NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

“Abban Baffa, I am talking and you are listening because you have made Me nothing.” Maganar ta takatse masa tunanin sa

Still murmushin yayi yace, “kin fiye rigima ke kam Hajjaju, kin ga na nemi taimakon ki ne? Meyasaka baza ki ji da naki aikin ba? Ko da ma abinda ya shafi aikin asibiti ne ai ba ɓangaren mu ɗaya ba bare ki taya ni, ki je abun ki na gode”.

A fusace Hajja Fatu take kallon sa, cikin takaici da halin mijin nata da har yanzu ya ƙi ya gane tace, “haka kace ko Alhaji? Well shikenan God help”.

Da gama maganar; ta miƙe ta nufi ƙofa don ficewa, duk da har aranta ta nuna masa fushin ta ne don ta san halin sa zai iya dawowa da ita, daga nan ma ya faɗa mata abinda yake yi, ita kuma ta samu damar shiga jikin sa har tasan sirrin komi nasu

Amma kuma ga mamakin ta har ta buɗe ƙofan be ce mata komi ba, ɗan juyo wa tayi ta kalle sa sai taga aikin sa ma yaci gaba dayi tamkar ma be san da ita wajen ba, hakan ya ƙara tunzura ta; ta fice tana bugo ƙofan cike da tsantsan takaici

Murmushi Abba yayi yana bin ƙofan da kallo, kana ya girgiza kansa yana maida kansa yaci gaba da abinda ke gaban sa.

      Fitowan Hajja Fatu itama Shakira ta fito a ɗakin ta, kallon Mahaifiyar nata tayi cike da nazarin ta kafin kuma tace, “Lafiya Hajja me ya faru ne?”

Huro hanci tayi tana ɗaga idanun ta ta sauke kan Shakiran dake tsaye tana jiran amsar nata tace, “It’s me and your father. Let’s talk about it tomorrow. I’m not feeling well. What are you doing here?” Ta sauya maganar da tambayan ta

Shakira tace, “I just came out to drink water, har na fara barci ishin ruwa ya tado ni”.

Bata ce mata komi ba ta nufi ɗakin ta tabuɗe ta shige

Da kallo Shakira tabi ta dashi, har sai da ta shige kafin ta janye idanun ta tanufi bakin Fridge, buɗe wa tayi ta ciro goran ruwa tasha sosai, sannan ta mayar ta rufe ta koma ɗakin ta.

.

plz I don’t get a lot of comments, if you don’t like it please tell me in Dena, don ba nan kaɗai nake yi ba, can da suka fi buƙata sai in riƙa musu su kaɗai, ta comments ɗin ku kawai zan san kuna so aci gaba.

kar ku manta Vote and share.
[5/29, 8:48 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
              FAMILY DOCTOR’S
                         ????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
   NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL.

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT ????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

???????????????????? ???????????????????????? ????????✍️

????????????????????????????: ????????????????????????????????????????????????

        
????????????????????????????????????????
???????? ???????????????????????????????? ???????? ???????????????????????? ???????? ???????????????? ɗ????????????. ????????????????’???? ????????????????????????.

        EPISODE Twenty

      Da sannu rayuwa taci gaba da gudana, zuwa wannan lokacin Familyn Dr. Al’ameen suna ta shirye-shiryen zuwa Kano ne Bikin Salma (Ƴar Hajiya Laila), yanzu haka saura wata ɗaya

Kaka da kansa ya ba da odan kaya ya raba musu, wai wanda zasu ci biki dashi, matan kaɗai, daga iyaye har ƴan matan, har da su Aunty Zainab da Aunty Zulaiha sai da ya saka aka aika musu dashi, kala bibbiyu ne atamfa da Swiss less, kuɗin su kuwa zai kai dubu ɗari ko wanne, daga gani kasan kayan masu uban tsada ne, sun yi murna matuƙa, nan da nan kowa yakai ɗinki inda zai iya kai wa

Kafin ranan bikin kuwa tuni an amso musu, ranan Alhamis ƴan matan suka shirya tafiya, matan gidan kuma sai gobe juma’a za su taho, su kuma su Big Dady ranan ɗaurin auren asabar za su je, gaba ɗaya har dasu Usman, sannan kuma su dawo a ranan.

