NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Big Dady yace, “a’a barta kawai ta zauna”.

Murmushi Ɗahira tayi tana kallon Big Dad tace, “bari dai inje in dawo Dady, because I have some things to do”.

“Well shikenan Daughter”.

Daga nan fita tayi ta rufo musu ƙofa, She did not go back to the General Parlor. Sai tabi ta wani Corridor da zai sada ta da Part ɗin su, tana cikin tafiya ta hangi Baffa ya taho shima ɗin, yayi shigan nan nasa na ɗamewa irin shigan wizaye, kansa babu hula sai kwantaccen gashin kansa da ya sha askin zamani, sosai yayi masa kyau ya sake fito da kyawun sa ainun, hannun sa Sigari ne yake sha, shima yana hango ta ya matse Sigarin a hannun sa ya kashe kana ya tura shi cikin aljihu

Murmushi ya saki lokacin da ya’iso wajen ta yana faɗin “Oyoyo My Lovely sister”. Ya nufe ta da ninyan Hugging ɗin ta

Tayi saurin ja da baya tana murmusawa tace, “Oyoyo My Lovely Brother”.

Sai ya ɓata fuska and looked at her and said, “Why don’t you let me hug you?”

Still tana murmusawa tace, “ka san ba na so fa”.

Ɗage kafaɗa yayi yana cewa, “ok to ya Hanya? kin dawo ko ki neme Ni, kinsan nayi missing ɗin ki sosai”.

Ɗan huro hanci tayi tana kallon sa, sai kuma ta ɓata fuska tace, “Ya Baffa kamar warin Sigari nake ji?”

Waro idanu yayi yace, “Really?”

Sai ta harare sa tana cewa, “Where is our promise?”

He smiled and touched his forehead and said, “Sorry Sis ban saɓa miki ba ai”.

“I don’t agree, ga shi kana bani haƙuri”.

“Da gaske my Sister na Dena sha, sai dai idan hancin ki ya juyo miki wani warin daban”.

Kallon sa kawai take yi, sai kuma tace, “ok I Believe You”.

He smiled and said, “so where are you now?”

“I’ll go back to our Part”.

“Mu je ki taya ni hira mana”.

Girgiza kanta tayi tace, “No grave until tomorrow, now I have something to do.”

Baffa haɗe hannayen sa yayi yana kallon ta yace, “Please Mana my sis”.

Ɗahira ɗan kawar da kanta tayi

ya sake cewa, “Please kinji?”

“Ok Muje”.

Murmushi ya sakar mata yace, “yauwa ko ke fa”.

Itama murmushin tayi tabi bayan sa suka jera suka nufi cikin gidan.

Suna shiga cikin ɗakin sa tabi ɗakin da kallo tana yamutsa fuska, sai kuma ta kalle sa tace, “Wai Ya Baffa kwana nawa ɗakin nan be ga shara ba?”

Shafo kansa yayi yana kallon ta shima yace, “wlh kin san ban da lokaci kuma ga shi ke kinje anguwa, and na saka Shakira ita kuma kin san halin ta ba wani iyawa tayi ba”

Gyaɗa kanta tayi kana tace, “ok bari in gyara maka yanzu ko”.

“Ok my sis let me help you”.

Zuwa tayi ta soma kakkaɓe gadon yana tayata suna hira, bayan sun gama suka share ɗakin tare da wanke Toilet ɗin ɗakin, ita tayi Moping shi kuma ya koma kan sofa ya zauna yana latsa wayan sa

Bayan ta gama ta dawo kan hannun kujeran ta zauna tana kallon sa tace, “Yaya na gama maka bari in wuce sashin mu kar Mama taji ni shiru”.

Ok my sister, Thank you so much, that’s why I love you so much coz you are so kind”.

She smiled and said, “Yayana kenan! I love you more than anyone else in this house. Kaima kana da kirki.”

Tashi tayi tana nufan saman drower ta ɗau wayan ta tadawo tana kallon sa da shima ya kafe ta da nashi idanun, murmushi tayi masa tace, “Na tafi Yaya”.

