NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL
NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Daki Takoma inda ta tararda Laylah tayi sallah tana daga zaune gurin datai sallar
Ta dago ta kalla Sa’adah cikin yanayi na Dan bayyanarda tayata murna tace”
Anty Sa’adah duk ranarda Abba yatashi zaiyi farin cikin ganinki da aure,
Allah ya Sanya alkhairi Anty Sa’adah.
Wani irin murmushi Mai Dan ciwo Sa’adah tasaki tana cewa”
Amin ya Allah qanwata.,
Kuma kinsan kece Zaki ringa yimun dawainiyar kulawa dashi tunda Kinga kin fini iya aikin musamman abinci.
Fararen idanuwanta ta zubawa Anty Sa’adah din cikin jinjina Kai tace”
Eh Zan Miki komaima na aikin gidan Anty Sa’adah Inshallah.
Dafa kanta Sa’adah tayi kawai tana sake murmusawa
Aranta tace”
Tabbas wannan shine bahaguwar sauyin qaddara,
Anmiki aure batareda kinsan kece matarba,
Zakije gidanki da sunan ‘yar riqon ‘yayarki da kikewa kallon nice Matar,
Nikuma daga aure naqare a zuman riqo gidan Auren qanwa
Wannan badan akwai zumunci ba da dawane suna zasu Kira wannan sauyin lamarin.?.
Gidan umma Jamila ta kwana sbd goben da safe su Momy zasu fara wucewa kafin suma su wuce
Dan Haka duk wani saura ragamar rayuwar Sa’adah umma Jamilan tagama karbarsa daga yau din tunda momyn dai zatabi Abban bayan irin hanatan dasu umma Jamilan da Haj Karima basuyiba har fushi sukaso Yi da ita akan zata kassara sauran rayuwarta gurin jinyar Wanda gurin Cin Amanarta da son zuciyarsa ya hadu da hukuncin dasuke ganin Allah yayimasa akan abinda yayiwa momyn
Amma sbd zamtowarta sirikar Turaki yasa Suka danne fushinsu Dan yanzu Kam zata wuce rainin kowa duk da sunsan har abada sune masu juya momyn sai abinda sukace Mata takeyi.
A Daren Momy tasake jaddadawa Sa’adah komai nata yanzu su umma Jamila ne
Tunda batanan yanzu sune iyaye Kuma gatanta Dan Haka karta ringa komai batareda shawararsu ba
Itadai Sa’adah to kawai take cewa sai alokacin nema tasamu ta rungeme Momy tasaki kukan data keta dannewa aranta tun jiyan ga Kuma kewar mahaifiyarta dazatai dama mahaifin nasu da Babu tabbacin zasu sake haduwa dashi tunda ciwone Babu Wanda yasan yanda Allah zaiyi dashi,
Wani irin nauyi takeji aranta shiyasa ta qanqame momyn tana sake kuka siriri Mai tsananin tsima zuciya Amma su umma Jamila Kam Babu wani Abu dasukaji a zuciyarsu saima rarrashin dasuke Mata akan ai aure bautar Mata ne taje ta Kama uwar mijinta da kyau Dan kuwa mace ce Mai tsananin iko da kaida,
Sam Bata daukan Wasa ko shirme
Komai nata Kai tsaye take yinsa.
Sai datai kuka sosai har idanuwanta sukai nauyi ajikin momyn kafin ta saketa tanajin wasai a zuciyarta
Duk nauyi da radadin datake ji ya sauka gabaki daya tasauke Ajiyar zuciya tareda miqewa ta nufi dakinta tana Jin komai ya Kau akanta sai Kuma fuskantar sabuwar rayuwar Dake jiransu a Gidan riqonsu
Dan kuwa tasan Laylah ma dai kamar riqo ne za’ai Mata Dan maganar auren Anne tace ba yanzu zaaita ba lafiya da ilimi zasu kutsar da ita ciki.
Da wannan tayi adduarta ta kwanta ranta ba wata doguwar damuwa Dan kuwa tasan kyakkyawar rayuwarda mahaifinsu ke musu buri da fata zasuyi ta samun ilimi Mai inganci da zurfi.
Qarfe goma na safe su Momy jirginsu zai tashi Dan Haka tun qarfe Takwas na safe akazo da lafiyayyar mota motar Lexus aka dauki Amarya Laylah da ‘yar uwarta kokuma dai ace Amarya Sa’adah da qanwarta zuwa gidan Turakin Dake Nan,
Sosai Anne ta nuna yabawarta tareda karban Amanar yaran da zuciya Mai kyau
Nan akaiwa su umma Jamila yanda suke so wato kyautar girma data kusan sakata zubewa gaban Anne din Haka suka ringa zuba godiya suna qarawa da iyayi kala kala har suka tafi
Dan take daga umma Jamilan har Haj Karima da Matar Alhaji Qarami sukaji buqatar fita gidan Dan sanin yanda wannan kyautar tasu zata jujjuya a hannuwansu Dan kuwa dalolin Amurka ne Anne ta Basu wainda idan suka canjasu ba qananun kudade bane shiyasa ba kunya kowaccensu ta gifta uzurin rashin damar rakiyar Sa’adah din yanzu zadai suzo daga baya Idan sungama sallamar baqin nesa dasukazo biki
Illa kuwa canjin dalilinsu sukeson tsayawa suyi su kammala Kan dukiyar kowa yasan abinda yayi da tasa daga baya sunbi sahun su Sa’adah din Dan dama zuwa gidan Turaki yanzu Dole ne.
