NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Kwantawa tayi tareda neman numbern Laylah wadda yanzu laulayinta yafara yawa ba komai take iya ciba sai fruits datake Sha kaman me,

Ringing wayar taitayi baa dagaba Dole ta hakura ta qyaleta.

Washe gari jirgin safe zasubi Dan Haka tunda safe ta tashi ta shirya Kaya cikin qaramar suitcases guda biyu ta shirya tafito sbd driver na jiranta zai kaita gidansu Haj Karima dagacan zasu dauka su umma Jamila su wuce airport Abba daban zaiyi tafiyarsa ba taredasuba saiya gana sosai da Amininsa duk da kusan kullum tunda suka zo Abujan suna tare.

Anne cikin kulawa Tace Mata ki kula Sa’adah kinji,
Allah yadawo Dake lafiya duk da nasan Zaki kwana biyu sosai acan kafin kidawo.

Rumgume Annen tayi jikinta na sanyi tace”

Zanyi kewarki Anne,
Kuma Inshallah bazan Dade sosaiba Zan dawo.

Murmushi Anne tayi tana cewa”

Ba komai ki zauna da momynki tayi kewan zama Dake idan tagama ganinki da kyau Kya dawo,
Allah ya tsare.

Amin” tace tareda juyawa ta wuce halima na bayanta.

Harta Kai kofa tadawo ahankali ta tsaya gaban Annen cikin sanyi da nutsuwa tace”

Anne,
Anne Laylah ce take daukeda cikin,
Yanzu wata cikin na biyar……

Da wani irin mamaki Annen take kallon Sa’adah,
Wani murmushin manyanci ne ya subuce Mata sai kawai tace”

Ita Laylan?
Har wata biyar Kuma shine take zaune gida daya da Na’ima?

Shiru Sa’adah tayi tana Rasa abin cewa sbd yanzu Kam kowa yasan idan Na’ima Takoma yanzu ba shakka zataga ciki jikin Laylah, saidai rashin sanin mahaifin ciki shine saukin masifar.

Wuce driver na jira karkiyi latti.

Wucewa Sa’adah tayi tabar Anne zaune tareda Shiga mamakin duniya dama jinjina zurfin ciki irin na Laylah,
Tabbas tasan Na’ima zata buga rikici na gaske idan tasamu maganar cikin mijinsu a jikin ‘yar datakewa kallon Yar riqonta…

Tuno lokutan datake waya da Turaki tanajin mace tayi kusan lokuta da dama,
Kenan Laylah ce….

Kasa tunanin komai tayi kawai sbd daga Turakin har Laylan sun tsundumata mamaki harma batasan Mai zatace ba,
Me zata fadawa mutanen data gama tanadin gyaran Amarya agurinsu da sauran shaaninsu…

Abu daya ta yanke a ranta shine dauko Laylah kafin Na’ima Takoma.

*Zaune suke a lafiyayyan palon Turaki Dake cikin gidan
Yana zaune 2seater sanyeda skyblue yadi Mai tsananin taushi daya sake bayyanarda kwarjininsa
Gabaki daya turaren Bois elite ne ke sanyaya palon da qamshin ga sanyin AC daya Gama Kama koina hankalinsu akwance,
hankalinsa na Kan wayarsa yana kallon sakon LAYLAH yashigo na wasu kisses data turo Masa.

Ya Dan dauke Kai Yana Kama kansa cikin basarwa sbd Abban Laylan dasuke tare Yana zaune shima suna magana.

Dan gyara murya kadan yayi sbd neman sarkewar Dake da emojis din datake sake turowa
Yadauki wayar ya kashe gabaki daya sbd zata iya rikitasa ya Rasa meyake fada gaban Mahmoud dayake basarwa sbd karya gano waye.

Cikin nutsuwa Abba ya kalli Turakin bayan yagama kashe wayarsa ya aje gefe da sautin bayyanarda zallar gadiyarsa a natse yace”

Turaki Babu abinda Zan saka maka dashi sai godiya kawai,
Kayiwa Allah,
Kayiwa abota,
Kayiwa zumuncinka da Zainab,
Kakuma yiwa marayin Allah Dan Haka Banda bakin godiya daga Kai har Anne Ina muku fatar samun sakamakon gidan Aljanna.

Cikin basar da zancen ya Dan kalli Abban yana cewa”

Inaga ai mun rufe wannan maganar right¿

Numfashi Abban ya sauke ahankali da Jin nauyin abinda zai fada
Yadai Daure tunda ba boyo tsakaninsu da Aminin nasa ya dago ya kallesa yace”

Sai maganar Laylah…..

Sai alokacin Turakin ya dago a hankali ya kalli Abban Jin sunanta.

