NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL
NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Results dinsa sun nuna infection daya shiga qashinsa tun farko farkon hadarin da ba’a yanke qafafunba sunyi yawanda harsun fara shiga jininsa,
Tabbas yasan yanda yakeji ajikinsa lokacinsa yakusa zuwa
Saidai duk ya kalli Layla da rayuwarda zai barta aciki hankalinsa tashi yakeyi yabar jikinsa,
Tsoro da fargaba tareda kukane suke lullubesa aduk lokacinda yayi tunanin hakan.
Alhaji MAHMOUD tabbas rikicewar lafiyarka a Yan lokutan Nan sunada babbar nasaba da damuwa da kuncin dakake Tarawa aranka,
Da zaga sassauta damuwa da tunani kasamu hutun zuciya Dana qwaqwalwa ko yayane za’a ringa samun sauki ko yayane.
Sunkuyar da Kai Abban yayi ahankali cikin irin yanayinsa na masu ciwo irin nasa batareda ya iya ko dago idanuwansa ya kalli Dr Abbakar din ba.
Shiru sukai tsawon mintuna kafin Dr Abbakar din ya miqe tsaye Yana kallon abban cikin kulawa yace”
Zan tafi gobe zandawo zamu sake dibar sample ajikinka Inshallah saimu gwada wani awon mugani,
Allah yaqaro lfy.
Juyawa yayi ya fice daga dakin har lokacin Abban Bai motsaba Yana yanda yake.
Ahankali idanuwansa suka sauya zuwa ja jikinsa na daukan zafi na wani irin zazzabi Mai qarfi daya saukar Masa atake saidai zuciyarsa ta riqe yakasa tunanin komai saina Mutum daya daya fado Masa a Rai wato babban Amininsa Wanda shikadaine zai iya magance babban abunda yazo ya tokare ransa tsawon shekaru wato damuwar Laylah.
MAMUH
????????????Kuyi following Dina Dan samun posting akan lokaci dama sauran novels Dina complete ????????
Mamuhgee @Arewabooks
Rabo sai Mai shi…Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!
Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon ‘da amatsayin nata mijin?
Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?
NOOR ALBI Hasken rayuwata
Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne
Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi
NoorAlbi#MAMUH
Follow me @ArewaBooks
Mamuhgee For my latest updates
KUFAN WUTA
Safiyya Huguma
BAQAR INUWA
Billyn Abdul
RAYUWAR MACE
Hafsat Rano
MASARAUTA
Miss Xoxo
NOOR ALBI
Mamuhgee
Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank
Number shaidar biya????????
09032345899
KATIN MTN
09166221261
[7/10, 9:12 PM] +234 704 076 8969: https://arewabooks.com/book?id=628264fab77ff582983da456
NOOR ALBI
Mamuhgee
4
Washe gari tunda safe da hadari Mai qarfi aka tashi da iska
Da sauri ta fito palon ta nufa windunan dake palon guda biyu ta rufe ta nufi dakin momyn da sauri ta bude ahankali sbd karta dameta da motsinta
bakinta daukesa sallama ta shiga
Momyn na kwance kan gadon ta nufa windon dakin ta rufe ahankali ta fito ta nufa dakin anty Sa’adah itama ta rufe Mata nata windon kafin ta fito tsakar gidan lokacin iskan yaqara qarfi da gudu ta qarasa dakin abbanta ta rufe Masa koina duk da idonsa biyu bata tsayaba sbd aikin gabanta ta fito da hanzari tafara kwashe shanyar wankin momyn datai jiyan duk wasu har zun fado sunyi qura tahau kwashewa zuwa lokacin tuni ruwa masu qarfi suka sauko ta shiga ciki da sauri ta aje kayan palon Kan kujera duk da tasanma saita Kuma wanke wasu
Ta fito tsakar gidan ruwan na dukanta tahau tattara kayan dake tsakar gidan takai na kaiwa cikin takai na kaiwa Palo tasake fitowa ta taje ta bude gida sbd Kar suna ciki Abdullahi yazo basuji bugun gidansaba.