Bayan tafiyarsu motar daukar Momy zuwa airport tazo bakowane acikiba sai driver da Kawu a gaba.
Shigowa Kawun yayi Suka zauna Palo daga momyn sai shi sai Anne wadda kai tsaye tafara magana da cewa”
ZAINAB kamar dai yanda Kika sani Allah Yana jarabtan bawansa ne Dan gwada qarfin imaninsa Dan Haka ki dauka komai na rayuwa na samu da rashi dakuma wasu sauyin duk cikin jarabawa da qudirar ubangiji ne,
Kamar yanda kikafi kowa Sani da shaidawa idan rabo ya rantsa tunda ga Laylah Nan Kin gani ishara
Hakane yakuma faruwa auren da aka daura jiya da Laylah aka daurashi sbd itace da haqqin hakan kin sani
Dan Haka idan da ansaka son Rai an daura da Sa’adah to wlh matuqar akwai rabo tsakanin Turaki da Laylah wannan Rabon saiya kashe Sa’adah ta rasu Dan kawai ayi auren a haifosa yazo duniya Dan Haka mudai munyi adalci kamar yanda Sa’adah da kanta tazo tafada Kuma ta roqemu akan hakan sbd hakan dai shine daidai,
Zainab ki godewa Allah daya Baki ‘ya kamar Sa’adah wadda wlh samun ‘ya kamarta ayanzu Abu ne Mai wuya,
Tayi hankali sosai nakuma yaba Mata iya yabawa shiyasama Zan tafi da ita a hannuna na dauka riqonta da yardar Allah harsai Mahmoud yasamu lafiya Inshallah.
Wani irin kuka Mai sauti da shiga Rai Momy tasaki tana rufe fuskarta da tafukan hannayenta dake wata irin rawa.
Shiru sukai dukkaninsu sbd Bata damar kokawa Dan sunsan hakan akwai tsananin ciwo
Tana ganin ta aurar da ‘ya yanzu Ana fada mata ba wani aure.
Kuka takeyi sosai wanda yasakawa Anne tausayinta tafara Mata nasiha da rarrashi har zuciyar momyn ta Dan Yi sanyi Amma Kam wani nauyi da ‘daci sun Riga sun dasa Mata shi Dan Haka share hawayenta kawai tayi batareda ta dago ta kalli Annen ba murya a cikin yanayi na sanyi da ‘dacin zuciya tace”
Nagode nakuma bar Sa’adah a hannunku.
Jinjina Kai Anne Tayi tana sake Jin tausayin momyn sbd bayan qunci da baqin ciki Babu abinda yake zagaye da rayuwar momyn tsayin shekaru
Dan Haka tana Mata fatar samun budaddiyar zuciya Nan gaba.
Kasa ganin Sa’adah Momy tayi Dan bazata iya hada idanuwa da Sa’adahn ba Dan Haka Kai tsaye fice ta shige mota suka wuce airport
Suna Isa jirginsu ya daga.
Bayan tafiyar Momy da awa biyu Suma masu jirgin ya daga Wanda yasaka daga Sa’adah har Laylah cikin wani mugun yanayi Dan kuwa Babu Wanda yataba ko barin gari acikinsu bare Hawa jirgi har gwara Sa’adah tana Dan yawan tafiya wasu lokutan tareda umma Jamila kokuma Haj Karima Amma ba Wai tafiyar nesaba.
Tafiyar awanni sukai sai gasu a garin Abuja inda manyan Mercedes beymach ke jiran saukarsu Aka daukesu zuwa AB TURAKI RES.
MAMUH
SAKINA VENDABLES ????????
Ina ma’abota son qamshi da gyara? Ina masoya qamshi dasuka San darajar qamshi da gyara irin na qamshi?
To kuzo ga SAKINA VENDABLES Tasake zuwar muku da ingantattu Kuma tsararrin kayan qamshi masu kyau da qarko,
Ga wainda suke buqatan turarukan gaske masu kyau na asalin qamshi da Kama jiki da Kaya suzo ga inda aka tabbatarda kyau da qarfinsu a gurin SAKINA VENDABLES
Turaren wuta list
Queens special
Kajiji mix and r
Kajiji whole
Gabgab
Brown Hawiii
Special Halut
Sandal balls
Sandal strips
Sandal flakes
Dubai oud
White Hawii
Classy Dufr
Black bange
Black bange
Musky Dorrot(Na tsuguno)
Cous cous
Khumra White & Black
Kulaccam Black(for hair) white (for body)