NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

“Fodio, why did you break my wife’s phone?”

Shiru yayi batare da ya ɗago kan sa ba, kuma be dena latsa wayan ba

“Kai ba magana ake maka ba? Are you crazy? Uban meyasa ka fasa mata waya? Ka dawo kenan zaka soma takura mata ko?” Big Dady yayi maganar a zafafe yana kallon sa

Sai a lokacin ne Usman ya ɗago kai fuskar nan a ɗaure yana kallon su, sai dai be iya cewa komi ba

Abba yace, “miƙo wayan mu gani uwata”.

Miƙa masa wayan tayi, ya’amsa yana juyawa sai ya ɗago yana kallon ta yace, “Agarin ya yafasa miki wayan?”

“Mun yi karo ne shine ya faɗi, da nayi masa magana shi ne ya dawo ya tattaka min da takalmin sa”.

“It’s your fault, why did you talk to him then? Stop following her shit please”. Abbu yayi maganar yana amsan wayan daga hannun Abba and put it aside

Big Dady said, “why doesn’t she talk and break her phone?”

Sai kuma ya mayar da kallon sa ga Usman ɗin yace, “Make sure you buy her her phone and pay for it, idan ba haka ba zan mummunan saɓa maka kana jina ko?”

Gyaɗa kan sa kawai Usman yayi yana kallon Ɗahira da kanta ke ƙasa, kawai tunani yake yi a ransa abinda zai yi mata idan har ta shigo hannun sa

Kaka ne yace, “ya isa haka Lawal (Noor), karka ɗau abinda zafi haka mana, yanzu mu mayar da hankali kan abinda ya tara mu. Alhmadulillah and Allah show us this time to see my grandchildren finish their studies and become doctors now, don haka na tara ku in sanar muku da Albishir da na tanadar muku”.

Murmushi yayi yana kallon su ɗaya bayan ɗaya kana yaci gaba da cewa, “Zuwa nan da Sunday motocin ku da na siya muku za su iso sai kowa ya zaɓi wanda yake so, wannan shi ne kyauta na a gare ku, sannan ina jan hankalin ku ku mayar da hankali wajen aikin ku, abinda ya kai ku shi za kuyi ba na son wasa,
May God help you all. May God bless you.”

Duk ka parlour’n suka amsa da ameen ban da Usman da har yanzu latsa wayan sa yake yi, nan ɗaya bayan ɗaya suka yi ta mishi godiya kana ya kalli Usman yace

“Kai kuma Fodio, the opportunity I have given you is enough. dole ne ka dawo Nigeria kaci gaba da aiki a asibitin mu, domin baza mu zira idanu ace kana can kana ma Nasara aiki suna ƙaruwa mu nan ka bar mu haka ba”.

Usman da ya ɗago kansa yana kallon Kaka, a karo na farko yace, “wai Kaka meyasaka kake son takura min ne? I don’t want to work here. I want to..”

Be dire maganar ba Big Dady ya daka masa tsawa, hakan yasaka shi yin shiru yana kawar da kai still fuskan sa ba walwala

“Umarni ake baka ba shawara ba ka ajiye aiki ka dawo nan kaci gaba, karka sake mu ƙara ja’inja da kai”. Big Dady ya faɗi maganar da kakkausar murya

Murmushi Kaka yayi yace, “ka bar shi nace Lawal; ba na son kana nuna masa zafi, ai ba cewa yayi bazai dawo ba, abi shi a sannu, kowa zai iya tafiya. idan kuma da me magana ko ƙorafi akan wani abu sai yayi magana”.

Kafin Kaka ya rufe baki Usman yayi saurin tashi ya fice, haka sauran ma su kayi ta tatashi suna ficewa ya rage daga Kaka sai su Big Dady

               *

      Hajja Fatu ce ta shigo parlour’n Hajiya da sallama

Hajiya wacce ke zaune a parlour ta’amsa mata sallaman sannan tayi mata maraba

Zama Hajja Fatu tayi tana kallon Hajiya da murmushi a face ɗin ta tace, “Oh ashe haka abu ya faru? Na zo miki jajen abinda Ɗahira tayi wa Usman ne, gaskiya bata kyauta ba”.

Hajiya tace, “Haka ne. amma shima da laifin sa ai, da be taka mata wayan ba baza ta kawo ƙarar sa ba”.

