NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Sai a lokacin Baffa ya ɗan saki fuskar sa kafin yace, “Allah Sarki ai ban gane ki ba, amma fa bakin ki ya riƙe suna na da yawa”.

Ayush cike da yanga tace, “ai ba baki na bane ya riƙe sunan ka ba, sunan ka ne ya zauna a baki na, daɗin sunan ka ke sakawa ba na gajiya da faɗin sunan ko da kuwa na so bari”.

Murmushi kawai yayi yana kallon ta

Ita kuma sai ta gyara zaman ta da kyau tana sake kafe sa da idanu tare da son burge sa tace, “kayi haƙuri da kiran da nayi maka jiya amma zuciyata ce ta kasa haƙuri da son ƙulla alaƙa da kai, idan har baza ka damu ba zan so mu zama friends duk da kuwa nasan nayi maka katsalandan cikin rayuwa, amma gaskiya bazan ɓoye maka ba ka burge Ni ne sosai shiyasa nake son wata alaƙa me ƙarfi ta shiga tsakanin mu”.

Numfashi Baffa ya sauke yana kawar da kansa kafin yace, “naji bayanan ki A’isha duk da kuwa Ni ɗin ba na abota da mata, sai dai bazan iya watsa miki ƙasa a idanu ba musamman yanda kika yabe Ni kuma kike son ƙulla alaƙa dani, babu damuwa”. Yaƙarike maganar yana kallon ta

Murmushi tayi tace, “gaskiya kana da sauƙin kai ba kamar yanda nayi zato ba, naji daɗi da ka amshe Ni hannu bibbiyu Allah yasa hakan shi yafi alkhairi”.

Baffa smiled and said, “ameen no worries”.

Ayush miƙe wa tayi tana kallon sa tace, “Let me go and see you next time, friend?”

“Ok Thanks friend”. Yayi maganar cikin kwaikwayon muryan ta

Sai suka yi dariya gaba ɗaya cike da nishaɗi

Ɗaga masa hannu tayi tana murmushi kafin ta juya ta nufi ƙofa ta buɗe

Dai-dai lokacin itama Ɗahira ta saka hannu za tayi Nocking

Ganin an buɗe ƙofan shiyasa ta janye hannun ta tana kallon Ayush da itama ta kafe ta da nata idanun tana ci gaba da murmushin ta

Kallon kallo sukai wa juna na ɗan sakonni kafin Ɗahira ta janye jikin ta a hanya don Ayush ɗin ta wuce

Fito wa Ayush tayi still tana kallon Ɗahira da ita kuma ta cire nata idanun akan ta tana gyara zaman Eyeglasess ɗin ta, sai kuma ta sake kallon ta har yanzu Ayush ɗin itama kallon ta take yi, hakan yasa Ɗahira ɗan sakar mata murmushi cikin sanyin muryan ta me daɗi tace

“Sannu ko”.

“Yauwa sannu”. Cewar Ayush itama tana faɗaɗa murmushin ta

Ɗahira bata sake cewa komi ba ta buɗe ƙofar ta shige tabar Ayush nan tsaye tana bin ta da kallo kamar t.v

Tana shiga ta sauke idanun ta kan Baffa da shima har yanzu yana murmushi be ci gaba da aikin ba

Yana ganin ta ya sake faɗaɗa murmushin sa yace, “welcome my dear Sister”.

Murmusawa tayi kafin ta soma takowa ta’iso wajen; ta zauna a kan kujeran da Ayush ta tashi

“Dear Brother Welcome to work”. Sai kuma ta’ajiye takardun hannun ta a saman table ɗin tana faɗin “ga shi Yaya”.

Ɗauka yayi yana dubawa cike da jindaɗi ya sake kallon ta yace, “yauwa my dear wlh Sam na manta, kuma Abba ne yace na taho masa dasu ashe na barsu a gida, yanzu bari inje in Kai masa”.

Ya miƙe tsaye riƙe da takardun a hannu

Itama miƙewan tayi tana gyara zaman jakar ta a kafaɗa tace, “nima bari in wuce sai anjima”.

Za gayowa yayi suka jera suka nufi bakin ƙofan, shi ya buɗe ƙofan ya matsa mata ta wuce sannan shima yafita.

            ⚫⚫⚫

    Kallon sa Hajja Fatu tayi cikin ƙasa-ƙasa da murya tace, “Dr. Zubairu idan har ka yi min aikin nan tabbas Ni da kai yanzu muka ƙulla, duk abinda kake so zan taimaka maka da shi, da kuma yarda na zaka ci gaba da shigo da kayan ka ba tare da ka sami wata matsala ba, Ni dai kawai fata na ka shiga jikin su sosai ta yanda zaka gano min duk wani sirri na cikin asibitin nan, kai Ni ban cire maka Mijina ba har shi ina so ka shiga jikin sa, idan har…”

Maganar nata ne ya maƙale sakamakon turo ƙofan da aka yi, idanuwan ta kamar za su faɗo ƙasa haka take bin ƙofan da kallo, ganin wacce ta shigo ɗin ne ya saka ta daka mata tsawa cikin fusata tace, “Are you going to come into my office without my permission?”

