NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Duk wasu manyan malamai da bokaye sungama shirinsu akan yanda zasu Dora Sa’adah a zuciyar Anne dashi kansa Turakin Dan samun abinda sukeso shiyasa batason zuwa Inda suken gashi yanzu Dole zata sbd ranar data dawo daga last tafiyar datai Suka hade airport da Haj Karima Dole ta sanar cewan dawowarta kenan yanzu tana Nigeria ta dawo shiyasa suka takura tazo wannan bikin da za’ai.

Motarta ta bude tasaka siyayyar datai bayan motar ta zagayo zata shiga…..

Haj Karima data Gama abinda take itama acikin gurin tana cikin motarta tana waya da Ms Na’ima da shigarta gida kenan ta koma Laylah dake fama da zazzabi Mai qarfi ta fito tana Mata sannu da dawowa….

Haj Karima ta zubawa Sa’adah Ido tana kallonta da kyau Dan ta tabbatarda ita din ce
Cikin tsananin tsana da baqin cikin ganin Sa’adahn tace”

Na’ima ga matsiyaciyar kishiyarki Nan gabana Kamar na taketa da mota…

Dakatawa Ms Na’ima tayi daga tafiyar datake zuwa daki ta miqawa Laylah handbag dinta zuciyarta na tsananin Kuna da zafi sbd da baqin cikin Turaki tadawo khairat Chiroma ta sanar Mata tagansa last month a LA da mace Kuma yarinyace,
Ayanda tace tagansu tamkar Mata da miji sbd yanda yake riqe da hannunta….
Sai data Bata rantsuwa ta tabbar Mata da abinda ta fadan shiyasa ba shiri ta baro yau din tadawo Dan kuwa saita Gane ko wacece Koda komai nata zai qare,
Tafasar da zuciyarta keyi yasa a qule tace”

Kibi kanta da mota Zinat narage masifar Dake gabana akan Turaki,
Kibi kanta da motar yanzu Nan nafada Miki Zinat Dan wlh zuciyata balbalin wuta takemun.

Tana daf da shigewa motarta Haj Zinat ta bawa motarta wuta tayi kanta da motar take kuwa Sa’adahn tayi sama ta Fado gurin ya dauki ihu da salatin jama’a akayo gurin..

Securities ne Suka taso da sauri duk Suka nufo gurin
Sai alokacin Haj Zinat ta fahimci zata iya samun matsala Dan Haka ta sauya shawara ta bude motarta ta fito da sauri ta nufi Sa’adahn tana cewa”

Innalillahi wainna ilaihirrajiun,
Ban luraba wlh,
Na Shiga uku,
Please ku taimaka min nakaita asibiti
Innalillahi….

Kama Sa’adah akai aka Sanya motar Haj Zinat tareda Mai aikin Haj Zinat din tunda tace ta santa sai securities guda biyu dasuka ja motar Sa’adah din itama Suka tafi..

Wani private hospital takaita aka karba Sa’adah din wadda taji rauni sosai take fidda jini akai ciki da ita.

Sun Jima agurin kafin aka gama dressing ciwukan Sa’adah da sauran Taimakon da aka Bata aka kaita wani lafiyayyan dakin hutawa.

Tsinuwar da Haj Zinat ta ringa sheqawa Sa’adah batada adadi Ms Na’ima kuwa acan gida daga hankalinta tayi tana Kira tana tambayar ko Sa’adahn ta mutu Dan buqatan ace ta mutu kawai takeyi.

Handbag din Sa’adah da Mai aikinta ta miqo Mata ta kalla Mai aikin cikin tsananin girmamawa tace”

Ma’am anata Kiran wayarta acikin jakarnan tun dazu.

Kallon wulaqanci Haj Zinat tayiwa jakar tareda cewa”

Bude ki dauka wayar ki sanar idan gidane suzo asibitin Dan Ni tafiyata zanyi Allah yasa kafin suzo tagama Isa lahira.

Bude jakar nafisa Mai aikin tayi ta zura hannu ciki tana neman wayar cikin jakar Amma tayi qasa
Dan Haka saita fara Ciro takardar Dake sama ta riqe hannunta daya ta maida hannu zata dauko wayar idon Haj Zinat ya sauka Kan takardar hannun nafisar da sunan asibitin data sani a LA ke rubuce barobaro.

Hannu takai ta karbi takardar tareda budewa Kai tsaye idonta Bai fara sauka koina ba sai Kan 7weeks pregnancy.

Zare Ido tayi hannuwanta na rawa
A gigice takai idonta Kan date tagani….

