NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Sallamar momyn ce data dawo daga fitar datai tasaka Anty Sa’adah kallon kofa ita Kuma Laylah sauke kanta tayi qasa tana cigaba da wankin sbd sanin fuskartace abinda yafi komai tada zafi da ciwon Dake qunshe cikin ran momyn na shekaru yasa so da dama ita da kanta take dauke kanta da duk inda momyn zata kalleta din.

Kallon abban Dake zaune zugum idanuwansa a rufe yanajinsu sbd ganin yanda rayuwar yaransa biyu takeda banbanci Mai girma.

Direct Palo take neman shigewa Sa’adah tace Mata”

Momy zafi ake sosai fa gashi kin dawo kilama kin gaji.

Matuqar Laylah ko abba na guri bakajin muryarta cikin sakewa ko walwala Dan Haka batareda ta juyoba ta qarasa ciki tana cewa”

Bari nayi sallar la’asar saina fito ai.

Tana shigewa ciki Laylah ta tsame hannuwanta daga ruwan wankin ta dauraye tareda gogewa ta miqe taje ta dauko babbar daddumar da momyn ke zama akai ta dawo ta Kama kujeran abbanta ta matsar dashi gefe kusada ita sosai kafin ta shimfidawa momyn daddumar ta dauko Mata ruwa da abincinta duk ta aje Mata akai kafin ta koma ta juyarda kayan wankinta dayan gefen tana fuskantar abbanta sbd bawa momyn baya kamar yanda yake tun yarinta.

Wankinta taci gaba dayi har lokacin Sa’adah na janta da labari Amma tunda momy ta fito tayi tsit bayan motsin wankinta Babu abinda ke tashi sai qarar cokalinda momyn kecin abinci
Sa’adah ma datasan Laylah bazata Kuma maganaba Kuma saitayi shiru tamaida firarta gurin momyn.

Kusa rayuwar gidan gabaki dayansu Sa’adah ce kawai wadda Allah yabawa ikon gudanar da rayuwarta cikin walwala da sakewa tareda wadataccen kwanciyar hankali da nutsuwa harma da farin ciki sbd Sam bata dauka komai tasakawa rantaba,
Abban nema so da dama batada shaquwa dashi Sam Sam sbd farko datana yarinya abunda yafaru yaso cusa Mata tsanar mahaifin nata Amma Kuma qaunarta da ‘yar uwarta da batada kowa saishi dakuma yanda shima Bai boye qaunar Laylah din ba ko a idanuwansa yasa takasa riqe komai aranta saima Suka dawo tausayinsu yayi rinjaye akan Jin zafin cin amanar da yayiwa momynta da mahaifiyar Laylah din Dan Haka tana qaunarsa saidai ba wani shaquwa a tsakaninsu musamman dayake Mata kallon wadda sbd itane mahaifiyarta take taimakonsu take riqe dasu duk da hakan ta wani bangaren itama Yana farin ciki da ingantacciyar rayuwar farin ciki da kwanciyar hankalin datake.

Sai gab da magriba tagama wankin lokacin tuni Momy tayi baquwa suka shige ciki Dan hakama wankin nata yayi sauri cikin tayita tashi kaiwa baquwar momyn ruwa da abinci.

Jin anfara Kiran sallar magriba yasa ta aje shanyar datake ta goge hannuwanta dasukai sanyi ta nufi gurin Abban da idanuwansa suke zuru dan dama hakan suke rayuwar kullum.

Maidasa ciki tayi tasaki labulai sbd sauro tana kokarin fitowa saiga abdullahi yashigo tace”

Anyi sallah Yaya abdullahi shima Abban sai yayi.

Eh dama shine nashigo Dan dubawa.

Ficewa tayi shikuma ya qarasa ciki yaja Abban zuwa toilet din dake dakinsa Dan Koda Abban na buqatan toilet.

Har aka gama sallah Bata Gama shanyarba Saida aka sallame tagama ta tattara gurin ta share ta tsaftacesa ta watsa ruwa tayo tata alwalar ta nufi ciki ta wuce dakinta direct tasaka wata baqar jallabiya ta tada sallah.

