiyo ta dau hijabinta tasaka tafice

Gajiya yayi da kwanciya ga bacin rai yana fama a banza akan wannan shedaniyar yarinyar yafito kofar Gida da sigarinsa a hannu kaman kullum

Bari yaje Jawwad yazo yarakashi su Dan zaga gari koze rage takaici ya sha sigari kusan kara 7 amma har yanzu ransa a bace yake

Cikin gidansu Jawwad yakoma yanufi bangaren Jawwad wayarsa tafara ringing tsayawa yayi ya dakko wayar Cwt dad ne ke kiransa murmushi yadanyi yadaga wayar.

Tazo fita taganshi tsaye bangaren Yaya Jawwad yana amsa waya yana murmushi
Kai amma wannan akwai nacin bala’i wai dama yana murmushi

Dogon tsaki taja Wanda yasashi waigowa
” dubeshi dan Allah kalli askin kanka daganin wannan askin bana mutanene kirki bane kullum baki cikin fidda hayaki kaman salansan tifa ko gajiya bakayi, kuma kazo ka likewa Dan uwana mutumin kirki kana nema ka lalata shi,
Kai dashi akwai banbanci shi yana da tarbiyya yana girmama iyayensa sabanin kai kaga kunada banbanci!!!””.

(Turkashi kindebota da zafi Jalila mekuke tunani zefaru keep following aakwai cakwakiya fa!!!!!!!!!)

Please share ▶▶▶
more comments more typing…………

https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL.

????️????️????️????️????️
[8/31, 8:26 AM] Safiyya: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_

  _WRITTEN BY AISHA HUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE-  6

PART 1

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

I want comments not stickers????????????????
Comments dinku shine kwarin gwiwata

   _My first novel_

“Gobe ma in kikaga Jalal kikuma zaginsa useless creature kawai”

Yayi tafiyarsa ya barta a gurin tana ta mimmikewa tana fama da numfashi ta galabaita har a tafara fita hayyacinta.

Mummy ce tafito daga sashen daddy zata shiga kitchen ta dinga jin kakari da nishi, dawowa tayi da baya a Dan tsorace, tana duba meke wannan nishin,
Jalila tagani a zube a gurin tafita hayyacinta numfashinta nata fita da sauri

(Lallai JALILA ta sha hayaki)

” subhanallah ke Jalila meyafaru meke damunki??”
Tazo tana taba ta
“Ohh ni khadija meke damun ta kodama tanada athma ne

” Ilham!, Ilham!!, Ilham!!!,”

Tashiga kwala mata kira

“Ke Ilham kifito da sauri”

Itakam Nana gajiya tayi da jiran Jalila Dan haka kawai tayi tafiyarta ta shige Gida,kai tsaye taje dakin mummy

“Mummy mun dawo “
“To sannunku ina Jalilan?”
“Wayarta ta manta ta koma dakkowa shine na taho”

Kai inkuma Yaya Jalal ne yamata wani abunfa tai wannan tunanin a ranta
da sauri tafito ta nufi gidansu Jalal

Shikuwa Jalal gurin Jawwad yatafi abunsa, kaman be aikata komai ba hankalinsa kwance
Amma lokaci2 in ya tuna maganganun Jalila se ransa yabaci .

Da gudu Ilham tafito
“Mummy lafiya kuwa?

” zo kiga Ilham dama tanada asthma ne ko wani cutan?”
Ilham ta Dan zaro ido

“Mummy ya za ayi in Sani”?

” maza jeki gidansu kifada suzo akaita Asibiti kar ta mace min a Gida”
“To bari in je”
Mayafi Ilaham ta dauka ta fito da sauri a bakin gate taci karo da Nana
” yawwa Nana Jalila dama tanada asthma ne kowani cutan?”

A firgice Nana ta kalleta
“Asthma kuma? Bata da wani asthma, me yasameta?”
“Zo muje kyagani”

Ilham tafada tana janyo hannunta zuwa cikin gidan

“Subhanallah Jalila meya sameki?”

Nana tafada tana jijjiga Jalila amma Jalila bata San me akeba tafita hayyacinta
Da gudu Nana ta tafi gida domin sanar dasu abinda yake faruwa,
tana shiga gida a harabar gidan ta ci karo da su Jawwad

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button