NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Kallon Laylah dake zaune gefe tana kallonta tayi tasaki murmushi jikinta amace tanajin inama aurentane na gaskia da Amana za’ai
Datayi farin ciki sbd ita kanta tanason tayi auren Dan ta tallafa rayuwar Laylah din Amma wannan aurene da ake Shirin ginawa Kan yaudara.

Fitowa tayi riqeda hannun Laylah Dake sanyeda doguwar rigar jallabiya sabuwa Navy blue da Sa’adah din tabata tasaka
Kanta nade cikin gyalen Abayar
Idanuwanta ki kwalli babu
Babu komai akan fuskarta sai asalin zallan kyawunta da Allah yabata duk da Babu wata walwala ko sakewa a fuskar tata Wanda Kuma hakan dabiarta ne tunda ahaka ta taso ba walwalar.

Kallonsu Haj Karima tayi kafin ta tsayarda kallonta Kan Laylah Dake rabe bayan Sa’adah din
Ta bude Baki zatai magana
Umma Jamila ta tareta da cewa”

Karma kiyi wahalar magana barta taje da ita din dan taurin Kan Sa’adah Ni har tsoro yakeban yanda kikasan kafiran farko Haka take da taurin tsiya akan wannan Mai Kama da ‘yar tsanar.

Shiru Haj Karima tayi tareda dauke Kai daga kallon inda suke din ta kalli Momy dake zaune tana kallon su Sa’adah din itama tace”

Gatanan gurin gaida uwar mijinta dasuka iso yau za’a kaita.

Umma Jamila ce ta karba zancen da cewa”

Ga abinci dasu komai can a mota duk ansaka.

Miqewa Haj Karima tayi dayake ita zata kaita suka fito bayan umma Jamila tasake bin jikin Sa’adah din da turarukan (AMARYAR KB GLOBAL ENTERPRISE 08067558902) masu qamshi.

Suna fitowa suka shiga babbar CR-V din Haj Karima driver yajasu zuwa masaukin Anne wadda ta iso aranar tareda jamaarta su biyu.

Wani babban makeken guest house din Turaki dake garin suka dosa
Tun a gate Sa’adah ke kallon koina zuciyarta a sanyaye har aka abarsu suka qarasa harabar gidan sukai parking suka fito.

Kallon Laylah da kanta ke sunkeye cikin sanyi Haj Karima tayi Kai tsaye tana cewa”

Kwaso kayan abincin,
Ki dauko da kyau karki barar kosu hargitse.

To” tace anatse tareda daukan kayan abincin tanabinsu abaya.

Wani babban palon dayake a tsare da komai na irin Rayuwar turawa akai musu iso suka zauna Kan milk and golden Royal set dake palon
Banda Laylah data tsaya da kayan abincin tana jiran afada Mata inda zata aje
Kafin suyi wata magana qamshin turaren Haj Anne yafara iso musu kafin ta fito cikin doguwar jallabiyar kuwait baqa Mai Fadi sosai kanta yane da mayafi Mai Dan girma sosai Wanda yasaka Hasken fatar datake dashi fitowa sosai duk da tsufa da manyanci Amma komai nata a natse yake,
Fuska dauke da Dan murmushi take qarasowa tana kallonsu ta iso ta zauna Kan 2 seater tana amsa gaisuwarsu a mutunce musamman Sa’adah wadda ke zaune gefn Haj Karima din…. Sauka Idanuwanta sukai Kan Laylah Dake tsaye har lokacin daukeda kayan abincin…

Dukkanin hankalinta da idanuwanta zubawa Laylah su tayi sbd ba shakka fuskar Zainab take gani akan fuskar yarinyar,
Babu abinda tabaro na zainab face yanayin jikinsu daya banbanta ita sirirya zainab Kuma ba siririya bace Amma kamanninta da mahaifiyar sunyi nauyi sosai take taji qaunar datakewa Zainab din kafin rasuwarta tadawo Mata sabuwa fil akan Laylah
da mamaki Kan fuskarta Tace”

wannan ‘yar Zainab ce basai nayi tambayaba.

Haj Karima wani juyi tayi tareda Yi kamar batajiba tasake dasa sabuwar gaisuwa da barka da hanya kafin tacewa masu aiki dasuke kawo musu kayan tarba su karba abincin.

Suna karba ta kalli Laylah zatai mgn Anty Sa’adah tariga cikin nutsuwa da cewa”

Laylah kixo ki gaida Mutane.

