NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

MAMUH

????????????Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete ????????

Mamuhgee @Arewabooks

Rabo sai Mai shi…Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!
Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon ‘da amatsayin nata mijin?
Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?
NOOR ALBI Hasken rayuwata
Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne
Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi
NoorAlbi#MAMUH

Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates

KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN

09166221261
[7/10, 9:15 PM] +234 704 076 8969: NOOR ALBI
Mamuhgee

https://arewabooks.com/book?id=628264fab77ff582983da456

5
Last Free Page
Guraren la’asar Rana ta Dan bude kadan daga hadari da ruwan da aka tashi dasu
Tana ganin ranar ta Dan bullo ta kwaso kayan wankin jiyan datai Wanda iska ya lalata tasake wankewa sama sama ta shanya
Tana gamawa ta sakarwa abbanta labulan palonsa sbd magriba datai danma yau Bata fito dashiba Shan iska tsakar gida kamar yanda tasaba kullum take fitowa dashi yasha iskan yamma sai magriba ta turasa ciki
To yau sanyi sanyin ruwan da akai yahanata fitowa dashi Dan ita kanta dannewa tayi Amma zazzabin dukan ruwan datashane yake cinta sosai Amma ba amfanin kwantawar Dan haka ta danne sai idanuwanta ne dasuka ja
Sai Wanda yakeda zurfin ganewane zai gane zazzabi ne ajikinta.

Alwala tayi bayan tasake share tsakar gidan tas ta shigarda komai kicin tarufe kicin din Dan dama abinci daya sukeyi har dare basa abinci biyu matuqar ba baqi Momy tayiba aka cinye abincin Amma abinci daya akeyi har dare sbd lallabawa da neman da take.

Dakinta ta Isa ta tayarda sallah cikin dauriya tayi sallar tazauna tana adhkar har tsawon lokaci saidataji zazzabin na neman fin qarfinta ta miqe batareda ta cire hijabin sallartaba ta nufa kofa tafice zuwa gurin Abba Dan bashi abincinsa da magani kafin ta kwanta jikin ya hanata tashi.

Cikin qarfin hali tagama bawa Abban abinci tabasa magani ta maida kayan kafin tadawo ta zauna tana goge Masa fuska sai alokacin Abban yaji tsananin zafin hannuwanta da har wani siracin zafi sukeyi
Ya zuba Mata idanuwansa kafin ya Dan motsa hannunsa alamar mgn
Ta kallesa tana kawarda abunda ta fahimci yaji Wato zafin jikinta.

Cigaba da gage Masa fuska tayi tana qin Bari ya kalla idanuwanta dasukai laushi
Tana gamawa ta miqe tana Masa addua Tai Masa Saida safe ta fito takoma daki Kai tsaye Tai sallar ishai ta kwanata take baccin wahala ya dauketa a gefen katifarta ko rufar arzki bataiba.

Washe gari sbd zazzabin data dauka zai sauka kafin safiyar yasa tayi lattin tashi jikinta a matuqar zafafe da zafi Amma hakanan ta tashi taje tayo alwala tazo tayi sallah
Tana gamawa ta miqe ta fice Dan ayyukanta data Saba dasuke gabanta.

Kunun abbanta tafara damawa kafin ta soya doya tadafa ruwan Lipton ta juye a qaramin flask ta Kai Palo tadawo ta dauki na abbanta takai masa.

Cikin dauriya tayi aikin gyaran koina ta zauna tana bawa Abban abinci,
Daga fuskarsa Yana iya Jin hucin zafin jikinta dake hurowa
Take jikinsa yayi matuqar sanyi zuciyarsa ta narke da tausayin kansu dagashi har itan
Ya zuba Mata idonuwansa dasuka sauya Yana danne hawayen Dake kokarin gangaro Masa Dan karya qara Mata damuwa akan wannan halin datake cikin.

Tana Gama basa ta gyarasa ta fice zuwa gyaran palon Momy da dakunansu,

Daqyar tagama gyaran ta dauki kasko ta fita tasamo garwashi maqota tadawo ta zuba turaren wutar kadan ta aje palon Saida ya Kama koina har dakunansu kafin ta dauka takaiwa abbanta shima ya samu tadawo da kaskon tsakar gida ta aje.

