NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Da wannan Ya tafi yabar Sa’adah din wadda Anne keyiwa nasiha cikin hikima da tambayayi akan Laylah datake iya amsa wasu
Wasu Kam bazata iya amsawa sbd basuda dadin saurare Kuma hakan tamkar zubarda mutuncin mahaifiyarta ne zatai.

Anne da kanta da Yan bayanin data samu daga Sa’adah din tasake fahimtar rayuwarda Laylah ta taso aciki Dan Haka ta yanke shawarar hadawa har Laylah din ta riqesu da Sa’adah bazatai saurin sakata a rayuwar aureba sai Laylan tadawo kamar kowane ‘da mai walwala da rayuwar yanci,
Bama za’a nuna Mata tanada aurenba a yanzu tana buqatar Abubuwan sauyin rayuwa harma da ilimi duk bayan tadawo cikakkiyar lafiyayyarta kenan idan depression yabarta Dan Haka zata barta Akan riqo ta daukosu kokuma akan biyo Sa’adah datai gidan Aurenta.

Tafiyar Kawu ba jimawa Haj Karima tadawo tareda Laylah dake bayanta kamar Mara lafiya tana tafiya a sulale
Kallon qauna Mai girma Anne ke Mata tana Jero adduar samun tsaftatacciyar zuria daga gareta.

Kasa boye kulawarta tayi tasa aka dauko kyauta ta musamman na kayan Alfarma da aka dinko masu tsadar gske da sunan Amaryar Turakin tabawa Laylah tace”

Gashinan kema gobe ranar daurin auren kiyi ado.

Saida takalli anty Sa’adah kafin tasaka hannu biyu ta karba tana godiya kanta aqasa.

A hanya ba kalar fada da masifar zuwa da ita da Sa’adah tasa sukai Wanda Haj Karima din bataiba kamar ta rufe laylan da duka duk da yau Sa’adah dinma tafi qular da ita Haka suka koma gida masu gyaranta na jiranta ayi za’ai Mata qunshi.

umma Jamila taso karbar kayan ta sauyawa Laylah da wasu Momy ta Hana da cewan Kar ayi abunda zai zubarda mutuncin ko wani kallon daban daga Anne.
Hakan yasa ta hakura ta barwa laylan Amma Kam mugun kallo Babu kalar Wanda ba’a bita dashiba ta sulale tashige daki ta zaunawarta anata hidima da hayaniya sbd gidan acike yake tap da dankin Momy anata bidiri cikinma an hanasu bikin komai da Allah kadai yasan irin shagalin dazasuyi.

Qunshi akaiwa Sa’adah sai bayan magriba aka kammala tasamu ta wanke tayi wanka tayi sallah har lokacin Laylah na daki Bata fitoba dan yau fitowa daki tafi qarfinta a gidan sbd dangin Momy duk Babu Wanda yake qaunar ganin ko giftawarta.

Duk yanda taso janta da zance akan ta sake kasa sakewa Laylah tayi dan itadai matuqar dangin momyn na gidan batada sauran nutsuwa ko sukuni.

Haka Sa’adah ta qyaleta har lokacin kwanciya yayi Laylan tayi bacci tabar Sa’adah na binta da kallon gobe Kamar wannan lokacin ra igiyoyin Turaki uku cif na Aure akan Laylahn,
Wannan shine babbar nasara sbd batada masaniya,
Lokacinda zatasan da aurensa akanta kilama lokaci yaja lokacin zatafi Jin zancen auren Al’amari Mai girma.

MAMUH

Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates

KUFAN WUTA
Safiyya Huguma

BAQAR INUWA
Billyn Abdul

RAYUWAR MACE
Hafsat Rano

MASARAUTA
Miss Xoxo

NOOR ALBI
Mamuhgee

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya????????

09032345899

KATIN MTN

09166221261
[7/10, 9:22 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 14
Washe gari gidan da wata irin hidima aka tashi Duk da kusan fiyeda Rabin hidimar a gidan umma Jamila ake yinta Dan ba qaramin Jin auren Nan takeyiba cikin tsakiyar ranta sbd dukkanin burikanta da mafarkantane zasu cika
Duk arzikin dasuke dashi batajin kammaluwar zuciya Kamar yanda take Shirin jinta daga lokacinda ta zama sirika ga AB TURAKI Dan Kamar itace uwa ga momyn kanta bare Sa’adah Dan Haka Bata dauki wannan auren da wasaba ko kadan
Danma anrage musu armashin komai dasu Anne suka nema aure a sirrance kawai batareda anyi hayaniyaba da Allah kadai yasan irin shiri da dukiyar dasuka so bajewa su zubar dan sunsan wannan yanzu ba matsala bane tunda sunsan inda ‘yarsu zataje.