Bayan tagama sallar dakin Anty Sa’adah taje ta dauka Qur’an ta nufi palon abbansu ta zauna gefensa tafara karatun al qur’an din cikin zuciyarta har akai sallar ishai anan palon tayi sallah bayan tagama taga alamar shima sallar yakeyi Dan Haka Kai tsaye ta nufa abincinsa ta zubo ta tareda zuba Masa ruwa a wani kofin ta daukosu tareda magani tadawo gabansa.

Tana Gama basa komai ta gyara Masa koina abdullahi yazo ya daukesa daga kan kujera ya maidasa Kan gadonsa Tai Masa addua ta fice shima abdullahin tare suka fito taja Masa kofa.
gurin Anty Sa’adah ta nufa Dan karatun dare datake koya Mata na littafan addini.

Acan takai kusan karfe goma na dare suna karatun kafin ta harhadawa anty Sa’adah dakin ta gyara Mata shimfidar gadonta dasuka zauna Baki taje ta dauko Mata ruwan dare datake yawan tashi Sha ta aje Mata kafin ta fito taje ta rufe gidan da koina ta nufi nata dakin tayi Shirin kwanciya tayi addua ta kwanta.

????????????Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete ????????

Mamuhgee @Arewabooks

Rabo sai Mai shi…Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!
Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon ‘da amatsayin nata mijin?
Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?
NOOR ALBI Hasken rayuwata
Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne
Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi
NoorAlbi#MAMUH

Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates

KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN

09166221261
[7/10, 9:09 PM] +234 704 076 8969: NOOR ALBI
Mamuhgee

2
Ajiyar zuciya anty Sa’adah ta sauke lokacinda taga laylan na aje plate din gefe daya alamar ta koshi
Ta dauki ruwan dake da sanyi sosai
Saikuma ta maida ta aje Dan batashan ruwa Mai sanyi sosai sbd lafiyarta na daya daga cikin abubuwan datake kiyayewa badan kantaba sai Dan kula da Abban da gidan gabaki daya Dan kuwa idan ta kwanta ciwo komai cak yake tsayawa a gidan duk da ba wani babban gida bane ko gidan taro su kadaine agidan Wanda yakeda iya nasa girman na masu rufin asiri.

Miqewa tsaye tayi batareda ta kalli Anty Sa’adah ba ta nufi kofa daukeda plate din da ruwan cikin sanyi tana cewa”

Zanje nafara aikin abincin Rana
Lokaci yafara ja.

Ficewa tayi tabar Anty Sa’adah na bin bayanta da kallon Kamar koyaushe cikin jin qauna irin ta jini dakuma tsantsar burgewa da laylan ke Bata akoda yaushe Dan kuwa Babu abinda Layla ta baro mahaifiyarta tun daga kalar fatar,da jikin,da tafiyar dama sanyi da nutsuwa Wanda hakan kesa Koda mugun kallo Momy Bata kaunar kallon fuskarta sai da dalili Wanda kallo daya take Mata ta dauke Kai,
Ita kanta anty Sa’adah so daya taga fuskar mahaifiyar Laylah
Shine lokacinda sukaje asibiti tareda momyn da aka Kira cewan Abban yasamu hadari aka kaisu har gadon mahaifiyar Laylah alokacinda ta haifeta,
Kallon mintuna masu tsayi Momy tayiwa ZAINAB da jaririyarta kafin suka juya suka fice Bata sake ganin fuskarba har yau saidai Akan fuskar Laylah.

Wayarta ta dauko ta Danna Kiran umma Jamila yayar Momy Wanda ke ji da Sa’adah din itama Kamar itace ta haifeta sbd ita Bata taba haihuwaba.

Dan madaidaicin kicin dinsu ta Isa ta ajiye plate din hannunta tareda Dora ruwan data dawo dasu akan fridge su huce kafin tasha
Ta tattara kayan da akai amfani dasu tafara wankewa cikin Dan sauri sbd lokaci yaja Mata sosai.
Tana gamawa ta goge kayan ta saka a kwando ta dauko tukunya ta kunna lafiyayyan risho dinsu babba ta Dora abincin Rana ta fito ta nufi palon gidan Wanda yake daukeda dakin Momy a gefe saina anty Sa’adah a gefensa sai nata daga can gurin hanyar fitowa palon.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button