NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

????????????????????????????
  NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????
        

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

        EPISODE Ten

       WASHE GARI

       BAFFA ne jingine jikin motar sa yana duba waya, yana sanye cikin ƙananan kaya kamar yanda ya saba waɗanda suka matse sa sosai, kansa da askin zamani da yayi masa kyau sosai, sai faman shaining yake yi alamun ya sha mayuka masu tsada

Shakira CE tafito cikin shirin ta, tana tafiya ɗai-ɗai kamar baza ta taka ƙasa ba, har ta wuce ta hangi Yayan nata tsaye wajen motan sa, sai ta juyo tana kallon sa taɗan ɗaga murya tace, “Yaya inzo mu tafi tare ne?”

Lokacin ne Baffa ya ɗago kansa yana kallon ta, sai da ta samu harara kafin yace, “Where is your car and I will take you?”

“Here’s Yaya, wlh I don’t feel good about my body that’s why I don’t like driving”.

Gajeren tsaki ya ja yana ɗauke kai a kanta yace, “babu inda zan kai ki ki nemi drever”.

Har ta buɗe baki da ninyan yin masa magiya sai taga yana kallon hanyan ƙofar shiga gidan yana sakin murmushi, itama juya kai tayi ta kalli wajen

Ɗahira ce ta fito sanye da Jan abaya me kwalliyan Flower’s da stones a jiki, tayi Rolling da ɗankwalin Rigan, face ɗin ta sanye da ɗan siririn farin glasses ????ɗin ta wanda ya ƙara wa Sky Green ɗin cikin idanuwan ta kyawu, tunda ta fito itama take murmushi tana taho wa cikin tafiyar ta na yanga tamkar zata karye

Tana isowa suka sakarwa juna murmushi me bayyana haƙora, sannan ya buɗe mata motan ta shiga, shima zagaya wa yayi ya shige yaja ya nufi Gate

Shakira dake tsaye kamar an dasa ta ta saki baki tana kallon motar har ta fice

“Cab ɗijam.. Kar dai ace hasashe na ya zama gaske? Uhmm idan ko haka ne tabbas akwai matsala, babu yanda za ayi na bar Yayana yaso wannan me kama da mujiyan.. ina sam”.

Ƙwafa tayi tana nufan motan ta ta shige taja ta fice a gidan, ko a cikin motan tunanin yanda ta gansu yau ɗin ya tsaya mata arai, duk da ta san cewa babu wanda ya kai Ɗahira da Baffa shaƙuwa a gidan, amma kuma abinda take gani cikin idanun yayan ta yasa yau ta ɗaura zargi akan su.

             Har tazo ta wuce motan su Baffa a hanya tana kallon motan ta mirror tana jan tsaki, tana kitstsima abubuwa aranta da yawa.

          Su kuwa a cikin motan hira Baffa yake ta mata cike da tsananin ƙaunar ta, ji yake yi ba ya son ko kaɗan tafiyan da suke yi ya ƙare sabida shauƙin da yake ji, shiyasaka yake tafiya a hankali kamar bazai yi ba

Ɗahira kallon sa tayi tana dariyan labarin da yake bata tace, “Yaya don Allah ka bari haka kar cikina ya fashe”.

Dariya shima yayi yana kallon ta cike da so yace, “ai Ni nafi son in gan ki kina Farin ciki ne shiyasa nake baki labarin, don haka Ni bazan Dena ba, bari ma in baki wani”.

Murmushi tayi me ƙayatarwa cikin ɗauke kai akan sa tace, “to Yaya kabar ni haka dai zuwa anjima sai ka bani”.

“Well, my dear Sister, it’s over no matter what you want me to do.”

Still Murmushi tayi idanun ta akan titi, sau da dama tana mamakin yanda Baffa yake nuna mata kulawa fiye da tunanin ta, kuma yake yin duk abinda take so yake barin duk abinda ba ta so, tasan cewa yayan nata me ƙaunar ta ne tun tana ƙarama don ba ya son ɓacin ranta.

       Yana yin parcking a haraban asibitin ya fito ya zo ya buɗe mata yana nuna mata hanya da hannu, cike da murmushi a face ɗin sa yace, “Yauwa Gimbiya fito an kawo”.