Sabone data taso cikinsa na idan ba umartarta akai da Abu ba Bata Yi sbd kaucewa laifi da matsala shiyasa Bata qaraso ta gaida Anne ba Saida Sa’adah din tayi magana
Ta qaraso ahankali cikin natsuwa batareda ta kalli Annen ba ta gaidata da muryarta Dake yankewa.

Kasa rike mamakinta Anne Tayi takai tattausan hannuwanta ta kamo hannuwan Laylah cikin tsananin kulawa tace”

Wannan ‘yar Zainab ce ko?

Eh itace” Sa’adah tafada kanta a qasa
Haj Karima kuwa kasa hakuri tayi ta miqe tana cewa”

Bari muje mukai wani sakon sainmu dawo mu dauki Sa’adah din daga baya Idan tagama gaidaki.

Cikin kulawa Anne tace”

Ba damuwa kuje tunda zaku dawo saina sake gaisawa da Laylah ko? Tafada tana kallon Laylan Wanda har lokacin itadai bayan gaisuwa batace komaiba kanta na qasa Wanda yasa Anne fahimtar Kamar Laylan nada matsala ko damuwa sbd sanyinta da rashin kuzarin yayi yawa.

Sa’adah datafi kowa farin cikin tafiyar Haj Karima da Laylah
Tana ganin Haj Karima taja Laylah suntafi sbd karsu bada damar da Anne zata qaunaci Laylah
Shi Turaki basama maganarsa Dan sunsan bazai taba ganin laylan ba saidai idan yaganta wata Rana a gidansa acikin Yan aiki.

Ajiyar zuciya Mai sanyi anty Sa’adah ta sauke tareda Dan dagowa kadan tanason magana Amma tanajin nauyi da fargaba saiga sakon zuwan Kawu saidu ya isowa Anne Ana neman ison shigowa dashi.
Wata irin Ajiyar zuciya anty Sa’adah ta sauke sbd tabbas wannan zuwan nasa wani aike ne daga ubangiji.

MAMUH

????????????Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete ????????

Mamuhgee @Arewabooks

????????????????????
KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN

09166221261
[7/10, 9:19 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 11
Umma Jamila kasa nutsuwa tayi ta ringa addabar Haj Karima Saida suka sako Kawu saidu da Kira Kan Kira ya shiryo ya taho sbd matuqar ba yana garinba Turaki yazo yatafi to fa Babu wata maganar aure bayan sukam tuni suka hau Shirin aure gadan gadan batareda lissafin komaiba ko tunani irin na masu shekaru,

Koda Kawu saidun ya iso daga nijar ya sauka a dakin Abba sosai yashiga mamaki da takaicin ganin halinda Laylah ke ciki sbd shikam kallo daya yayi Mata bayan Sa’adah takawota sun gashesa ya fahimci batada isashiyar lafiya Dan kuwa ko dagowa ta kallesa bataiba kanta a qasa ta gaidasa.

Abinci kawai yaci yayi salloli ya wuce asibiti gurin Dan uwansa yabar gidan
Yana fita kuwa saiga Alhaji Atiku da Umma Jamila sunzo gurinsa Basu tarar dashiba Dole suka koma da niyar dawowa gobe Dan subarsa yau din ya huta.
A asibiti kuwa tunda yayi ido biyu da Dan uwansa take jikinsa yayi Sanyi Dan baiyi zaton Jikin yayi Munin hakanba take qwallar tausayi Dan uwa taciko idanuwansa ya hadiye Yana jinjina Kai Yana sauraron bayanin yanda Abban yaketa fama da jikin duk tsawon lokacin Nan daga Abdullahi…

Shiru Abdullahin yayi yanason sanarda kawun wasiyar Abban na bawa AB TURAKI auren Laylah ko bayan ransa Yana shakkar Shiga zancen sbd sanin maganace Mai girman gaske tunda aure ake magana
Auren Kuma da mutum kamar Turaki,
Shi daza’a basa auren Laylah dinma da wlh Yanaso ya karba.

A asibiti Kawu ya tarewarsa Bai sake komawa gidanba ya zauna jinyar Abban Abdullahi yasamu hutu duk da kullum da daddare saiya leqo asibitin kawowa Kawun abinci duk da Babu wata wata daga gidan umma Jamila ake kawo Masa abincin safe Rana dare Kuma abincin Alfarma lafiyayye Wanda tun Kawun Bai kawo tunanin komai aransaba yafara tunanin akwai dalilin hakan Dan Haka ya zuba musu ido yaringa cin abinda Dan yasan Umma Jamila batada Tausayin bawa Dan uwan Mahmoud ko abunda bataso matuqar ba babban daliline garesuba Mai matuqar mahimmanci.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button