NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Shigowa tayi dashi palon baqin gidan suka zauna takawo Masa ruwa tana kallonsa jiki mace muryarta na bayyanarda damuwarta tace”

Yaya Abdullahi Allah yasa lfy dai Dan nikam ganinka yasa jikina mutuwa.

Ruwan data kawo Masa ya Dan Sha Yana dauke idanuwansa daga kallonta ganin irin yanda ta sauya sbd zallar gyara da ake mata tayi haske sosai tayi fresh duk da ta rame Amma duk da hakan a idanuwansa ko ahakan batakai Laylah kyawu da haske ba.

Aje ruwan yayi tareda Dan kallonta kadan cikin nutsuwa yace”

Abba dai yananan yanda take hakama Laylah tananan da dama itama saidai Kam duk tayi wani iri sbd kadaici da rashinki ahakan ma dai aikin gidan yadawo kanta,
Saidai ba wannan ne yakawoniba.

Kallonsa Anty Sa’adah din tayi batareda ta iya cewa komaiba tana sauraron abunda zai fada.

Ya fuskanceta dakyau Yana tattaro nutsuwa yace”

Maganar auren Nan ne da za’a daura jibi nazo nafada Miki sbd naso daurewa nayi shiru nakasa hakan sbd Abba da Laylah dama ke din.

Ahankali ya zayyano Mata burin Abba da babban qudurin nasa na Bawa Turaki auren Laylah tareda sanar da ita asalin abindaya faru ranarda ciwon na Abban ya rikice sbd shima Kamar yanda Momy taji komai yaji komai ganin momyn zata juyo tabar gurin yasashi barin gurin tun kafin tagansa ya fice daga gidan
Dan Haka ya Dora da cewa”

Sa’adah ke kadaice gatan Laylah ayanzu tunda Babu Wanda take nuna yasanda ita bare damuwa da rayuwarta,
Kece gatanta ayanzu da Abban yake kwance,
Kece uwa Kuma uba gareta hakama ‘yar uwa,
Idan kikayi auren Nan Kika tafi Amatsayin Laylah da wace daraja Turakin da Mahaifiyarsa zasu kalleki?
Hakama Abban duk ranarda ya tashi da wace darajar zai kalleki da Momy,
Hakama babban abindayake faruwa shine Turaki yasa ahada takardu da komai na lafiyar Abban za’a daukesa daga Nan zuwa wata qasar Kuma ansanar da Momy ta aminta da atafi dashi din Dan Haka bayan aurenki bana tunanin Laylah tanada wani sauran abinda yarage anan bayan kunci.
Nidai abindayasa nazo nafada Miki gaskiyar lamarin sbd kome Zakiyi karki manta da ‘yar uwarki Dan Allah,
Kamar yanda Kika dauko tallafar rayuwar marainiyar Allah kici gaba da tallafa Mata Dan Allah karki Bari ta Shiga wani mummanan halin dayafi Wanda take ciki sbd nidai da antafi da Abba zuwana gidan nasan yaqare tunda dama dawainiyar Abban ke kaini…..

Dogon numfashin data saukene yasashi dakatawa Yana sauke nasa numfashin shima kafin ya kalleta ganin yanayinta ya sanyashi miqewa Yana kallon Agogo
Gwara ya tafi kafin umma Jamila tadawo ta taddasa gidan
Hardai idan tasan abin daya kawosa da Babu shakka saita Ari hauka ta Masa mummunan wulaqanci.

Bayan tafiyar Abdullahi Sa’adah na shiga gida tafara hada kayanta Dan kuwa ta yanke shawarar komawa gida ayau din,
Gwara Takoma gida kawai aqarasa komaima acan.

Koda umma Jamila tadawo agajiye take shiyasa Koda Sa’adah din Tai maganar komawa gida Bata kawo komai arantaba tasa driver yakaita Dan dama gobe za’a maida Sa’adahn gida sbd gobe su Haj Anne zasu iso
Dan Haka Kai tsaye tasa aka maida Sa’adahn gida da maraicen ta bugawa Mai hajiyar dasuka dauko ta musamman Dan gyaran Amarya waya cewa subi Sa’adah din can gida aqarasa acan na yau da goben.

Ko data iso gidan tsit kamar ba hidimar biki akeba Momy na Palo da baqi suna magana tashigo a natse fuskarta daukeda murmushi taqaraso gabansu cikin girmamawa ta gaidasu tana kallon Momy datake kallonta tana yaba kyawun datayi tace”

Momy kinata kallona
Na sauya Miki ne?

Murmushi momyn tayi tana cewa”

Dan sauyi kin sauya Kam kamar ba Sa’adah ba
Wannan hajiya Sa’adah shuwa Arab ce.