Sunan da ya kira ta dashi ya saka tayi dariya tana kallon sa cike da farin ciki, zuro ƙafafun ta waje tayi ta fito, sannan ya rufe suka jera sukayi ciki.

               ⚫⚫⚫

“I told you to come in at 08:00am o’clock. Me ya tsayar da ke?” Doc. Said yayi maganar yana juyawa cikin kujeran sa

Fari tayi da idanun ta sannan tace, “kai ma ban da abun ka ya Docta; kasan ba a raba mu da ɗan shafe-shafe na kwalliya, kuma ka ga 08:00am yayi wuri da yawa”.

Murmushi ya saki yana sakar mata wani shu’umin kallo

“Uhmm Sulaima kenan! That’s why I love you more sabida wannan kwalliyan naki, ko kaɗan baki wasa da jikin ki wajen kin ga kin fito kin burge kowa, wasu kuwa ko a jikin su be dame su ba”. Yaƙarishe maganar da taɓe bakin sa

Dariya tayi tana sake lanƙwashe murya tace, “Ya Dacta kenan! Ni fa nasan da wacce kake yi, kuma kasan zan iya zuwa in faɗa mata”.

Waro ido yayi yana dariya yace, “rufa min asiri don Allah karki haɗa ni da ita kin san halin ta, but yaushe Ni zaki bani dama ne wai? Na gaji da wannan kwane-kwanen da kike min”.

Sulaima tace, “Ya Dacta Ni fa gaskiya ba na tunanin zan iya harka da kai, ko ka manta kai Mijin Yayata ce? Haba dai ka sauya tunani mana Ni gaskiya bazan iya ba”. Taƙarike maganar a shagwaɓe

Lumshe idanu yayi yana sake kallon ta cike da tsananin sha’awar ta, sai da ya ɗago daga jikin kujeran ya ɗaura hannayen sa kan Deks ɗin sa sannan yace, “Sulaima kin san ni; na sanki, why kike son haramta min kan ki? karki manta fa ba wai na ce miki auren ki zan yi ba bare ki kawo wani zancen Ƴar uwan ki, Ni dai don Allah ki bani dama mu more rayuwan mu tare kin san bazan iya haƙura dake ba, kinga matsayin ki daban matsayin ƴar uwanki daban a waje na”.

Murmushi tayi tana girgiza kanta cike da yauƙi tace, “ya Dacta let’s change our talk, muyi abinda ya kawo ni ka ga ina da inda zan je”.

Doc. Said yace, “to shikenan tunda kin fi son haka, amma ki sani ba wai na bar maganar bane kenan, yanzu ya aka yi kika bar ciki ya shiga jikin ki?”

“Hmm tsautsayi mana, wlh nayi mamaki da naje Hospital aka gwada Ni wai ciki ne dani, kuma duk wani matakan tsaron da na saba yi nayi but abun kamar almara”.

Ɗage kafaɗa yayi yace, “any way muje ki hau gadon in duba ki mu gani, don Nima Ina da aiki yanzu a gaba na”.

Tashi tayi tana cire gyalen jikin ta ta nufi wajen gadon, shima ya tashi ya bi bayan ta.

             ⚫⚫⚫

    Zuwan ta Office ta tarar da patients ɗin ta suna jiran ta, yau bata zo akan lokaci ba hakan yasaka har suka rigata zuwa tunda ƙarfe 10:00am zata soma duba su, yanzu gashi har goma saura

Tana shiga ta saka rigan aikin ta sannan ta zauna taba su umarnin shigowa ɗaya bayan ɗaya tana duba su, tayi wajen awanni biyu tana faman duba su sannan ta gama ta tashi ta shiga Toilet tayi uzurin ta ta fito, wasu files ta ɗauka ta fita ta nufi rooms ɗin patients ɗin ta masu jinya

Tana shiga da gadon farko ta fara, taƙarisa da fara’an ta tana gaishe da matar dake jinyar wata burduwan yarinya, bayan sun gaisa cikin faram-faram sannan Ɗahira tace, “Mama har yanzu bata farka bane?”

Mama tace, “ta farka jiya da daddare, kuma Dacta ɗin da kika ce zata zo ta duba ta ita ta duba ta, ga ma takardan da tace, “in baki”. Ta miƙo mata takardan

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button