Miƙewa yayi ya rako ta har bakin ƙofa kana ya koma ciki yana zama saman kujera tare da aza kansa ya kwantar kan hannun yana lumshe idanun sa, murmushi kawai yake saki yana tuna ɗan kyakykyawar fuskarta, sosai yake matuƙar son ƙanwar tasa, kuma so na aure, burin sa kawai a rayuwa yaga ranan da zai mallaki Ɗahira a matsayin matar sa domin tayi masa tako ina, sai dai har yanzu ya kasa samun ƙwarin gwiwar tunkaran ta yace mata yana son ta

Ɗahira tana da wani irin kwarjini da zai yi wuya namiji ya tunkare ta da zancen so, shiyasaka tun tasowan ta bata taɓa yin saurayi ba duk da tana da farin jini sosai na mutane, a lokacin da suka je ABU Zaria karatun su na Degree yawancin Friends ɗin ta maza ne, kuma duk acikin su babu wanda ba so yake kawo sa wajenta ba but basu iya gaya mata.

Shima haka Baffa ya daɗe yana ƙaunar ta yana dakon son ta Amma har yanzu be iya sanar da ita ba, kuma duk abinda tace “yayi ko ya bari” yana bari, shi ɗin ma’abocin shan Sigari ne don wani lokacin har Alcohol yake korawa, amma babu wanda ya sani a gidan sai ita kaɗai kasancewar tana yawan zuwa ɗakin sa koda ba ya nan, wani lokacin sai tazo ta kwanta tayi barcin ta, yawan kusancin su dashi ne ya saka tasan wannan sirrin nasa, kuma tun sanda tace ya dena sha ya dena, sai dai har yanzu Sigari ne be dena gaba ɗaya ba, amma idan har zata gani zai yi ƙoƙarin ɓoyewa.

        WASHE GARI

         Ranan ne ya kasance ranan Walima, kowa idan ka gani agidan cikin farin ciki yake, sosai gidan ya sake cika sai hada-hada ake yi, har mutanen Maiduguri tushen su kenan duk sun hallaro, duk girman gidan nan sai da aka cika sa da mutane

Ƙarfe 02:00pm. Aka soma tafiya AL’AMEEN FAMILY HOSPITAL kasancewar acan ne za’ayi taron, haka motoci manya-manya suke ta jidan mutane suna kai su.

Kar ku manta da
Share
Comments
Vote
Like.
[5/21, 9:54 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

NATSUWA A SALLAH
Manzon Allah mai tsira da aminci, ya ce, “sallah ba kome ba ce illa miƙa wuya da tawali’u…” Kuma ya ƙara da cewa, “Bawa bai samun ladan sallar sa sai gwargwadon abinda ya hankalta daga sallar.” Watau, gwargwadon natsuwar mutum cikin sallah gwargwadon darajar da yake samu gun Allah. Don haka ne ma ma’aikin Allah ya ce, “Allah ba ya juya wa Bawa baya yana cikin sallah matuƙar bai waiwaya ba; idan ya waiwaya kuwa, sai Allah ya bijire masa.”
Babu abin da yake kawo waiwayo cikin sallah kuwa sai gafalar Bawa da muƙamin Ubangijin sa, watau ya zama tamkar wanda ya tsaya yana ganawa da Ubangijin sa alhali zuciyar sa tana shagale da wani abin dabam. A kan wannan matsala ne Allah yake ce wa Manzon sa, da al’ummar sa ma, a cikin suratul A’ARAF aya ta 205:
“Kada ka kasance daga gafalallu.”
In muka lura sai mu ga cewa ta ya ya kuwa gafalalle zai iya tunawa da muƙamin Ubangijin sa yana cikin wannan hali na rashin kula har wani abin tsoro ya auku? Bugu da ƙari, daman can ga shi Allah ya yi umarni a cikin suratul Ɗ.H., aya ta 14 da cewa:
“Kuma ka tsayar da Sallah domin tuna Ni”.
In mutum ya Yi haka, ana fata ya rabban ta.
   Allah yasa mu dace.

  *EPISODE four*

    Babban haraban asibitin cike yake da mutane bila adadin, mutane ne kamar tsaki kama daga yara manya masu kuɗi da manyan likitoci duk an gayyace su, har ta da gwamna Malam Nasiru El Rufa’i sai da aka gayyace shi wajen, komi ana yinsa ne akan tsari gunun sha’awa

Ɗahira, Shakira, Yusra da Fadila can na hango su wajen zaman su daban, sosai su kayi kyau cikin shigan su na material fari ƙal da akayi masa ɗige-ɗigen Coffee colour, ɗinkin doguwan riga akayi musu fitted, sai suka yane kan su da Goldeen Veil tare da sanya Hill shoes shima Golden, sosai su kayi matuƙar kyau kamar ka sace su ka gudu sai faman haskawa suke yi kamar taurari

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button