Qafafunta wannan karon suka dauki rawa da sauri ta kalli sunan Wanda yake da cikin taga MRS AB TURAKI kawai aka saka kenan matar Turakin ce Mai ciki ita Sa’adahn harna sati 7,kenan yanzu yakai wata hudu cikin…

MAMUH

[7/10, 9:36 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 37
Wunin ranar cikin sanyi tayisa zazzabin ma tuni ya gudu sbd kunyar anty Sa’adah dake dawainiya da ita musamman da Abban yakirata tana zaune tareda Anty Sa’adahn sai kame kame take tana amsa Masa a Dan gajarce duk da irin maganganun dayake Fado mata.

Asibiti ma dasukaje kasa sakewa tayi tana ganin Kamar abbanta da Momy zasu gane Dan Haka duk tabi ta takura
Daqyar Suka Gama kwanakinsu anty Sa’adah ta karbe duka takardun asibitin dasukaje na sakamakon cikin da harsu scanning dasukai sbd kada tsautsayi yasa wani ganinsu a hannun Laylan,

Anty Sa’adahn tafara wucewa tanajin kamar ta tafi da Laylan tayi rainon cikin agabanta Dan har cikin ranta take Jin rashin nutsuwar barin Laylan a tareda Ms Na’ima sbd tana ganin irin girman qiayyar da Ms Na’ima ke Mata sbd kallon datake Mata a matsayin kishiyarta,
kadan take jira tasamu sanadin illarta rayuqarta,
To bare idan daga sama kawai tasamu cikin mijinta jikin ‘yar datakewa kallon ‘yar data Haifa, take raino agabanta,
Ba labarin aure ba komai tafara Jin ciki…. Tabbas komai zata iya aikatawa Dan kuwa ta wani bangaren an Mata saukar masifaffiyar bazata ta inda Bata tsammani.,

Dan Haka idan Takoma taji Bata nutsuba zata sanarda Anne Dan gwara kunyar da Laylan zatai akan wani abun ya sameta suna ganin sunfara samun lafiyar abbansu zuciyarsa bugawa zatai wani Abu yasamu Laylah.

Bayan tafiyar Anty Sa’adah itama jirgin dare tabi Takoma Atlanta bayan ta nawa kanta qwarin gwiwa ta tattaro karfinta da nutsuwarta Takoma yanda take Dan kada ta taba bada Daman ganin sauyi atareda ita har shi Abban Dan Yana gano da ciki jikinta tabbas bazaiyiwa kowa boyoba asirinsu tonuwa zaiyi,
Gashi kunya da tausayin mum Na’ima takeyi sbd tamkar taci Amanarta ne.

Tana sauka A Abdoul ne yazo daukanta yaja suitcase dinta har mota tana Shiga motar qamshin Bois elite daya cika motar ga sanyin AC ya shiga hancinya ta waiwayo da Dan sauri ta kallesa Yana zaune cikin navy blue Ralph Lauren suit dasukai masifar yimasa kyau sbd ta Jima Bata gansa acikin suit ba,
Da alama kodai yayi dare sosai daga office kokuma yayi taron aiki da baqi a office din.

Rufe motar A Abdoul yayi tareda shigowa ya tada motar yaja Suka wuce sbd dukkaninsu harshi din baby Wanda baya tareda gajiya Dan Suma yau din baqi yan china sukai shiyasa sukai dare a office.

Ahankali ya Kai hannu ya kamo nata ya matse cikin nasa da sauti Mai taushi Mara hayaniya yace”

Welcome.

Kallonsa tayi Jin yanda yayi Mata sannu da dawowan sai taji jikinta ya sake sanyi da gajiya ta matso ta shige jikinsa ta kwanta tana cewa”

Sannu da gajiyan aiki.

Lumshe fararen idanuwansa Dake sake bayyanarda gajiyarsa yayi har suka Isa gida har ciki A Abdoul ya shigo Mata da akwatinta Cindy dake murnar dawowarta ta karba sukai ciki.

Sama ya wuce itakuma ta wuce dakinta,
Cindy ta janyo akwatinta ta bude tana cire kayan ciki Dan maidawa closet ta jera ta cire masu dauda ta fita dasu itakuma wanka ta fada tayo jikinta ya sake da gajiya tana fitowa tasaka Riga da wando na bacci masu kauri da hula tayi sallar ishai dan ita kadaice batai ba.
Dukda tanajin gajiya Amma batajin nutsuwar barinsa ya kwana ahaka tunda tasan haryanzu Mum Bata dawoba Dan Haka ta nufi kitchen ta dafa Masa green tea ta Dan gasa sliced hudu na bread ta Madara Mai zafi daya Dan fara Sha yanzu sbd kwanakin Nan dasukai tare.

Samansa ta hau takai Masa har bedroom dinsa Kamar tasan Yana buqatan Dan har yayi wanka Yana zaune Yana kashe wayoyinsa zai kwanta.
Kallonta yayi da shanyayun idanuwansa harta qaraso da kayan jere ta aje Kan table din gabansa ta fara miqa Masa madaran ya shanye a hankali da qaramin sauti ya furta”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button