Uncategorized

ABDUL JALAL PART 1 HAUSA NOVEL

Ilham ta kalli yaseera tace “yaseera Dan Allah mubar batun yarinyar nan kawai munemi mafita”
“Wace mafita Ilham, so muke mu tabbatar da zarginmu tukuna”
“Yaseera lokaci fa kuremin yake, nagaji zanyi abunda naga ya dace”
“Ilham kibi komai a sannu kar garaje yakaiki ya baroki”
“Nasan yadda zan tsara komai ki manta da ita kawai”
“To Allah ya taimaka”

Suna shiga Gida Jalila bata tsaya ko inaba ta nufi dakin su,
Jawwad jikinsa yayi sanyi sosai, Jalal ya kalleshi yaga Jawwad yayi wani iri kaman Wanda yayi wani babban zunubi
Dariya Jalal yai
“Wai meya sameka ne kawaniyi shiru”
“Hmm ba komai,” inni Jawwad
“Dan tace tana sonka shine kawani damu, meye a ciki to, naga dai su biyun duk dayane”
Jawwad ya kalleshi
“Allah ko? Eh ai shiyasa kai gakanan kun jone da Ilham, Dan tace tana sonka, kana sonta kaima”
“Mtseww Dan Allah idan ina magana kadena sakamin maganar banza”
“Ilham dince maganar banza?”
“Ban saniba”
Ya mike yai waje yabarwa Jawwad dakin
Jawwad yayi murmushi “Ashe ba dadi”
Yana zuwa Gida yaji yanason shan madara, Dan haka ya duba fridge dinsa, bawani lemon kirki a ciki duk se giya, rufe fridge din yayi, ya mike ya tafi cikin Gida, yana zuwa yatarar da Ilham a palour bebi takanta ba ya wuce fridge ya bude ya dau abunda yakeso, yana rufe fridge din ya juyo yaga Ilham tsaye a bayansa
Gefenta yayi ze wuce, takuma dawowa gabansa
Ya kalleta “meye Haka?”
“Abunda kagani mana, Yaya Jalal meyasaka nishadi haka? yau, naganka kana dariya dakuma fara’a abunda ni bakayimin,”
“Zaki bani hanya kosena barar dake a gurin nan”
Hannu ta mika masa “bani in tayaka daukar kayan”
“Jalal dama kana gidan nan, amma baka Neman inda nake”
Suka jiyo muryar mummy, ya juyo ya kalli mummy
“Idan nazo mezan miki? Bani da wani amfani dazan miki, be kamata in dinga zuwa ba”
“Ni kake gayawa haka ko?”
“Yau nafara gaya miki? Kina son maida hannun agogo bayane kawai”
“Jalal kaji tsoron Allah, anya kanaso ka gama da duniya lafiya”
“Mummy ke yakamata kiji tsoron Allah tun a farko ba a yanzuba da aikin gama ya Riga ya gama”
Ilham ta Dan juya baya tayi murmushi, a ranta tace Ashe kana sane da komai, Jalal mahaifiyarka tayi kuskuren da kake karbar hukuncin
Mummy ta kalli Jalal
“Yanzu JALAL….
” Enough mummy, baki da abunda zaki gayamin in saurareki”
Yana zuwa nan a zancensa yai waje, yayinda mummy ta zauna akan daya daga cikin kujerun palourn tafara kuka

Naja ta shigo dakin su Nana ta tarar da Jalila kwance akan gado Nana kuma tana gyara dressing mirror, kalli Nana “Nana wai bakin sun tafine?”
“Eh sun tafi” ta kuma gyara tsayuwa sannan tace
“Y’an uwansu Jalilane?”
“Eh ya akayi”?
“Naga suna kamane sosai da wannan yarinyar, amma wannan namijin dasukazo tarefa?”
“Yayan Hanan ne” Nana tabata amsa
Jalila tana jinsu tayi musu banza
NaJa takuma cewa
“Yana da aurene”?
Nana ta dan bude baki, ta kalli Jalila sannan ta kalli Naja
“To ai Jalila zaki tambaya bani ba”
Jalila ta kalli Naja
“Kinada damuwa da hakanne, ina ruwanki ne, Suma daga dangin arnan suke, kinada matsala da hakanne?”
Jalila tayi maganar a fusace, da son huce takaicinta akan Naja, ta mike ta shige toilet
Nana kam dariya takama yi, “to hajiya Naja, kinji dai inma sokike seki hakura”
Bayan sallar magariba Jalila ta kira Abdallah, yace mata sun isa Kaduna lafiya tai masa godiya da bangajiya
Nana ta shigo da katon Leda a hannunta
“Nima bari in Dana Queen inji Hanan”
“Sarkin tsokana,”
“Ba wani tsokana, zomuje kirakani please”
“Ba inda zani”
“Maama ce fa tace kirakani”
“Ina?”
“Gurin mummy”
“Waike kullum sekinje gidansu Ilham ne?
” to queen ya zanyi Maama ce ta aikeni,”
“Ba sunana queen ba,”
“To Baby Jalila, na dena”
“Kyaji dashi dai” Jalila tasaka hijjabi tabi Nana zuwa gidansu Jalal
Suna zuwa suka tarar da mummy tana kuka a palour Ilham kuma tana kan kujera tana chatting,
Ilham tace “mummy lafiya kuwa?”
Ta goge hawaye, “bakomai Nana bari in dakko miki kudin”
Ta karbi kayan hannun Nana ta wuce dakinta
Nana ta kalli Ilham “Ilham me akayiwa mummy take kuka?”
“Ta tsuniyar gizo ai bata wuce koki, ita da danta ne, yamata rashin kunya ya fita”
Nana ta girgiza kai “kai abun ba dadi Allah ya shiryi Yaya Jalal”
Jalila ce kawai tace Ameen yayinda Ilham ta maida kai kan wayarta
Jalila tace “yawwa Ilham nikam Neman me kukemin dazu?”
Ilham ta Dan daga kai ta kalleta
“Manta kawai ya Riga ya wuce”
Daga nan Jalila bata kuma cewa komaiba
Mummy ta fito tabasu kudin ta koma dakinta
Ilham ma ta mike tabasu guri Dan zuwa yanzu ba Jalila ba har Nana ma haushinta takeji.
Suka koma Gida Nana ta tafi kaiwa Maama kudi, Jalila kuma ta shiga dakin Halima
Suketa hirar zuwansu hanan Jalila take gayamata farincikin datayi,
Tace kinsan wani abu Halima
Halima tace “a a”
“Yau abunda yabani mamaki ganin Jalal yana dariya”
“Naganku kunata hotuna kaman bashiba”
“Wallahi kuwa,Allah sarki mahaifiyarsa ce babban abun tausayi, tanada da kamar Jalal da yakamata ace, tana cikin farinciki amma kullum cikin tashin hankali take”
Halima ta kalli Jalila
“Tab wannan matarce abun tausayi, amma bata taba shukamiki rashin mutunciba”?
Jalila ta kalleta da mamaki
“Me kike nufi Halima?”

