NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Sunkuyar da kanta Ɗahira tayi don bata san me zata ce mata ba

“Ina magana kin yi shiru, meyasa zaki zauna ki saka damuwa a ranki har kiyi irin wannan kukan da ya haddasa miki ciwo? Bayan kin san halin kanki abu kaɗan ne yake haddasa miki ciwo idan kin saka damuwa?”.

Matso hawaye Ɗahira tayi, har yanzu ta kasa yin magana tunda bata san yanda za’a yi ta faɗa ma Mahaifiyar nata matsalan ta ba

“Ko sabida ya ƙi zuwa ne kike kuka?”

Ɗaga mata kai tayi, kafin ta cire kunya ta sanar mata komi

Ajiyan zuciya Aunty Amarya ta sauke, cike da tausayin ɗiyar ta tace, “ki yi haƙuri haka Allah ya so dama ba shi ne wanda zaki aura ba, Allah ya musanya miki da wanda ya fi shi, amma ki dena saka damuwa a ranki kinji? ki fauwala wa Allah komi, ai Kakan ba cewa yayi zai zaɓa muku wani ba idan baku kawo wanda zaku aura ba, don haka ki dena saka maganar auren nan na damun ki”.

Gyaɗa mata kai tayi

Sai da ta sake tausan ta kafin ta fice ta bar ta

Sosai maganar Maman ta ya sanya ta jin sanyi a ranta, dama ita yanzu damuwar ta yanda kowa zai kai zaɓin sa, amma ita ban da ita.

      A haka ta saki jikin ta a ranan taci gaba da walwalan ta, sai dai bata je aiki ba ta bar wa gobe.
[6/4, 11:07 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
              FAMILY DOCTOR’S
                         ????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
   NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL.

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

        
????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

        EPISODE Twenty-Five

       Kamar yanda Hajja Fatu tace zata kira Hajiya Amina su yi magana, hakan kuwa tayi, sun gama ƙulle-ƙullen su a waya, kafin suka yi sallama akan zata turo Sa’adatu gobe-goben nan kamar yanda ta buƙata, yanzu ɗin ma don ba ta kusa ne da sun yi waya.

      Washe gari zuwa yamma sai ga Sa’adatu ta dira garin Kaduna

Hajja Fatu zuwa tayi har ɗakin Baffa ta tasa shi gaba akan “lallai-lallai sai ya je ya ɗauko Sa’adatu a airport”.

Ba da son ransa ba haka ya tashi ya saka riga a saman Singlet ɗin dake jikin sa, ya fito ya wuce ya shiga motar sa ya bar gidan, a cikin mota in banda tsaki da yake saki babu abinda yake yi, kaso mafi rinjaye na zuciyar sa yana ga Ɗahira, ya rasa meyasa zuciyar sa ta kasa nutsuwa da halin da ya saka ta, yana ji a jikin sa tabbas tana wani hali a sanadiyar Text ɗin da ya tura mata, amma ya zai yi? Bazai iya zuwa ya same ta ba, bazai iya jure ganin damuwa a kyakykyawar fuskar ta ba, ya gummaci ƙaurace mata har sanda komi zai dai-daita. Lumshe idanuwan sa yayi yana buɗe wa sai ga hawaye sun zubo masa a kunci, hannu ya saka ya share yana jan numfashi cike da takaicin Mahaifiyar sa, zuciyar sa sosai take mishi ƙunci fiye da tunanin mutum, yana ji a ransa bazai iya jure wa ba, bazai iya auren kowa ba face Ɗahira, dole ya sake yi wa mahaifiyar shi magana, ko zata iya tallafa wa rayuwar sa, Allah ya gani ba ya ƙaunar yarinyan nan da za’a liƙa masa, sannan kuma bazai iya zuwa ya tunkari wata ɗiya mace da sunan so ba, bare har ya iya auren ta, ita dai Ɗahiran da Hajja ba ta so ita zuciyar sa ke so..

