NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Shiru sukai daga ita harshi Dan ko Dan zancen datake Masa wasu lokutan takasa sbd mutuwa da jikinta yayi dakuma damuwar datashiga yanzu din akan yanayin nasa tasan Dole Kam akwai abinda yake damunsa tsakanin jiya zuwa yau din.

Ganin gwara ya kwanta kozai samu baccin yazo Masa yasa ta tashi ta tura kujerarsa har bakin gadonsa da kanta ta mirginasa zuwa Kan gadon ta gyara Masa kansa akan pillow ta rufe Masa Rabin jikinsa sbd akwai sauran sanyi sosai na ruwan saman da aka gama ta bude Masa windows Dan iska da Sanyi na shigo Masa ta fice Takoma dakinta itama ta zauna jigum sbd Haka tata rayuwar take.

Sai qarfe kusan goma Sha daya saura momy da anty Sa’adah suka fito dayake komai takawo musu palon na Kari suka zauna karyawa
Ita Momy tuni tayi wanka kafin ta fito.

Motsinsu yasata aje littafin datake karatu na koyan wasu abubuwan addini da anty Sa’adah tabata ta aje gefe tareda miqewa ta fito.

Bata tsaya ba kicin ta nufa ta dauko maganin data dafawa Momy Kai tsaye ta juyo tadawo palon cikin tsananin girmamawa ta qaraso gabansu ta aje kofin maganin gefen Momy anatse da biyayyarta tace”

Barka da fitowa Momy.
Ga magani andafa na ulcer dinki naga
Kamar zafin jiya ya tada Miki ita.

Batareda ta kalli gefenba ta dago ta kalli Sa’adah dake kallon Laylan cikin tsananin qaunarta kafin ta kalli Momy tasaki murmushi tana sake maida kallonta ga Laylah cikin sakewarta tace”

Laylah kinfi kowa sanin Momy da iya kulawa da ita.

Miqewa laylan tayi tabar gurin ta nufi kofa ta fice tsakar gida tana Kama hanyar kicin Dan Dora abincin Rana Dan kuwa tasani ko shekarun duniya zatai agurin ba tankawa Momy zataiba hakama ire iren wannan son cusata agurin momyn da anty Sa’adah keyi tana iya gani akan fuskar momyn tado Mata da tsananin dacin Dake zuciyarta na shekarune kawai takeyi shiyasa anty Sa’adah na farawa take ficewa Dan dama idan ba aikin doleba Bata tsayuwar data wuce minti biyu agurinda momyn take tunda momyn ta bayyanarda rashin son hakan qarara tuntuni.

Sbd ulcern momyn yau tuwan shinkafa tayi da miyar zogala da Babu Mai sosai,
Da kanta take zuwa bakin titin anguwar karbo kayan cefane gurin malam rabiu Wanda sai anhada kudi Kamar 4 zuwa biyar sai momyn tabiyasa sbd ita kanta duk qarfin haline,
Iyayenta da Yan uwanta nada arziki Mai yawa sbd kusan gidansu duk manyan Yan shiyasa ne,
Hakama yannanta da qannenta Mata duk masu hannu da shuni suke aure saidai kaf kusan danginta Babu Mai iya Taimaka Mata sbd aurenta da Abban da Babu Wanda yaso Dan Yana talaka Mara qarfi,
Ta tsaya tsayin daka ta auresa sbd tana sonsa,
Yanada iliminsa da hankalinsa Dan Haka bataga illar aurensaba Dan bayada kudi,
Mahaifinsu baya Raye sai mahaifiyarsu wadda Sam batawa momyn auren Wanda baida aikin Yi sai takardun karatu,
Yayyunta sunso inganta rayuwarta ta hanyar Bata karatu Mai zurfi tareda auren Hadi na tsakanin masu kudi Amma ta ture komai tace bataso sai Abba Wanda hakan yakawo rarrabewar Kai aka samu hargitsinda kowa yabarta ta aura Wanda takeso Wanda ba jimawa da auren yasamu aiki yafara ta samu kwanciyar hankali da nutsuwarda take tunanin tabbatuwarta har abada,

Mahaifiyarsu ta rasu alokacinda Abba baya gari ga laulayin ciki Haka tashiga damuwa da gagari Mai tsanani Dan kuwa acikin Yan uwanta kasa sakewa tayi ga ciwo,
Qarshe dasuka Bai dawoba Haka Kuma tana buqatar taimako suka kaita asibit saidata share sati uku a kwance kafin aka sallameta ahakan Takoma gidanta taci gaba da rayuwar kadaici da tawakkali sbd zuciyarta idan tanason Abu tana Masa sone mai tsananin gaske.

