NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEENOVELS

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL

NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Gurin Abba Sa’adahn tazo cikin nutsuwa da farin cikin ganinsa ta zauna gefensa tana gaidasa tareda Masa ya jiki.z

Zuba Mata idanuwansa yayi Yana kallonta cikin farin ciki tareda tausayinta Mai girma cikin ransa,
Tabbas Sa’adah Mai hakuri da tawakkali ce tunda Bata Bari son abun duniya ya hanata barin Yar uwarta ta auri Wanda akace dinba,
Kawu saidu ya sanar dashi komai Dan Haka har abada bazai daina sakawa Sa’adah albarka ba gode Mata.

Tunda Anty Sa’adah ta iso Momy take Nan Nan da ita sai jikin Laylan yasake yin sanyi tanason sakewa da anty Sa’adahn Amma ta Kama kanta sbd gudun bacin ran momyn.

Ana Gama sallar magriba saiga A Abdoul yayi knocking ahankali yashigo dakin sanye cikin white Balenciaga sleeves da blue Armani trousers sai jacket din sanyi Mai tsayi datakai gwiwarsa,
Qamshin turarensa na D&G na tashi ahankali ya kalli Momy cikin tsananin girmamawa ya gaidata…

Dayake ta Saba dashi sosai sbd komai na dawainiyarsu shi yake zuwa yayi shiyasa sukeda sabo cikin sakewar fuska da kulawa tace”

Lafiya kalau Abdoul, Jiya saika tafi baka Bari nadawo ba.

Murmushi yayi Yana cewa”

Nakira wayanki naji akashe shiyasa na wuce din kawai…

Zatai magana sukaji shigowar Turaki Wanda qamshin turarensa yafara shigowa dakin kafin shi din yashigo Yana sanye cikin navy blue Ralph Lauren Kaftan St, Hasken fatarsa yafito sosai sbd duhun kayan jikin nasa hannunsa dake sanyeda agogon diamond Rolex riqeda wata paper bag da tsadadden turaren dayasan Amininsa Yana amfani dashi tun lokacin Yana lafiyarsa cikin arzkikinsa yasaba duk zaizo gurinsa saiya zo Masa dashi Dan Haka cikin nutsuwarsa da kamewarsa ya qarasa shigowa dakin duk sukai tsit suna Dan rage kallonsu daga kansa,

Sa’adah kallo daya tayi Masa ta Dan sauke Kai tareda bude Baki ta gaidasa cikin girmamawa,
A hankali ya amsa tareda Dan kallon gefen Momy suka gaisa Yana tambayarta jikin Abban Dake kallonsa da dukkanin kauna irin ta Dan uwa na jini dayake jinsa.

Daga inda take zaune ta saci kallon abbanta da Momy harma da anty Sa’adah kafin ta Dan saci kallon gefensa taga yanda kwarjininsa duk yabi ya cika idon dukkanin wainda ke dakin sai Taji kunyar da Babu dalili ta kamata Dan Haka ahankali itama cikin nutsuwa kanta a qasa tace”

Abba barka da shigowa.

Bai waiwayoba ya amsa Mata a gajarce cikin kamewa sbd idan yayi gangancin waiwayowa ya kalleta gurin amsawa za’a iya gane halinda suke ciki Dan Haka gabaki daya hankalinsa na Kan Mahmoud dayake magana dashi.

Miqewa tayi ta sulale ta fito Momy ma dama duk fita zasuyi Dan Haka gabaki dayansu Suka fito dakin aka barsa daga shi sai Abban.

MAMUH

[7/10, 9:36 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 35
Suna fitowa waje Momy taja Sa’adah suka nufa inda zasu zauna taje ta siyo Mata ginger drink Mai zafi suka zauna suna magana.

Itama zama tayi a can gefe tareda fidda wayarta jiki amace ta Rasa wa zata Kira saiga Kiran Anne ya shigo wayarta wani sanyayyan murmushi ne ya sauka Kan kyakkyawar fuskarta ta dauki wayar anatse cikin farin cikin Jin Annen tafara sauke nannauyan numfashi tace”

Nagode Anne.

Murmushi Annen tasake Jin irin numfashin da Laylan tasake na samun saukin damuwa kafin tace”

Kina asibitin ne haryanzu tareda Momynku kenan?