Ɗan taɓe baki Hajja Fatu tayi tace, “eh Haka ne kamar yanda ki kace, amma abinda tayi ai be kamata ba, wannan ai kamar tana so ta haɗa Ɗa da uba ne, ko ba kya ganin yanda Mahaifin sa ya nuna fushi dashi? Kuma da ba haka yake nuna masa ba, don Ni kai na shaida ce wajen ƙaunar da yake masa, amma a kan ta ya rufe idanu ya suburbuɗa masa faɗa a gaban ƙannin sa, wannan abun ba yi bane, idan ma uwarta take zugo ta ai zamu gani”.

Shiru Hajiya tayi tana sauraron maganganun Hajja Fatu, kuma da alamun sosai zancen yake shigan ta duba da yanda fuskarta ta sauya, domin abinda aka yi wa ɗan nata dama be mata daɗi ba, amma kuma maganganun Hajja ya sake saka ta taji haushi matuƙa

Ita kuwa Hajja Fatu ganin haka ya saka ta sakin wani shu’umin murmushi tana cewa, “Ai sai haƙuri amma dai na san yarinyan nan yanzu hure mata kunne ake yi, ada ai ba ta yin haka duk kuwa da cewa yana dukan ta, amma yanzu tunda ana son haɗa sa da ubansa ai an koya mata yanda zata riƙa kawo ƙarar sa, kin ga hakan zai sa Mahaifin sa ya riƙa fushi dashi”.

Hajiya kallon Hajja Fatu tayi don da alamun kalaman nata sun gama ratsa ta sosai tace, “nima naga alamun haka Hajja, sai dai ko ma wa ya koya mata da duk abinda suke nufi da ɗana sai dai ya koma kan su, babu wanda ya’isa ya shiga tsakanin ɗana da mahaifin sa, dole ne ma in ja masa kunne babu ruwan sa da ita tun wuri ya fita harkan ta, ba na son abinda zai saka mu sami saɓani, domin akan ɗana babu abinda bazan iyaba, kowa ya san da cewa ina matuƙar ƙaunar sa; don zan iya yin komi akan sa”.

Ajiyan zuciya Hajja Fatu ta saki tana kallon Hajiyan da alamun nuna damuwa a fuskarta tace, “gaskiya ne Hajiya, gwara dai ayi wa tufkan hanci tun kafin magana tasha banban, Allah ya kyauta gaba to, Ni bari in tashi na tafi”.

“To shikenan Nagode sai nima na leƙo”. Cewar Hajiya da murmushi a fuskarta

Tashi Hajja tayi ta nufi ƙofa ta fice tare da barin Hajiya cikin tunani. Tana fita ta saki wani shu’umin murmushi fuskarta cike da farin ciki, dama abinda take so kenan kuma tana ganin da alamu tarkon ta ya fara kamawa, taku ɗaya zuwa biyu tayi ta tsaya tana juyowa ta kalli ƙofar parlour’n Hajiya, a fili ta furta

“Now the game has started. If I am Hajja Fatu, I will open the heart of everyone in the house. I will make everyone hate you, A’ishah. tare da ƴarkin da kika ƙwallafa rai a kan ta, zan maye gurbin zuciyar kowa da ƙauna ta a ran shi, zaki san kin shigo cikin Familyn da ba na ki ba, mu zuba dani dake..”

“Hajja ke da wace ce zaku zuba? Me tayi miki?”

Da sauri Hajja ta juyo tana kallon ta, wani irin bugawa zuciyar ta tayi, nan da nan tsoro da fargaba ya ɗarsu a cikin zuciyarta har bata san sanda ta fiddo idanu waje ba suna kallon kallo..

Hhhh to Fans shin wa kuke tunanin wacce Hajja ta gani haka har ta sorata ainun?

karku manta da Comments, domin comments ɗin ku shi ke saka na ƙara yawan post.
[5/21, 10:02 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT ????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

TUNATARWA
Manzon Allah mai tsira da aminci, ya yi mana bayani a kan sallah da abin da Bawa yake iya samu. Cewa ya yi, "Yana yiwuwa mutum ya kawo sallah ga baki ɗayan ta amma a ba shi lada wadda ba ta wuce sudusin ta ko ushurin ta ba." Abin da yasa haka kuwa shi ne  rashin nutsuwa cikin sallah.    Allah yasa mu dace.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button