Dariya baqin momyn sukayi suna yaba gyaran na Sa’adah dake bayyane afili Dayar tace”

Momy ko Zaki bani numbern me gyaran Nan sbd auren sanah da zaizo qarshen watan Nan Dan Naga ta iya gyaran amare Kam gashi Sa’adah sai wani irin qamshi takeyi Mai Dadi.

AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE 08067558902 itace Mai wannan aikin na gyaran Amare tareda kayan qamshinda ko a anguwa za’a San ankawo Amarya,
Turarukanta na musamman ne Dan kuwa daga Chad suke zuwa ga kayan Mata na gyara masu kyau da inganci
08067558902.

Kai tsaye daki Sa’adah ta wuce inda ta tararda Laylah a dakinta zaune tana ninke kayan wanki datai na tarin tsoffin kayan Sa’adah da aka Bata akace gashinan ta ringa sakawa can gidan idan Sa’adah din taje da ita Dan karta ringa saka tsoffin kayanta dasuka Gama kodewa.

Tana ganin Sa’adah taji wani irin sanyin farin ciki harsaida fuskarta ta bayyanarda hakan
Fararen idanuwanta akan Sa’adah din tabude baki tace”

Anty Sa’adah kindawo tun yau ne?

Qarasowa Sa’adah tayi gabanta fuskarta daukeda murmushi tana kallon kayan da Laylah din ke linkewa tace”

Meyasa zakiyi wankin kayana tunda banananma ba sakawa nayi ba.

Kallon kayan tayi tana qarasa Nade rigar Dake hannunta tace”

Jiya Umma Jamila datazo suka bani itada Momy sunce Dani zakije na ringa sakawa acan.

Shiru tayi tareda sauke Kai tana jiran abinda anty Sa’adah din zatace ko tana buqatarsa kayan nata.

Shiru anty Sa’adah tayi cikin Dan takaicin yanda idanuwansu umma Jamila ke rufewa Akan komai,
Koda zata tafi da ita amatsyinta na wadda zata aura Mai Hali yakamata ace andinka Mata ko kala biyu ne na tufafi Amma shine za’a Bata tsofin Kayan da ita takashe taje dasu.

Wani murmushin takaici da baqin cikine ya kufce Mata,
Ita yanzu sun kore Mai aurenta da qarfi da yaji sbd zasuyi auren yaudara da ita
Gashi yanzu zata tashi a Babu tunda biyu Babu takamata.

Kallon Laylah tayi tace”

Aje kayan bazaki dasuba za’a Baki wainda Zaki ringa sakawa idan munje.

Ba musu ta ajiye kayan tareda dagowa ta zubawa Anty Sa’adah din idanuwa tana kallon sauyawar datai tareda tayata farin cikin auren dazatai din Babu babban farin cikinta irin tafiya da ita dazatayi Dan kuwa ita kanta da kanta tasan kanta yakusa qarasa juyewa sbd wasu abubuwan datakeyi wani lokacin.

Akwai gyaran yamma da ake Mata Dan Haka Koda masu gyaran sukazo Laylah tasaka suyiwa tace”

Kuyiwa qanwata gatanan itama da Dan sauya tunda da ita zani.

Momy dai batace komaiba ta qyale akaiwa laylahn sbd lallaba Sa’adah dasukeyi asamu ayi auren tukuna.

Fes Akaiwa Laylah wata irin dilka da wankan lalle tareda wasu gyaran da fatarta ta amsa atake sbd tanada Hasken fata sosai hakama tafi Sa’adah fata Mai taushi sosai shiyasa gyaran atake yaringa shiga jikinta tayi Dan Shar da ita
Abdullahi daya shigo yayi Ido hudu da Laylan tsinkewa yawunsa yayi Yana dauke Kai zuciyarsa na basa qwarin gwiwa da tabbacin Ana Gama bikin Sa’adah zai bayyanarda kansa a manemin auren Laylah din yasan Kuma zasu basa tunda neman Kai su umma Jamila keyi da ita kokuma ya lallaba Kawu saidu kafin yakoma yabasa aurenta basaima Sa’adah ta tafi da ita dinba Dan zata iya fin qarfinsa idan taje daular gidan Turaki ta samu sauyin rayuwa.

Da daddare duk maganin da aketa faman dirkawa Sa’adah Haka ta tattarosu ta bawa Laylah tasata ta shanye a sunan maganin rashin lafiyartane ba musu laylan ta shanye.

Washe gari da safe bayan angama gyaransu masu gyaran sun tafi umma Jamila tareda Haj Karima suka iso gidan da wasu irin Kaya na Alfarma da aka dinkowa Sa’adah din wasu manyan lace ne dasuka Sha maqudan kudi tareda gyalensa da takarmi aka Bata ta shirya tafito fes a Amarya sai qamshi take zubawa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button