Cikin rawan murya Safna da ta ƙame a bakin ƙofan tace, “don Allah Dr. Kiyi haƙuri wlh nayi Nocking naji shiru shi ne na shigo”.

Harara ta balla mata tace, “uban Nocking kika yi, kin yi Nocking ɗin ne zamu kasa ji? Shashashan yarinya kawai”.

Safna saukar da kanta ƙasa tayi duk jikin ta rawa yake yi

Dogon tsaki Hajja Fatu tayi tace, “uban me ya kawo ki to?”.

Da sauri Safna said, “These are the files that Dr. Abubakar told me to bring to you, in the Female ward to check on the Patiens brought in, and then one needs an emergency theatre”.

Tsakin Hajja ta kuma ja kafin ta sake balla mata harara tace, “dalla bani ki ɓace anan”.

Kamar dama jira take yi ta’iso da saurin ta tazuba files ɗin gaban ta ta juya ta fice da mugun sauri, tana fita ta sauke ajiyan zuciya cike da tsoro, sai da ta sake juya kanta ta kalli ƙofan kafin ta sake sauke wani ajiyan zuciyan, cikin ranta take cewa, “waii! wannan matar shegiyar mata ce wlh duk ta tsorata Ni da wannan uban tsawar nata, ko ma uban meye suke tattaunawa da ba ta so inji? Munafuka kawai”.

Sai ta sake kallon ƙofan sannan kuma ta juya tayi gaba da sauri, Office ɗinta babu nisa da wajen tayi saurin shige wa.

     Fadila da ta fito cikin office ɗin ta kusa dana Safnan; tana sanye da labcoat ɗin ta a jiki ta nufi office ɗin Hajja Fatu

Hajja Fatu wacce taci gaba da yin ma Dr. Zubairu bayani ta sake jin anyi Nocking, cak ta tsai da maganar ta tana kallon ƙofan

while shima Dr. Zubairun yabi sahun ta

Siririn tsaki taja tana ba da umarnin shigowa

Fadila opened the door and walked in

Ganin Fadila ce hankalin Hajja Fatu ya ɗan kwanta har da ƙirƙirar murmushi tana yafa ma fuskarta

Cikin miskilancin ta Fadila tace, “Hajja Drugs ɗin nan zaki bani”.

Hajja bata ce komi ba ta buɗe drowan table ɗin ta ta ɗauko keeys ta miƙa mata tana faɗin, “Take” look at the Sif there and pick it up.”

Amsa kawai Fadila tayi ta nufi wajen sif ɗin ta saka keey ɗin ta buɗe ta ciro wanda zata ɗauka ta rufe ta dawo mata da keeys ɗin, tana amsa ta juya ta fice

Ita kuma Hajja ajiyan zuciya ta sauke tana sake mayar da hankalin ta kan Dr. Zubairu da shima yake kallon ta

“Dr na rigada na gane duk abinda kike nufi, kar ki damu zan miki duk abin da kika ce, kin san dama ban da matsala da Dr. Noor tunda Aboki na ne, to sauran ma ba wahala bane tunda muna mutunci dasu, sai dai kuma gaskiya kafin nasan komi zan ja lokaci da yawa, sai dai mu riƙa bin komi a sannu a hankali”.

Washe baki Hajja tayi tace, “Na san da haka Doctor, Ni dai fata na Buri na ya cika, Miji na ko kaɗan ba ya kyauta min matsalan nan duk daga wurin sa yake, idan da ya saka Ni cikin su ai da ba haka ba, amma koda yake..”

Sai kuma tayi shiru tana jan numfashi, cike da takaici tace, “Dr zuwa gobe insha Allahu zan san yanda za’ayi kayan ka su shiga ciki, baka da matsala da wannan”.

Dariya yayi yace, “Na san haka Dr. Shiyasa tun farko na zaɓe ki, Allah dai ya cika mana burin mu gaba ɗaya”.

“Ameen Doctor”. Hajja Fatu tafaɗa tana murmusawa

Tashi yayi yace, “Let it be tomorrow,”

“Ok”. tace dashi tana miƙe wa

Sallama suka sake yi kafin ya fice

Ita kuma Files ɗin da Safna ta kawo mata ta ɗauka a ran ta tana ƙorafin mijin nata, sam bata so kawo mata aikin nan da yayi ba tunda lokacin tashin ta yayi, tsaki taja ta ɗau abinda zata ɗauka ta fice.
[5/25, 7:57 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
             FAMILY DOCTORS
                         ????
????????????????????????????????????????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button