     Be fasa tunanin sa ba har sanda ya dangana ga airport ɗin, tunda ya faka motan ya hange ta, sabida kasancewar ta doguwar mace, idan har ta tsaya cikin mutane nan da nan ake iya gane ta, ga ta fara kuma tana ƙara wa dana kanti

Ya ɓata lokaci cikin motan kafin yaja numfashi ya buɗe ya fito, yana hangen ta sai faman waige-waige take yi tana duba agogon dake ɗaure a tsintsiyan hannun ta. Lumshe idanu yayi ya sake buɗe wa a kanta, kamar bazai taka ya isa wajen ta ba, sai kuma ya daure cike da baƙin ciki ya nufe ta, fuskar sa babu ko alamun walwala

Sai da ya dangana ga inda take tsaye, sannan ne ta hange sa, ai nan ta saki murmushin da ya bayyana haƙoran ta, wanda da gani kasan tana cikin tsantsan farin ciki, kiran sunan sa tayi tun kafin ya ƙariso

Sai ya kau da kai yana sake ciccin magani, ya tsaya cak a wajen

Ɗaukar jakar ta tayi ta nufo sa tana sake washe baki, tana iso wa wajen sa ta soma gaishe sa cike da fara’a, amma yanda ya amsa mata ne sai walwalan ta ya ragu

“But yaya lafiya dai ko?” Tayi masa tambayar tana kallon sa

Be ce mata komi ba ya juya ya nufi motar sa

Sai ta tsaya kawai tana kallon sa baki sake, duk da ta san ba ya son ta amma ai suna mutunci sosai ba kamar yanda ya nuna mata haka ba, “so what’s wrong with him?” Tayi wa kanta tambayar har yanzu tana tsaye a inda take. Sai da taji horn ɗin motan sa kafin ta ankara, taja akwatin ta ta nufi motan, buɗe bayan tayi ta saka akwatin kafin ta shiga gaban motan ya ja suka bar wajen.

         A cikin motan ma babu abinda yace mata, duk da kuwa ta sake tambayar sa abinda ke damun sa, amma yayi mata banza, har suka kai gidan ya sauke ta yaja motar sa ya bar gidan

Tsaye tayi a wajen tana bin motar har ya ɓace wa ganin ta, sai kuma jiki a sanyaye taja Trolly ɗin ta tayi cikin gidan, duk wanda ta gani a hanya gaishe sa take yi har ta isa Part ɗin Hajja Fatu

Sosai Hajja Fatu tayi murna da ganin ta, nan tayi ta nan-nan da ita har ta cika mata gaban ta da kayan ciye-ciye

Ruwa kawai ta ɗauka tasha, sannan ta kalli Hajja Fatu tace, “Hajja where is Shakira I didn’t hear her movements?”.

“Ai kuwa Shakira tana wajen Yusra, amma yanzu zaki ga ta zo tunda ta san an tafi ɗauko ki”.

Gyaɗa kai Sa’adatu tayi, kafin ta sake cewa, “Hajja is something happened to Yaya Baffa? na ga tunda muka zo be ce min komi ba ne?”

Murmushin yaƙe Hajja tayi tace, “bar shi nan yanda kika ganshi, shi ya san me ke damun shi”.

Langaɓe fuska tayi tace, “eyya Hajja taya zan bar shi bazan damu ba? kinga fa shi ɗin Yayana ne, wlh baki ga tunda muka biyo hanya duk na gama damuwa da halin da na ganshi, ko dai Ni ce ba ya son gani?”.

Hajja tace, “Taya Zaki ce haka? Ina ruwan shi dake da zai ce ba ya son ganin ki? Kin San tunda nayi masa maganar bazai auri yarinyan da ya zaɓa bane, shi ne ya dena min magana, ko abinci ma ba ya ci a nan, ya dena walwala gaba ɗaya, Ni kuwa bazan yarda ya aure ta ba bayan ga ki kina son shi, muddin idan be kawo wacce yake so ba, to ke ce matar sa da yardan Allah kamar yanda muka tsara”.

Washe baki Sa’adatu tayi, cike da farin ciki tace, “Allah ya amsa bakin ki Hajja ta. Amma to wace ce wacce ya ke so ɗin?”.

“Kar ki damu ba sai kin san ta ba, don ba na son ma maganar tariƙa tsawo azo kuma a samu matsala, maganar ta faɗa kunnen wani”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button