       Tun 11:00am. Suka gama shirin su, ko wacce da jakan ta a hannu, har haraban gidan iyayen su mata suka rako su

Drever ya amsa jakunan nasu ya saka a bayan mota

Yusra ce ta shiga gaba, su kuma su uku a baya, drever’n yaja motan suka ɗau hanya cike da ɗoki

To dama ba wai sun saba zuwa sosai bane, kasancewar Boarding school suka yi a A.B.U Zaria, shiyasa ba su da lokacin kansu bare su riƙa ziyarce-ziyarcen ƴan uwa, kuma suna gamawa suka soma aiki, wannan dalilin ne yasa sun daɗe rabon da su je Kano, gwara-gwara ma Katsina, hutun ƙarshe da suka samu kafin su gama school a can suka yi, sai kuma suka ƙarisa sauran a Maiduguri, Kano ne dai sun shafe kusan shekaru biyar rabon da su je.

         Zuwa ƙarfe 02:00pm. Tayi musu a Kano, Direct family house ɗin General Isah Basheer Isah (Walid) suka nufa, wanda a yanzu ake kiran sa da Granny

Gate aka wangale musu drever yaja motan zuwa ciki, be tsaya ba sai a ɓangaren su Salma, kasancewar gidan babba ne me Part-part, da ƴaƴan sa guda hudu maza da jikokin sa waɗanda suka yi aure su wajen uku duk a cikin gidan suke da zama, kuma kowa da na shi Part ɗin, sai na Granny ɗin da matar sa da suke ce mata INNA Haja.

     Tun kafin ma su fito daga motan su Salma suka fito tarban su, dayake sun san da zuwan su, ƴan mata ne kusan su goma kuma duk jikokin Granny ne, a ciki har da ƴaƴan yaran sa mata da sukai aure a wani wajen

Sai kuma Shamsiyya da itama tazo tun jiya

Nan da nan suka karaɗe ɓangaren da murna da ihun ganin juna, daga baya kuma suka ɗunguma zuwa ciki

Hajiya Laila na zaune a parlour’n ta tana jiran isowar su, ganin su yasa ta washe bakin ta kafin ta fara musu maraba

Gaba ɗaya wajen ta suka isa suna gaishe ta cike da tsananin farin ciki a fuskokin su

Bayan sun gama gaishe-gaishen ne ta tashi taba su waje, nan kuwa suka ƙara ɓarke wa da Surutu ana hiran yaushe gamo, Sarkin surutu Firdausi tuni ta soma zuba ko haɗiye miyau ba tayi, tana ɗire aya take ɗaukan wani

Yau har da Fadila ba’a bar ta a baya ba, domin tayi zaman ta cikin ƴan uwa ana ta hiran da ita

Sai daga baya ne ma da Hajiya Lailan ta fito, take musu tsiya “ko abinci basu ci ba sun zauna suna ta zuba zance”

Salma ita da su Shamsiyya suka tashi suka haɗo musu abincin, duk sun baje a parlour’n suna ci suna ci gaba da hiran su cike da nishaɗi.

      Ƴaƴan Hajiya Lailan ne guda biyu maza, Bashir (Abba) da kuma Yaseer suka shigo cikin parlour’n, yanzu haka ko wannen su da iyalan sa, shi Abban ne babban jikan gidan

Gaishe su suka yi cikin girmamawa, su ma suka amsa cike da fara’a da nuna farin cikin su na ganin su, har da tambayan su Baffa da Usman tare da sauran ƴan gida, duk suka amsa musu da “lafiya lau sun ce a gaishe su,” daga nan suka wuce ɗakin Mahaifiyar su suka bar su nan suna ci gaba da hiran su

Ɗahira ce ta kalli Fardausi da ta cika su da Surutu, don ita ce ma ƙarfin hiran, cikin tsokana take ce mata, “Ni wlh da an haɗa ku gaba ɗaya Dady ya aurar daku, ko gidan ma sun huta da surutun ki, yarinya ko haɗiye yawu ba ta yi”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button