Kicin taje ta zaunda Kan kujera ta janyo abincinta tafara ci taji Bata iyacin ta dauki Kofi taje ta debo kunun babanta kadan ta zauna acan tasaka kanta Sha Dole sbd Kar ciwon yafi qarfin hakan.

Tana gamawa cikin magunan abbanta ta dudduba tasamo paracetamol Wanda Yaya abdullahi ke ajewa Dan kansa shima ta balla biyu Tasha ta fito Abban na binta da kallo zuciyarsa na sake shiga hali na damuwa.

Shanyar Momy ta kashe tayi ciki dasu ta aje gefen kujera ta zauna qasa Dan tana lumshe fararen idanuwanta dasukai duhu ga jiri datake Dan gani.

Mintuna biyar ta dauka zaune agurin kafin ta miqe ta Kashi kayan ta dauko dutsan guga daga dakin anty Sa’adah tayi palon Abba sbd acan take guga Dan palon Momy tanada center carpet bayan tayils din dake qasan batason a Kona Mata carpet shikuma palon abban tayils dinne kawai Dan Haka acan take gugar duk zafi kuwa ahaka take gugar ita zufa Abban zufa.

Qatuwar daddumar baqin Abban ta shimfida tazauna akai tafara gugar.

Har Saida Suka tashi daga barci suka fito gurin Sha daya kafin tagama gugar ta kwaso ta fito suna Palo zaune Momy tagama cin abinci tana waya da umma Jamila hamshaqiyar yayarta Mai abun duniya Kamar yanda take fada.

Anty Sa’adah dake Shan ruwan Lipton har lokacin tafara kalla cikin kulawa tace”

Anty Sa’adah antashi lfy?

Lfy kalau Laylah,
Gama abunda kike wani guri Zaki rakani
Yau umma Jamila nanan zuwa inason binta daga can yafimun kusa da hanyar makaranta sbd exams din zamu fara kinsanni da yawan bacci anan duk exam sainayi latti.

Ahankali ta gyada Kai tana sakewa anty Sa’adahn murmushi tace”

Allah yabaki sa’a Anty Sa’adah.

Satar kallon gefen Momy tayi kafin ta qarasa kadan gefenta cikin nutsuwa da girmamawa tace”

Barka da fitowa Momy.

Hannu kawai momyn ta iya amsa Mata dashi kafin tasaki murmushi ta juya ta shige dakin momyn da kayan gugar
tana shiga ta ajiye Kan gado ta bude Yar qaramar wardrobe din momyn ta jere Mata kayan tas ta cire na Anty Sa’adah ta aje gefe tafara gyaran gadon da momyn ta tashi
tana gamawa ta nufi toilet din dakin shima ta wanke kafin ta dauki kayan Anty Sa’adah din tafito dasu takai Mata nata dakin.

Ganin alamar yau momyn Bata fita yasa ta nufi dakinta takoma ta Dan kwanta Dan kanta Kamar zai tsage ga zazzabi.

Baccin wahalane ya dauketa har batasan yayi nisa ba Saida taji Ana tasata da qarfi
Bude idanuwanta tayi tana kallon anty Sa’adah dake tsaye kanta shirye cikin Riga da skirt na embellished atampa dark brown da gyale Sai qamshi takeyi abunta tace”

Laylah maza tashi muje
Yi sauri na tare Mana Mai napep a kofar gida yanzu zamu dawo ba jimawa.

Tashi Laylan tayi tana miqewa tsaye tace”

Bari na fadawa Momy to.

Aa muje kawai tasani.

Jan hannun laylan tayi suka fito dama da Dan hijabinta a jikinta
Sam anty Sa’adah Bata wani damu data bari ta Dan gyaggyaraba kafin fitar itadai tunda ba tube Laylan takeba bata damuba.

Suna fitowa palon Momy na zaune har lokacin tanata wayoyinta anty Sa’adah tajata suka fice har lokacin Bata saki hannuntaba.

Napep suka Shiga Saida suka hau titi ta kalli Sa’adah din tace”

Anty Sa’adah Ina zamuje ne?

Dariya anty Sa’adah tayi tana Ciro wayarta daga handbag dinta da ake Kira taga Kiran Nasir ne Mai nemanta taqi dauka ta maida wayar jakar tana cewa”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button