NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Amma dai zamu kwana biyu anan kafin ka wuce Abuja?

Dan waiwayowa yayi ya kalleta batareda ya motsaba yayi Mata kallon minti biyu kafin ya maida kallonsa kan tv cikin kamewarsa da Dan sakewar fuska tunda ita din iyalinsace a gajarce yace”

Gobe Zan wuce Abuja da yamma.

Marairaice fuska tayi tana sake shigewa jikinsa tace”

Please Turaki ka qara ko kwana biyu ne kafin zuwa abujan,
Idan muka koma gobe kana zuwa can bazakai lokacin hutawarmu ba.

Ki zauna anan idan nagamo daga Can kafin nakoma zanyi kwana biyu anan bayan tafiyata din saiki koma Abujan.

Ba Dan tasoba tace”

Ok Amma dai zanbika Abujan Kuma idan zaka dawo nasake biyoka.

Kallonta ya Dan Kuma waiwayowa yayi sbd yasan tsoronta akan zuwansa bada itaba baifi akan maganar qarin aure da Anne keson yayiba ko zai samu haihuwa.

Juyar da idanuwa tayi tana kokarin boye yanayin data shiga din Dan kuwa har cikin ranta Bata qaunar kebewar Anne da Turaki tunda tasan zancen dai daya ne na qarin auren.

Wani irin lafiyayyan murmushi ne dayafi komai kasheta yasaki Yana dauke kansa daga kallonta yabarta tana qarasa zubewa ajikinsa Dan kuwa murmushin abune dabai cikayiba Amma yanayi din sosai.

Har qarfe goman dare Yana tareda Ita yabata lokacinsa sosai kafin buqatunta suka biyo baya inda ta wawashi kudi masu matuqar yawa agurinsa Wanda dama ita sune suka riqeta a auren.

Sai daya rabu da Mss Na’ima kafin ya nufi office room dinsa na cikin gidan inda A Abdoul ke jiransa da tarin bayanansa
Yana shigowa kuwa A Abdoul din ya miqe Yana Masa barka da fitowa kafin ya zauna Kan kujerar 1 seater dake facing din A Abdoul ya miqa hannu ya karba iPad din Dake hannun Abdoul din Yana duba bayanan.

Sai dare sosai ya fito ya ta kofar Dake palon qasan ya nufi sama ya Haye
Kai tsaye ya nufi bedroom dinsa.

Washe gari qarfe Tara an kammala komai na breakfast din gidan an jere sai qarfe goma yasauko sanye cikin Ash Kaftan na babban yadin Ambassador sai hular qube
Hannunsa sanye da agogon Chanel
Take qamshinsa ya gauraya palon kallo daya A Abdoul da M Sarat sukai Masa Suka sauke Kai ganin Mrs dinsa a gefensa sai wani Jan girma takeyi cikin nata adon.

Breakfast yayi tareda Ms Na’imah da A Abdoul kafin ya fito zuwa Inda zai gana da baqinsa.

Qarfe biyu yagama da baqinsa yadawo gida yayi lunch tareda Ms Na’imah kafin ya haye Bai fitoba sai qarfe hudu da rabi Ya sauko Kai tsaye suka shige mota zuwa airport dukkaninsu.

A jirgi ma hankalin Na’imah gabaki daya yakasa kwanciya Dan ita harga Allah ma rashin zuwan Turakin yafi Mata kwanciyar hankali akan zuwansa
Dan zuwansa kullum cikin sakata fargaba yake,
Kishinsa take sosai sbd bazaso akaro wadda zata tayata cin wannan dukiyarba.

MAMUH

????????????Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete ????????

Mamuhgee @Arewabooks

????????????????????
KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN

09166221261
[7/10, 9:19 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 12

SAKINA VENDABLES
Ina ma’abota son qamshi da gyara? Ina masoya qamshi dasuka San darajar qamshi da gyara irin na qamshi?
To kuzo ga SAKINA VENDABLES Tasake zuwar muku da ingantattu Kuma tsararrin kayan qamshi masu kyau da qarko,
Ga wainda suke buqatan turarukan gaske masu kyau na asalin qamshi da Kama jiki da Kaya suzo ga inda aka tabbatarda kyau da qarfinsu a gurin SAKINA VENDABLES

Turaren wuta list
Queens special
Kajiji mix
Kajiji whole
Gabgab
Brown Hawiii
Special Halut
Sandal balls
Sandal strips
Sandal flakes
Dubai oud
White Hawii
Classy Dufr
Black bange
Black bange
Musky Dorrot(Na tsuguno)
Cous cous
Khumra White & Black
Kulaccam Black(for hair) white (for body)

Handles Instagram @sakina_vendibles Facebook @Sakina vendible Tiktok @Sakina vendibkes
08106974073