Gyara zama Abban yayi Yana cigaba da cewa”

Nasan Bai kamata ba nashiga zancen tunda ikonta a hannunka yake yanzu Amma tunda kamar alfarmace tun farko kayimin ka amince da Aurenta
Yanzuma Ina riqon Alfarmar karka duba tarayyata dakai idan har bakada raayin auren zaka iya sawwake Mata tadawo gida ko ahakan kayi matuqar kokari da taimakawa sosai wlh……..

Tunda yafara hada shimfida da LAYLAH Bai sake kallon cikin idon Mahmoud ba sai yanzu daya dago ya zuba Masa manyan fararen idanuwansa akansa batareda ya bude Baki yace Masa kala ba,

Abban yasan Turaki farin sani,
Babu halinsa da Bai saniba sai Wanda yaqara daga bayan Nan saidai duk da hakan idon da Turakin ya zuba Masa bazai iya cewa na menene ba
Dan Haka ya Dan muskuta Yana gyara zama jiran mgna ta fito daga bakin Turakin Dan Yama kasa qarasa sauran zancensa…

Ahankali Turakin ya dauke ido daga kan Abban Yana saukewa Kan Tv Dake aiki batareda ya iya cewa komaiba,.

Shi kansa Abban shiru yayi sbd yasan maganar na buqatan nazari Dan Haka ya kalli Turakin murya a mace yace”

Inaga gobe Zan wuce Nima A Abdoul yagama min booking ticket da komai…
Tafiyar safe zanyi saidai idan naji daga gareka.

Har lokacin Turaki Bai iya cewa komaiba sai gyada Kai da yayi Ahankali cikin nutsuwa.

A Abdoul ne yatafi maida Abbansu Laylan daga can ya wuce gida shima sbd dare yayi Daman.

Tunda Mahmoud yatafi Yana zaune inda ya barsa qafarsa daya Kan daya idanuwansa sun sauya sosai ya rufesu ahankali ya bude saiga Ms Na’ima tashigo sanyeda doguwar Riga idonta a hargitse sbd kwanakin gabaki daya Bata cikin nutsuwar zuciya.

Zama tayi gefensa cikin kokarin danne baqin cikin dake cin ranta tace”

Turaki gobe Zan wuce Lagos acan jirgin da zanbi zai tashi komawa zanyi,
Ga Laylah anbarota ba kowa nasan tana cikin kadaici….

Batareda ya waiwayo ya kalletaba Kai tsaye a karon farko tsawon shekarun aurensu dazai fara hanata tafita yace”

Ba yanzu Zaki komaba ki zauna anan tukuna.

Da mamaki ta kallesa tana juyowa gabaki daya suka fuskanci juna
Tace”

Nariga nayi komai na tafiya zakace bazanjeba?
Babu ruwanka da dukkanin tafiye tafiyena sai yanzu Kuma,
Kayi hkr sbd nariga na shirya tafiyata Banga zamanda nakeyiba anan nabaro yarinya ita kadai acan Dan Haka Ni tafiya zanyi….

Jajayen idanuwansa dasuka sauya tun kafin shigowarta ya dago ya Mata kallo daya dayasa gabanta faduwa Amma batajin zata yarda ta zauna sbd abinda yake gabanta,

Nafada Babu inda Zaki ki
Idan Kuma Zaki tafin ki tafin Amma Kar qafarki ta Isa kofar gidana….

Miqewa yayi tareda daukan wayarsa yabar gurin.

Cikin masifaffen tashin hankali da tsoro harma da firgici Ms Na’ima tabi bayansa da kallo tana shedar da tsananin bacin Rai data hango cikin idonsa,
Karta Isa kofar gidan fa yace????
Batasan lokacinda ta miqe tana neman zunduma ihuba ta fito tana cewa”

Wlh anshiga tsananina da Turaki andau hanyar rabamu….
Ina Zinat ga bala’i Mai zaman kansa na neman sauka rayuwata
Turaki na fadar karna Isa kofar gidan.

MAMUH

[7/10, 9:37 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 46
Lafiyayyan wadataccen Master Bedroom dinsa suka Isa sai alokacin ya sake hannunta tareda waiwayowa suka fuskanci juna ya kalli cikinta da yayi Mata kyau,
Ya dago da mayun idanuwansa ya kalli fuskarta da ita shi take kallo jiki amace da gajiya..

Murmushi tasaki tana juyawa ta nufi sofa ta zauna tana warware nadin gyalen kanta ta ajiye gefe,
Gashinta dayake a gyale tsaf Yana qamshin hair oils masu tsadar gaske.

Gefenta ya zauna yana riqo hannunta ya shinshina kanta Yana Dan lumshe ido sbd ya tabbatar idan tana kusa da inda yake koinane qamshin da komai nata keyi yasa baya iya Dauke hancinsa da idonsa akanta.

Da kansa ya tayata cire kayan jikinta sbd gajiyan datakeji dakuma yanda take sake sake jiki cikin shagwaban ganinsa,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button