NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Murmushi tayi kawai ba tare da tayi tunanin matsa masa akan sanin meyasaka be son sanar mata ba? Ita a komi nata tana ma mutum uzuri maybe yana da dalilin hakan ne

“To yaya na gane, but hurry up and tell her because soon Kaka will start talking about your marriage, kuma ka ga idan baka sanar mata ba za’ayi babu kai haka zakai ta zama a Gwauron ka”.

Baffa laughed and said, “Well shikenan my sister, but ni nafi son nayi aure lokacin da kema za kiyi”.

Zaro idanu tayi tace, “Yaya baka shirya auren ba kenan? Because I don’t have a real boyfriend.”

“Hmm you’re just saying, duk da ban taɓa ganin kin kawo kowa gida ba amma fa ina da tabbacin kina da masoyi don kuwa irin ki ba su rasa masoya”.

Shiru kawai tayi a wannan karon tana murmusawa, sai kuma ta duƙar da kanta tana ci gaba da juya spoon ɗin hannun ta cikin abincin

“Talk to us My dear, when will you show me my son-in-law?”

Ɗago kai tayi tana kallon sa tace, “Yaya Ni bani da gwani har yanzu, amma dai ka taya ni da addu’a”.

Sanyi yaji cikin ransa, cike da nuna tausayawan sa a fuska yace, “My dear Sister, I promise to help you. I pray to God to bless a good husband who loves you so much, kuma Allah yasa nan kusa za kiyi aure baza kiyi nesa damu ba”.

Dariya tayi cike da farin ciki tace, “kamar ka sani Yayana ko kaɗan ba na Son auren nesa sabida ba na Son nayi nesa da ku, sannan ba na son na dena aiki a hospital ɗin mu, Burina yana da nasaba da aiki cikin Hospital ɗin mu, ka ga kuwa ba na so na zama kamar Aunty Zulaiha da tabar aiki lokaci ƙanƙani, tayi nisa babu daman ci gaban ta a nan, nima ina so ayi alfahari dani cikin Family na; ya kasance ina ba da tawa gudunmawa wajen haɓɓaka shi”.

Filled with her love Baffa said, “God fulfill your dream My dear sister”.

“Ameen my brother, we should hurry back because my waking time is near, and I want to check on my patients.”

“To sarkin aiki ba kya gajiya?”

Murmushi tayi kawai tana ɗaukan Holandia tana sha, bayan ta gama ta’ajiye tana kallon sa tace,”Come on, I’m full.”

Ɓa ta fuska yayi yana kallon abincin gaban ta yace, “Baki ci da yawa ba ai?”

Marairaice fuskar ta tayi tace, “Yaya na ƙoshi ne”.

“Ok to tashi muje nima na ƙoshi tunda kin ƙoshi”.

      Sai da ya biya kuɗin sannan suka fito suka shige cikin motan yaja suka nufi Hospital ɗin

Suna shiga haraban Hospital ɗin suka fito ya rufe motan suka jera suka nufin cikin asibitin

A reception Ɗahira ta hango aunty Zainab, tayi saurin zuwa wajen ta tana cewa, “Aunty Zainab”.

Juyo wa Aunty Zainab tayi tana kallon ta sai ta faɗaɗa fara’an ta tana faɗin “a’a! my sister. I have been asking Fadila Ni kam ban ganki ba tunda kuka fara aiki”.

Dariya Ɗahira tayi tana cewa, “wlh kuwa Aunty nayi ninyan zuwa har Office ɗin ki, to, aiki yayi yawa I don’t have time.”

Aunty Zainab kallon Baffa da ya ƙariso wajen su ya tsaya yana kallon su tayi tace, “oh ka ga masoya! ina kuma kuka je?”

Ɗahira kallon Baffa tayi suka haɗa idanu, sai ta saki dariya tana mayar da idanun ta kan Aunty Zainab tace, “aunty kenan abinci fa muka je ci da Yaya”.

Smiling, Aunty Zainab said, “Hmm Na ga alam ai”.

Baffa dake faman shafa kansa yace, “kin ji ABU da wata magana don mun fita da ƙanwata za kiyi mana fassara daban?”.

Ɗan waro ido tayi tace, “wai laifi ne don nace masoya kaji min yara?”

Yanda tayi maganar yasa su dariya gaba ɗaya

Still Ɗahira na dariyan tace, “Where’s Jinior?”

“Shigo wa ta kenan itama Fadila ta shigo shi ne ta’amshe shi”.

Baffa kallon Ɗahira yayi yace, “mu je kin ji My sister Kar mu biye mata”.

Hararan sa Aunty Zainab tayi tace, “to babu inda zata je.. kaje kai”.