Kofar kicin ta tsaya ta kakkama gefen kayan jikinta ta Dan matsesu tarage musu ruwan dake tsayaya ta zame Dan kwalin kanta shima ta matse daga waje ta shanyasa Kan kofar kicin din sbd Kan yasha iska Dan kuwa ta barsa da dankwalin sanyin Kan Dana dankwalin suka hadu sanyi zai shigeta ya kwantar da ita
Babu ciwon Dake tsananin azabtar da ita kamar sanyi idan yashigeta
Gashi kwantawarta ciwo ba kyau
Wuya takeci Mai tsanani Dan duk rintsi saitayi aikin dake kanta ga abbanta idan ta kwanta batada Mai kulawa dashi Dan hakan nema take dannewa duk girman ciwo sai idan yafi qarfinta Dan Haka takeda kiyayewa akan lafiyarta.
Risho ta kunna ta Dora ruwan zafi ta hada qullun kunun alkamar dazatawa Abban Takoma ta zauna Kan kujera tana jiran su tafada wani irin sanyin ruwan da ake Yana ratsata tanaji.
Ba jimawa ruwan suka tafasa ta hada kunun ta zuba Masa a flask dinsa ta rufe ta juyewa Anty Sa’adah sauran a flask itama sbd tanashan kunu sosai itama musamman nata dayake da Madara take shansa sbd lafiyar fata Inji momy.
Cikin ruwan takuma fitowa takaiwa bbanta ta basa Tasha tabasa magani ta goggoge Masa jiki ta fito Yana binta da kallo yanda take jiqe sharkaf sai Kama jiki take karta jiqa Masa daki Takoma kicin tahau aikin abincin karin kumallonsu momy.
Dakin Sa’adah taje cikin rashin son takurata daga baccin datake tace”
Anty Sa’adah me za’a dafa na Karin?
Cikin bacci Sa’adah ta juya tana sake shigewa Dan madaidaicin bargonta tace”
Laylah duk abinda kikai Amma dai karki manta da kunu na.
Anty Sa’adah jiya Momy bataci abincin dareba sosai Naga abincin yayi saura ko ulcer dinta ya tashine saina dafa Mata ruwan tea da faten dankali kawai.
Kimata duk yanda kikai kaina na ciwo bacci nakeji sosai.
Juyawa tayi Takoma kicin din tahau aiki.
Wani maganin ulcer din momyn tafara dafawa Mai wuyar dahuwa Haka taita jira har yayi kafin ta dafa taliya Mara yaji ko kadan sbd momyn ta juye a kula ta zuba Mata maganin a babban kofi ta saka Mata a fridge duk da Babu wuta zaiyi sanyi sbd ruwan sanyin Dake ciki.
Tana gamawa anan kicin din taci abincin sama sama tagama tai wanke wanke ta sharesa tsaf ta fito lokacin ruwan sun Dan rage sosai sai Dan yayyafi ta nufi dakinta tacire kayan jikinta ta watsa ruwa ta sauya zuwa wata atampar tafara gyara nata dakin fes ta fito tafara aikin gyaran palon tana gamawa tashiga na mum tayi Takoma na anty Sa’adah tayo tafito tsakar gidan shima Tai Masa tas kafin ta fita tasamo garwashi maqota tazo tayi turaren wutarda momyn qaidane sai anmata shi Dan tanason qamshi.
Gurin abbanta ta nufa ta gyare Masa koina taje ta dauko Dan sauran burbushin hayaqin turaren daga palon Momy takawo Nan dakinsa shima yasamu Dan qamshin ko yayane,
sai alokacin ta zauna gabansa bayan ta aje kaskon turaren cikin kulawa a natse Tai Masa Ina kwana tana kallon idanuwansa dasuka qanqance Suka sauya launi da alama Bai samu bacci ba ta dauko ruwa tasake bashi yasa cikin kulawa a natse tabude Baki tace”
Abba?
Akwai wani matsala da kakeji ne?
Saida ya Dan hadiye yawun dayake hadiyewa da dabara daqyar shiyasa shi nasa ciwon baya zubarda yawu ta gefen Baki Allah ya taimakesa saboda saukin dayake samun Yana iya hadiye yawu.
Dan rintse idanuwansa dasukai laushi yayi ahankali alamar yanada damuwa.
Faduwa gabanta yayi da qarfi saidai fuskar Bata nuna hakan
Ta zuba Masa fararen idanuwanta batareda ta iya cewa komaiba.
Hannunsa Dake rawa da gyangyadi yadan daga yayi Mana alamar karta damu bayajin ciwon komai.
Shiru kawai tayi Dan batasan Mai zataceba bayan jurewa ta boye damuwarta sbd ko nacewa tayi tasan abinda yake damun nasa Babu abinda zata iya Masa bayan tashiga qunci da damuwa sai addu’a da take Masa.