Sunkuyar da Kai tayi takuma sauke wani numfashin kafin ta dago ta saci kallonsu anty Sa’adahn yanda Momy ke magana da ita cikin tsananin kauna da kulawa irin ta mahaifiya zuwa ga yarta,
Jin tayi idanuwanta suna kokarin cikowa da hawaye akaro na farko dataji kewa da maraicin rashin uwa,

A da rayuwarta batasan Jin Dadi,yanci ko walwalaba,
Batasan wani kwanciyar hankaliba ko wata yancinda har zatai kewar uwa,
Batada lokacin kanta batada na mahaifinta koyaushe rayuwarta acikin hidima da dawainiyar Momy da Anty Sa’adah da dangin Momy take,
Bata samu yancin kewan tata mahaifiyarba sai yanzu datai rayuwar yanci,
gata,
Jin dadi da kwanciyar hankali,
Tabbas itadin marainiyace badan Anne da Abba turakiba harma da mum Na’ima dake kishiyarta sun Bata kauna da kulawar da Bayan abbanta da anty Sa’adah Babu Wanda ya taba kaunarta Haka…
Meyasa Momy bazata kaunacetaba Koda so dayane?
Aranta har Koda yaushe Momy zataci gaba da zama uwa gareta Koda bazata taba kaunartaba ko yafe Mata laifin mahaifiyarta datake kallonta dashi…

Kokarin maida hawayenta tayi a sanyaye tace”

Anne inason zanbiyosu Abba idan an sallamesu.

Murmushi Annen takuma Yi a natse tace”

Karatun naki fa?
Kinriga kin fara Haka Zakiyi hakuri ki lallaba ki Gama kafin kidawo
Koba komai dawowarki ai Dole ne idan har za’a sanarda Na’ima matsayinki zamanki acan nada hadari,
Dan Haka kici gaba da kiyayewa karkiyi maganar da kowa Koda Wasa fa,
Ba yanzune lokacinda zata saniba sbd akwai zafi kishi Sosai agun Na’ima kici gaba da rayuwanki bakida alaqan komai da Turakin Bayan ta Abbanki ayanzun tunda nanma bakowa yasan matsayinki agunsa dinba saikin Gama karatun tukuna Zaki dawo kafin ayi komai kowa ya shaida ke matarsace…

Tsit Laylan tayi sbd batada bakin mgana akan maganar Anne Dake gargadarta akan ta tsaya a alaqar abba da ‘yar riqonsa tsakaninta da Abba Turakin,
Kunyar kantama taji ta kamata sosai tunowa da dabatai barin cikin data samuba tayaya zata fuskanci kowa da cikin?
Ko sama da qasa zata hade tasan bazata fadawa mum Na’ima cikin waye ajikintaba,
Annenma batasan tayaya zata iya Bari ta hada Ido da itaba da ciki ajikinta,uwa uba Anty Sa’adah da afarko take Masa kallon mijintane…..gasu umma Jamila da Suma Suka Fado Mata arai
matuqar kuwa sukaji cikin jikinta na Wanda sukasan mijin anty Sa’adah ne umma Jamila zata iya ratayeta sbd irin tsanar datake Mata da bakin dasuke Mata Mai jinin cin Amana..

Wato tabbas akwai tashin hankali idanda cikin Bai fita ba,
Hakama akwai masifa Mai girma agabanta idan ta kuskura tsautsayi yasata samun wani cikin…

Wannan tunanin ya daga hankalinta matuqa sbd duka wannan tunanin baizo kantaba sai yanzu da maganar Anne ta tunatar da ita,
Shin yazatai da rayuwarta duk cikin Abban ya bulla ajikinta bayan Babu Wanda yakawota yace gatanan ankawota gurin mijinta,
Daga sama zancen Aurenta dashi ya bayyanar mata…..

Gama wayarta tayi da Anne ba’a cikin nutsuwartaba sbd yanzu Kam komai ya tsaya Mata akai,
Uwa take buqata ayanzun kamar Momy Dake dawainiyar Sa’adah Dan ta kwanta jikinta ta sanar da ita abinda yake faruwa a rayuwarta,
Anty Sa’adah ce tamkar uwa gareta wani lokacin,
Ita kadai take iya fadawa komai Amma Momy bazata taba barinta sakewa da itaba saboda tasan itama tayi kewar yarta Dan Haka take kallonsu daga nesa cikin burgewa da suna kulawa da juna….

Fitowa yayi daga dakin Abban wayarsa a hannunsa Yana kokarin daga Kiran daya shigo wayar idanuwansa suka sauka akanta jikinta duk amace ya zubawa su momyn Ido…

Yana iya hango yanayinda take ciki na kallon datakewa su momyn,

Wani iri yaji har cikin ransa na yanda take a kadaice tana musu kallo daga nesa..,

Jin kamar zuciyarsa bazata iya daukaba yasashi dauke Kai daga kallon gurin ya nufi inda take
Tun kafin ya qaraso taji qamshinsa na tunkarota ta Dan waiwayo ta zuba Masa fararen idanuwanta dasuka Tara hawaye saidai Basu saukaba tafara kokarin maidawa tareda sauke Kai daga kallonsa..

Yana zuwa Inda take a natse ya furta”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button