Kamar yanda Haj Anne ta sanar Masa da bayanin komai da Kawu saidu yayi Mata shiru yayi Yana sake juya zancen Dan kuwa Babu wani sauran abinda zai iya fada ayanzu tunda Anne tariga ta karba Auren Amma Kuma duk da hakan zai karba auren ne Dan taqaita maganar,
Zai karba auren Amma badan ya karbeta a matsayin Mataba,
Zai karba auren Dan inganta rayuwarta ta hanyar Bata ilimi Mai kyau da tsadarda zai iya bawa ‘yayan cikinsa da yanada,
Kar karbeta ne tamkar ‘yar riqo har zuwa lokacinda Allah zai bawa Amininsa nasa lafiya saiya sawwaqe Mata ayi Mata auren daya kamaceta,
Wannan shine abinda ya yankewa kansa da maganar auren
Dan kuwa bayajin har abada zai iya kallon ‘yar da Mahmoud da Zainab suka Haifa Amatsayin matarsa,
Macen da zai iya muamala ta daban da ita bayan ta uba da ‘ya.

Da wannan ya rufe maganar aka fara Shirin auren Wanda Babu Bata lokaci aka Sanya sati Mai zagayo ranar juma’a.

Wasu irin kudin gaske Aka aikowa Momy da Kawu saidu na hidimar Wanda yakusa haukata kawunan dangin momyn suka so cinye kudin
Dayake Kawu saidu shima idanuwansa a bude suke yace Babu wannan maganar shima Dole a fitarda na dangin uba abasa idan bahakaba zai fasa bada auren.

Wani irin murmushin bakada lafiya su Haj Karima sukai Masa
Alhaji Atiku kuwa Jin abinda Kawun Yafada yasashi kallonsa da kyau da hasaso irin dukan mutuwar dazasu saka Yan dabansu na shiyasa suyi Masa idan har ya kwatanta abinda Yafada din,
Umma Jamila kuwa cikin ranta fatar saukar masifar datafi ta Dan uwansa Mahmoud tai Masa.

Momy da har lokacin zuciyarta najin wani iri a al’amarin kallonsu tayi jiki a Dan mace ta rokesu akan subawa kawun haqqinsa na matsayin uba ko Dan asamu albarka a wannan auren.

Haka suka bawa Kawun saidu kudin dabai taba riqe irinsuba arayuwarsa hakama takamaimai baisan me zaiyi dasuba kawai dai yafison ya karba din Dan kuwa yagama ganin zallar kwadayin abun duniya da son zuciya a al’amarin dangin Zainab din.
(WAINDA SUKE RUDEWA DA SUNAN ZAINAB DANAKE FADA SHINE DA MOMY DA MAHAIFIYAR LAYLAH DA LAYLAH DUK SUNANSU ZAINAB,ITA LAYLAH SUNAN MAHAIFIYARTA AKA SANYA MATA BAYAN RASUWAR MAHAIFIYAR).

Sabuwar rayuwa Kawu ya bude a garin Dan kuwa tuni yasaka Abdullahi agaba akayo Masa manyan dinkunan bikin tareda huluna masu tsada da takarma harma dasu turaruka Kawun ya siya,
Dayake baida rowa har Abdullahi yabawa nasa kason kudi masu ‘yar tsoka wanda yasa Jikin abdullahi din yakuma sanyi da al’amarin yaji bazai iya boyewaba Dan Haka Ana saura kwana biyu daurin auren da daddare ya nufi gidan umma Jamila Dan ganin Sa’adah wadda ita kadai yasan zata fahimcesa sbd kaf kowa dukiyar tagama rufe idonsa
Shikuma yakasa danne al’amarin sbd sanin Auren Laylah da Turaki Kamar wani boyayyan burine Kuma Alqawarin Abba Wanda duk ranarda ya tashi yaga wannan sauyin bazaiji dadiba duk da itama Sa’adah din ‘yarsa ce Amma kamar sbd mahaifiyar Laylah yakeson Lallai laylance zata aura Turaki.

Babbar Sa’ar dayaci a zuwa gidan umma Jamila Bata Nan suna gurin hidimar bikin da aketayi duk da Turakin yasanar da cewan basason Ayada Dan kada Yan Media suji Amma zancen ya Dan firfita sbd sukam su Alhaji Qarami sunason asan Wanda suka bawa auren yarsu,sunason duniya tasan sun hada alaqa da ABUTURAB TURAKI Ko Dan matsayinsu da girmansu yaqaru a idon jama’a.

Lokacinda Anty Sa’adah taga Abdullahin ne Mai neman ta gabanta Saida yayi mummunan faduwa
Take jikinta yayi Sanyi sbd tasan tabbas kodai abbansu kokuma Laylah akwai Wanda wani Abu yasama.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button