Share please
More comments more typing………………..

????️????️????️????️????️
[9/12, 6:02 AM] +234 816 830 7871: ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

_ABDUL  JALAL_
       (2020)

  _ STORY & WRITTEN BY AISHAHUMAIRA_
(Daddy's girl)

           PAGE- 41

PART 1
Share please

_Bismillahir Rahmanir Rahim, da sunan Allah me Rahma me jin kai, Allah ka yi salati a bisa shugaban mu Annabi Muhammad (salallahu alaihi wassalam)
Bayan haka, ban rubuta wannan littafi domin cin zarafin wani ko wata ba, na yi shine domin nishadantarwa, da kuma wa’azantarwa, ku biyoni domin jin me wannan labarin ya kunsa.
Yanda nafara Allah yabani ikon kammala shi

Ina maraba da shawarwari, sharhi, ko kuma gyara, nagode.

Domin Samun karanta wannan littafin yi magana ta what’s app akan wannan lambar

07063065680
Kokuma addanna wannan link din domin samun novel din

????https://chat.whatsapp.com/EtB4KI52K0v5FQc2ELhidL

Special thanks to my group members ina Alfahari daku comments dinku na bani karfin gwiwa
ABDUL JALAL NOVEL FANS
Love u all guys ❤❤❤❤❤

      -MY FIRST NOVEL-

Halima ta kalli Jalila sannan tace
“Hmm Jalila kenan abar zancen kawai Allah ya kyauta”
“Amma halima yakamata kigayamin”
“Jalila fadan bashi da amfani, amma kiyi hankali da matar nan”
Daga haka Jalila ta mike ta tafi dakinsu, itakam takasa gane kan wannan al’amari ita dai a haka bataga aibun Mummy, amma meyasa Halima tace bata da kirki, kuma gashi taki gayamata meyasa,
Da wannan tunanin ta shiga toilet tai wanka tai alwala tazo ta tayar da sallar shafa’i da wuturi
Shikam Jalal daya koma part dinsa ji yayi baya kaunar shan madarar Mummy tagama bashi haushi, Dan haka ya kunna sigarinsa ya dinga sha, dayagama kuma ya sha giyarsa iya son ransa, sannan ya baje a gurin
Jeje ne a gaban wannan mutumin na rannan, mutumin ya kalli Jeje fuskarsa Sam babu alamar tausayi sannan yace
“Jeje nagaji fa, a wannan karon na raina kokarinka, har yanzu abu yaki karewa, har yanzu ace kunkasa aikata abunda nakeso”
“Jeje yace haba Oga KB duk kokarin danayi abaya, se wannan zaka kasa hakuri, aiko iya haka muka kyaleshi nayi maka kokari, balle ma ina kokari fa”
“Hakane amma gani nai yanzu kana nema kayi sanya, a wannan shekarun da kunyi tafiyar nan Dubai da dayan biyu ko akama shi saboda miyagun kwayoyin damuka Sa akayansa, ko kuma da kun tsallake da yanzu munyi arziki fiye da yanzu”
“Hakane Oga abun ne da matukar wahala, wannan Jawwad din shiyake hana ayyukan mu tafiya yadda yakamata, Hannah ma tanata nata kokarin amma hankalinsa baya kan mata, yafi ganewa shaye²”
Wanda aka kira Oga KB ya nisa sannan ya kalli Jeje
“Bawata yarinyar da za a iya sakawa aikin dole se Hannah?”
“Oga a matan da nasani na bariki a irin taurin kan Jalal inba, Hannah ba ba wadda zata iya,”
“To shikenan amma ka ninninka kokarinka, gaskiya sonake yaron nan ya lalace fiye da yanzu, sonake yazama kaman Dan akuya sabida bin mata, yasha miyagun kwayoyi yayi safararsu, sonake bakin cikin ABDUL JALAL Yayi sanadiyar rasa ran Hadiza sannan ya kare rayuwarsa a gidan yari”
“Kwantar da hankalinka Oga komai ze tafi yadda kakeso mu dai ka Dan karamana lokaci”
“To shikenan ina jira inji kyakykyawan labari”
“Kar kadamu zakajine Oga, kwanan nan ranar zagayowar haihuwarsa zeyi, zamu shirya masa party, a nan zamuyi kokarin ganin komai ya kasance”
“To shikenan ina saurarenku”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button