NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL
NOOR ALBI COMPLETE HAUSA NOVEL BY MAMUHGEE

Minti hudu da fitar Dr faruk ya dawo dakin daukeda folder din Sa’adah ya Ciro wata takarda yana kallon Anne dake kallonsa ganin ya dawo
Kowama kallonsa yakeyi suna jiran Jin Mai zaice ya miqawa Anne takardar Yana cewa”
Wannan inaga ba nata bane Dan a cikin namu gwaje gwajen bamu samu ciki a jikinta ba…..
Tsit sukai gabaki daya dakin suna kallonsa,
Anne da Momy da Abba dasukasan batada aure da mamaki da suke kallonsa,
Umma Jamila kuwa cikin kasa boye halin data shiga tayi saurin cewa”
Takardar ciki ta nuna ita ko me?
Miqawa Anne takardar yakuma Yi ganin tana Masa kallon buqatan qarin ya kalli sauran Yan dakin yaga duka iyayen Sa’adahn ne ya maida kallonsa kan Anne cikin nutsuwa yace”
Takardar pregnancy test ne tareda scanning Amma banajin nata ne sbd ba’a qasar Nan akaisa ba,
A America ne,Los Angeles….
Anne najin hakan ta karba takardar da sauri ta karance tsaf taga abinda yake ciki da sauri ta dago ta kalli Sa’adah Dake zaune tanajinsu Bata iya cewa komai sai rufe Ido datai cikin yanayi na rashin abin Yi.
Qamshin Bois elite ne yafara shigowa dakin Abba da Anne dasukan asalin waye Mai wannan qamshin Suka kalla kofa kafin shigowarsa
Tukuna ya shigo A Abdoul na bayansa
Dukkaninsu suka waiwayo suka kallesa yaqaraso cikin tsananin kwarjininsa daya Hana su umma Jamila tada hayaniyar murnar batun ciki da ake lokacin….
Haj Karima ce tayi qarfin halin gaidasa tana maida kallonta Kan Anne Baki washe tace”
Barka da arziki,
Ashe ciwon dai harda juna biyu ajikinta,
Allah ya raba lafiya yasa anbude hanyar tara zuria kenan…
Kujerar da A Abdoul ya gyara Masa ya zauna Yana kallon Abba dake neman rudewa da zancen da ake…
Anne ganin Kar rashin fahimtar tayi yawa ta bude Baki tana dauke kallonta daga kan Turaki daya Gama cika musu Ido dakin da kwarjini tace”
Ba sunan Sa’adah ne ajiki ba, takardar ba tata bace sbd ba komai ajikin Sa’adah.
Miqawa Turaki takardar tayi tana cewa”
Duba kagani ko zaka gane sakamakon waye.
Karba yayi tareda Dan kallon takardar akan sunan Mrs AB TURAKI idonsa yafara sauka kafin ya kalla date din jike jikin takardar.
Da sauri ya gangara da idonsa Kan signing dinta Dake qasan takardar.
Wani irin yanayi Mai wuyar fassarawa ya Shiga saidai mutanen Dake gurin ya sanyashi dannewa ya kame,
Miqawa A Abdoul takardar yayi bayan ya nade Yana miqewa yace”
Allah yabata lfy.
Kofa ya nufa ya fice A Abdoul na bayansa
Yan dakin duka kowa tsit yakuma Yi Dan su Kam Basu gane komaiba Kuma yanzu.
MAMUH
[7/10, 9:37 PM] +234 704 076 8969: Mamuhgee 44
Anne shiru tayi Bata sake tada maganar al’amarin takardar cikin ba sbd batasan wa zata Kama zancen dashiba,
Sa’adah dai batace komaiba sai cewa ba nata bane Haka kawai tace musu tabarsu a duhu,
Momy Bata damuba sbd tasan Babu abun daya hada sa’adahnta da wani zancen ciki Dan Haka itama tayi watsi da zancen tunda cikin Laylan Bai shafeta ba.
Abbansu ma share zancen yayi sbd Ganin Anne batace komaiba Kuma yasan tarbiyar yaransa daidai gwargwado duk da yajima baya taredasu
Amma tunda yanxu tarbiyarsu a hannun Anne take bashida ta cewa Akan maganar yabar zancen tunda yasan sunsan abinda suke.
Umma Jamila ce ta daga hankalinta Kan ayi maganar qarshe Sa’adah da kanta tace”
Ba’a son tada zancen ne sbd matar Turakin Ms Na’ima da ake gudun fitinarta.
Wata dariyar bin iska Umma Jamila tayi tana cewa”
Akwai Wanda ya Isa aji shakkarsa akan samu da qaruwa daya samemu na farin ciki,
Ita Ms Na’iman inace da Turakin take takama? To shine ake wani boye boyen karta sani.
Haj Karima dake Shan tea ahankali cikin nutsuwa da takama tace”
Sune sukasan wata Ms Na’ima
Mu abunda yake gabanmu mukeyi,
Ciki dai tunda Allah ne ya badashi ai Babu wata Na’imar dazata sakamu kame kamen rashin fadarsa.