Tunda safe Aka fito da Sa’adah tsakar gidan aka Kuma darje koina jikinta da lalle tareda wasu ruwan qamshi kafin aka Bata ruwa tashiga wanka a toilet din dakinta tana fitowa tasaka Laylah tashiga tayo wanka da sauran ruwan lallen.

Koda qarfe goma ta safiya tayi angama shirya Sa’adah din cikin Alfarma ta manyan kayan mutunci dasukaji asalin dukiya Wanda Anne ce ta Aiko dasu da safiyar tace abawa Sa’adah din tasaka
Dan haka taci adonta tana daukan ido tamkar a ace aurentane za’a daura
Ga mamakinsu Umma Jamila da farin cikinsu ba kamar yanda sukaga tana walwala da farin ciki dauke a fuskarta hakan na musu nunin auren dai ta karba hannu bibbiyu itama Dan Haka suka sake sakin jiki Ana hidima.

Momy kuwa sai bin “yarta take da kallo cikin farin ciki tana qarawa
Fuskarta daukeda murmushi Dan tama kasa gane irin kewar ‘yarta da zatai idan ta tafi itama gashi gobe da ita din za’a tafi da Abban qasar Germany.

Kamar yanda ake cewa Rabo sai mai shi hakama Matar mutum kabarinsa
Andaura Auren MUHAMMAD ABUTURAB TURAKI da ZAINAB MAHMOUD LAYLAH Akan sadaki naira dubu dari cif Wanda Kawu ne ya karba laqadan ba ajalan ba
Hakama babbar Sa’ar da Kawun yasamu akan qudiri da niyarsa na hanawa dangin Zainab sanin komai kamar yanda suka so cin Amana
Kafin su Alhaji Atikun su qaraso yasa aka daura auren batareda anjirasuba Dan dama a masallaci ne Kuma ba wani babban masallaci bane daga shi sai Abdullahi sune dangin Laylah sai Turakin da amintaccen yaronsa A Abdoul sai jamaar Dake masallacin wainda basusan waye angonba bare Amaryar Dan kuwa ko labarin duniya basabi bare su shaida Turakin Dan Haka aure dai andaura yakuma samu jama’a daidai gwargwado dasuka ringa bi da adduar Allah ya sanyawa aure Albarka
Dan Haka Koda su Alhaji Atiku dasu Alhaji Qarami suka iso da manyan motocinsu
Suna fakin Ana Gama shafa addu’ar daurin auren saidai Suka ringa bi da Amin na adduoin da jama’a keyi suna ficewa,

Ransu yayi mummunan baci da hukuncin Kawun na daurin batareda anjirasu ba Amma Turaki agurin sai Basu bayyanarba harda qarin sanin Kar abar Turakin da zaman jira yasa aka daura auren ba Kira badan hakan ba da Kawun sai sun nuna Masa rashin mutunta su day yayi
Dan hakan Kamar tazartawane agaresu.

Washe bakuna Suka hau Yi suna gaggaisawa da Turaki Ana Masa adduar Allah ya sanyawa aure Albarka manyan shaddodinsu sai daukan ido sukeyi Dan kuwa ba laifi kowannensu yanada nasa abun duniyar Amma dogon buri da kwadayi yasa Babu abinda suke gani da hange sai Tarin girma da matsayin Turakin Wanda su connection suke dubawa kafin dukiyar tasa.

Daga gurin daurin auren Kai tsaye gida ya wuce batareda jiran Anne ba wadda zata taho dasu Laylan ya wuce airport ya komawarsa Dan yanada baqin Dake jiransa a Abujan.

Fes Laylah take zaune daki cikin adon Dan lace dinta da aka Bata jiyan saidai batai gangancin fitowaba sbd biki sukeyi gidan sosai har dare tukuna aka Kira Sa’adah din akaita mata nasihu da waazin da sirrikan Kama miji musamman Miji irin nata Wanda aqalla kafin yafara Mata kallon mace ma kila saita kusa hade shekaru nawa a gidan kafin yafara Mata kallon Mata Amma dai sun Yarda da sirrinkansu na kayan gyara dasukai Mata Dan Haka suna jiran kyakkwan labari.

Shiru tayi ta a sauraronsu jikinta duk a mace kukanma takasayi sbd batasan ta Yaya zasuji zancen waye auren yake kansaba
Saidai tasan ko tana hauka bazatai gigin fadar komaiba sbd a yanda tsanar Laylah take cikin jininsu komai zasu iya aikatawa akanta
Shiyasa ta sake roqar Anne da Kawu akan Kar afadawa ko Momy sai lokacinda aka tabbatarda zasu wuce da Abba Germany yanda batada lokaci ko damar sanarwa dangi bare wani mummanan al’amarin ya biyo baya tunda Suma a goben zasu wuce.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button