Saida cikinta ya Isa haihuwa Allah yabawa Abba ikon dawowa daga doguwar tafiyar da yayi ta haifi Sa’adah wadda taci sunan mahaifiyarsu,

Darajar sunan yasa Yan uwanta ke qaunar Sa’adah har suke iya Mata komai Ahankali ahankali harta shirya da Yan uwanta suka ringa Bata kulawa da gata kamar yanda mahaifiyarsu tabar musu wasiyyar kulawa da momyn kamar tasan wani abun zai faru,

Bayan haihuwar Sa’adah Abban tafiye tafiyensa suka tsananta ahaka Sa’adah ta taso ba shaquwa sosai da mahaifinta sbd baya zama,
Duk wani dawainiyar gidan momynce keyi sbd Abban kullum ciki yawon kamfani yake Wanda yake aiki sbd aikin gwamnatin Bai samuba har lokacin.

Momy nasonsa Bata taba Jin damuwa takaici ko gazawa da zamanta ahakan ba saima tausayi da qaunarsa datake qarawa ahakan.

Babban budin daya fara shigowa rayuwarsu shine dawowar babban Amininsa MUHAMMAD ABU TURAB TURAKI Wanda duniya tafi sani da AB TURAKI
Turaki shine ya bawa abba manyan kudin daya bude kamfanin kansa da kansa bayan ya siya Masa babban gida da babbar mota,

Da farko rayuwarsu Momy da yarta da abban Takoma ta kwanciyar hankali da Jin Dadi saigashi kwatsam Abban yaga ZAINAB yaji Yana qaunarta,qauna Mai tsanani batareda jawakai lokaciba ya aureta ya ajeta anata gidan daban tsawon shekara da shekaru har Allah yabata ciki momyn Bata saniba saidai yanada niyar bayan haihuwar ZAINAB din zai hadesu yafadawa momyn gaskia wadda halaccinta da kunyartane tun farko yasakashi boye Mata
Ashe qaddara bazata bar hakan ba Dan kuwa mummunan hadarin motar yafarune ranar da Turaki ya sauka Nigeria akan wata babbar nasarar rayuwa daya qara samu a qasar US
abban ya dauki zainab suka Isa gidan Dan tayasa murna da yiwa hajiyarsa wato Anne Allah ya Sanya alkhairi saigashi suna shiga gidan tsautsayi ya Tarawa zainab din ta zame tayi mummanar faduwa nakudar Dole ta taso mata,
Hankali tashe suka juya zuwa asibiti ganin halinda Abban yake ciki na rudu da rashin hankali yasa Turaki bin bayansu da mota wadda shine da kansa yake tuqawa gashi dare ne Dan Saida sukai ishai sukazo gidan.

Motar abbance tafara shigewa qarqashin babbar motar data Rasa burki tayo cikinsu kafin motar Turaki wanda Bai ankareba Saida yakawo gaf dasu shima tasa motar tayi cikinsu anan wannan mummunan hadarin ya afku Wanda yayi sanadiyar rayuwar zainab duk da ansamu ta haife cikin,
Shikuma Abban ya Rasa nasa qafafun da wasu raunika
Turaki kuwa Babu wani babban raunika ajikinsa saidai buguwa da yayi sosai wadda tayi sanadin tasa qaddarar ta rashin haihuwa da ake fada duk da Babu tabbacin rashin haihuwarne kokuma asalin inda ake samun haihuwarne yasamu matsala Dan kuwa tunda yabar qasar baikuma dawowa ba Saida lokaci Mai tsayi yaja
Zuwansa Nigeria saiya koma sai dace ne kawai duk da Suna da tarin dukiya da matsayinsa Babu inda Bai zagaba a jaridu da gidajen talabijin da media Amma Kam ganinsa sai dace Dan kuwa babban mutum ne da ko acikin masu kudin ba kowa ke samun damar ganinsa ko ganawa dashiba,saidai Amininsa Abba da koyaushe yakan ziyarcesa ya duba lafiyarsa duk yazo Nigeria saidai wannan karon ya Debi shekaru masu Dan dama Bai dawoba.

Bayan abunda ya faru dukkanin arzikin Abba Saida yashige gurin neman lafiyarsa Wanda daga qarshe wannan gidan dasuke ciki shine kawai ya rage musu Wanda aka siya da sauran kudaden kamfaninsa da kadarorinsa da aka siyar,

Dangin momy sunyi fushi da Allah wadai da ita akan zaman datakeyi da Abban har bayan irin abinda yamata gashi yanzu Takoma jinya da dawainiya dashi,
Ta ciyar da kanta,ta ciyar da yarta,ta ciyar dashi da tasa ‘yar hakama itace dawainiyar komai da sutura duk da dai Bata yiwa yarsa sai abinda Sa’adah ta kashe ta bata Haka shima kayansa duk rufin asiri ne Dan Haka kowa danginta ya saka Mata ido suna muamala da ita Amma basa iya taimaka Mata,itama dama ayanda cin amanarsa ta kangarar Mata da zuciya sai Bata buqatar taimako ko tausayi daga kowa,
Zata Gina rayuwar yarta suyi rayuwa Mai kyau da Jin Dadi wannan shine babban burinta sbd a duniya tariga tasan bayan ‘yarta data Haifa da cikinta babu wata qauna ta gaskia da Amana.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button