Cikin sanyi Sa’adah Dake sin plantains ahankali tace”
Wlh tanada ban tsoro mama,
Komai zata iya,
Dan Allah abar maganar shine yafi zama alkhairi..
Tsoronta kike kenan? “” Cewar haj Karima tana kallon Sa’adahn a zube.
Ba boye boye tace”
Eh wlh Ina tsoronta mama,
Nasan komai zata iyane.
Umma Jamila ce ta kalli Momy dake saka kayanta cikin akwatinta sbd tafiyar da zasuyi Dan ansallamo Sa’adahn suna gidan Haj Karima daga Nan zasu wuce gabaki dayansu duk da sai Sa’adah Takoma gida ta dauko kayan da zatai tafiya dasu,
Cikin mamaki da takaici tacewa Momy”
Yanzu Zainab Haka Kina kallo Kika koyarda Sa’adah tsoron kishiya?
Sbd ke Taki zuciyar ta mutu gurin jinyar mijin daya zaba Taki kishiyar akanki da yarki shine Zaki kashewa yarinya zuciya da tsoron kishiya kina kallo harda bakinta take fadar tsoronta takeyi.
Rashin Jin dadin maganar da ake fadawan Momy yasa Sa’adah kallon Momy da batace komaiba ita sai shiru datai tana cigaba da shirya kayanta cikin akwati,
Ta maida kallonta Kan umma Jamila dake fada cikin takaici zatai magana Haj Karima ta katseta da cewa”
Yi mana shiru mutuniyar banza,
Shiyasa kika kasa gaba Kika kasa baya acikin gidan,
Kinkoma tamkar Yar riqo a gidan ma Matar gidan ba,
Tsabar rashin yanci a bangaren Mahaifiyarsa aka Baki Palo da daki
Bayan ita tanada makeken bangaren guda a gidan da zata aje irinki guda nawa,
Drivers ke janta da motacin Alfarma tana yawo a agarin Abuja da wajenta Amma ke kece kike tuqa kanki Dan kina ganin ansiya Miki tsadaddiyar mota bayan motocin Turakin da ake fita da ita cikinsu daya zata siya biyar din Taki harda canji Mai yawa…
Umma Jamila da Shirun Momy ke Bata ranta ko yaushe tace”
Ahaka me tasamu bare mu iyayenta muce ‘yarmu na auren Amb AB TURAKI,
Alhaji Qarami Babu shige da ficen da bayayi Dan yasamu ganin Turaki shida honourable kwangila sukeso kamar me ko manyan kudi zasu saukar musu Amma koyaushe yarinyar Nan cewa takeyi baya qasar
Ashe tsoron zuwa gurinsa take sbd kishiya,
Wlh Allah yayi wadaran naka ya lalace.
Yanzu dai tagama wannan shashancin mutafi ai muma lokacinmu yazo Dan idan muka tafi zamu bude namu asusun lissafin agurinsa tunda ga ciki
Kafin ki dawo saikin haihu tunda ba qasar yake zamaba Kuma kingama karatun ai dama Dan Haka muma Bismillahi.
Daga Sa’adahn har momy Babu Wanda yasake cewa komai,
Suna sauraron su umma Jamila nata musu fada kokuma fade da gorin dawainiyarsu dasuke Dan taimakawa tun lokacinda Sa’adahn na qarama da Abban baya wani zama har lokacinda yake jinyarsa sune suke Dan taimaka musu.
Har dare daga ita har momyn Basu huta da fadan umma Jamila ba Saida Haj Karima ta tsayar da zancen da cewan ai yanzu tunda Sa’adahn na hannunsu zasu qaru da Turakin.
Da wannan umma Jamila ta sarara musu har drivern Anne yazo ya dauki Sa’adah a gidan Suka tafi gida.
Tana Isa gida komai na dakinta halima ta gyara ko’ina sai qamshi da sanyin AC ke tashi Bata wani zauna ba ta shige ta kwanta sbd kunyar Anne takeji batasan Mai zatace Mata gameda cikin Nan da Allah yayi bayyanarsa gaban kowaba,
Takardar acikin hanbag dinta dasukaje asibitin tun wancan lokacin take Kuma tunda tadawo take boye hanbag dinma gabaki daya sai ranarda zata fita ta janyota ta fita da ita Kuma ranar ne tsautsayi yahau kanta har tayi murnar Babu Wanda yagani a jakar shiyasa takuma boye jakar sai yanzu Allah yanufa zancen zai fita,
Kunyar Anne datake ji shine na boye Mata itama Basu fada Mata ba bayan ta cancanta tasani sbd yanda ta daukesu tamkar jininta
Kuma tasan idan Annen tasani Babu yanda zatai tabari a cutatar da Laylan gashi rashin wayonsu yasa tasamu zancen daga sama gashi taqi cemata komai akan zancen
tamaqi tayarda zancen tayi kaman ba’ayiba.