Shima hararan ta yayi yana cewa, “ke fa kina son raina ni fa, wai ba tare kika gan mu ba?”

“Eh tare na gan ku amma aiken ta zanyi”.

Kafin yayi magana Ɗahira tayi saurin cewa, “Yaya ka je zan zo har Office ɗin ka”.

Gyaɗa mata kai kawai yayi jin wayan sa na ringing, zaro wayan yayi cikin aljihu yana yin gaba abin sa bayan ya ɗaga mata hannu alamun ya tafi

“Hmm Ni dai ina mamakin wannan shaƙuwa na ku, anya.. anya..”?

Ƙwalalo idanun ta Ɗahira tayi tana kallon ta tace, “kai Aunty babu daman Yaya ya nuna wa ƙanwar sa kula wa sai da wani abun? Ni fa na ce miki abinci muka je ci”.

“To ai nima ba fitar da kuka yi bane nake magana, mu je kawai”. Aunty Zainab ɗin taƙarike maganar ta tana yin gaba

Ɗahira tabi bayan ta suna sauya hiran su

Office ɗin Aunty Zainab ɗin suka shiga, bayan sun zauna ta ɗauko mata wasu files ta miƙa mata

“Ga shi don Allah Ɗahira, ki kai wa Dr. Said don ba na son ya sake damu na”.

Amsar files ɗin Ɗahira tayi tana kallon ta tace, “Aunty who is Dr. Said?”

“Aff baki san shi ba ashe, yana nan office ɗin sa na kallon nan wajen ta hannun dama”.

“Ok sai na sake zuwa kenan Aunty?” Tafaɗa tana miƙewa tsaye

Murmushi Aunty Zainab tayi tace, “Tom My Sister, ki gaishe dasu Kakus me ran ƙarfe”.

Dariya tayi tace, “insha Allah zai ji”.

Daga haka ta fice bayan sun sake sallama.

        Tana fita kamar yanda Aunty Zainab tace mata hakan tayi ta nufi hannun daman ta, tana zuwa ta soma dudduba sunayen Offices ɗin, nan kuwa taci karo da sunan sa a saman nashi Office ɗin, Nocking ta soma yi

Dr. Said dake zaune yana ma wata budurwa bayani yayi saurin ɗago kansa cike da fargaba, kallon Budurwan yayi yace, “Yi maza ki kwashe magungunan nan ki saka a jaka”.

Babu musu kuwa ta kwashe ta zuba a jakan ta

Shi kuma ya gyara zaman sa yana rufe Files ɗin dake gaban sa tare da kifa wa sannan ya ba da umarnin shigowa

Turo ƙofan Ɗahira tayi da sallama ta shigo

Idanun sa ƙyar a kan ta ya’amsa mata sallaman yana kallon ta, duk da be santa ba amma ya ga tana masa kama da Familyn Dr. Al’ameen

Ita kuwa ƙariso wa wajen Table ɗin sa tayi ta miƙa masa files ɗin tace, “ga shi Aunty Zainab ta ce in kawo maka”.

Sai a lokacin ya ɗan saki fuskar sa yana bin ta da wani irin kallo, cike da murmushi a face ɗin sa ya miƙa hannu ya’amsa yace, “Ok thanks”.

Juya wa kawai tayi ta fice ba tare da ta kalli ko budurwan dake zaune ba

Har ta fice yana kallon ta cike da tsananin burge sa da tayi, sosai Ɗahira ta ɗauke masa hankali da kyawun ta da cikan halittan ta, musamman ma da take siririyan mace, domin yana ƙaunar irin su. sai faman doka murmushi yake yi ya kasa ɗauke kai daga ƙofan da ta fice

Sai da budurwan nan ta buga table kafin ya dawo hayyacin sa

Ɗan shafa kan sa yayi yana kallon ta kafin yace, “kin tabbatar cikin nan be wuce 5 Months ba?”

Kallon sa tayi a yatsine kafin tace, “Dr. Na rigada na faɗa maka wata 4 ne”.

“Ok bari in zo”.

Miƙe wa yayi ya nufi wani dogon sip ya buɗe, ya soma bincika kayan aikin da zai yi mata amfani wajen cire mata cikin.

         Wannan shi ne halayyan Dr. Said, yana cire wa ƴan mata ciki ba tare da sanin kowa a cikin a sibitin ba, domin doka ne idan har aka kama ka kana irin wannan cin amanar za’a kore ka, asibitin kwata-kwata basu yarda da aikata wannan zunubin ba.

                 ⚫⚫⚫

     Ɗahira sai da ta koma Office ɗin ta tayi sallah kafin taje ta ƙara duba patients ɗin ta, tana dawowa ta haɗa komi nata da abinda zata buƙata ta fito ta rufe office ɗin

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button