NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Ita kuma ta’amsa tana dubawa, sai da ta gama dubawa sannan ta kalli Maman tace, “Mama to ya jikin nata tana samun sauƙi ko?”

“Ai alhmadulillah Dacta ba kamar jiya da safe ba, ta samu sauƙi sosai”.

Gyaɗa kai Ɗahira tayi tana rubutu cikin wani file, sai da ta gama ta matso kusa da yarinyan ta soma duba ta sannan ta ɗago tana kallon Maman tace, “Mama insha Allahu komi zai zo da sauƙi, idan ta farka sai ta soma amfani da ruwa me ɗumi ana mata tsarki, daga yau sai a soma mata amfani dashi ko yaushe insha Allahu komi zai zama normal”.

“To Dacta mun gode ƙwarai Allah ya saka da alheri”.

Murmushi Ɗahira tayi tace, “ameen Mama Babu komi ai, Allah Ubangiji ya bata lafiya”.

Mama ta’amsa da “ameen” tana sake mata godiya

Daga nan Ɗahira gadon gaba ta wuce, itama Yarinya ce budurwa, wata shirgegiyar mata take jinyar ta, sai dai yarinyan bata kai wancan shekaru ba don baza ta fi 13yrs ba

Bayan sun gaisa da matar ta tambaye ta jikin yarinyan

Matar cike da sanyin murya kamar za tayi kuka tace, “Doctor babu sauƙi wlh yarinyan nan tana shan wahala sosai, tun jiya farkawar ta biyu, kuma duk idan ta farka a firgice take tashi tai ta ihu tana surutai”.

Ɗahira da take bin yarinyan da kallo cike da tsananin tausayin ta ta juyo tana kallon Matar tace, “Mama ki kwantar da hankalin ki insha Allahu zan yi iya bakin ƙoƙari na wajen na ga ta samu lafiya, Allah zai saka mata duk wanda yayi mata wannan abun”.

Share hawayen ta matar tayi tace, “ameen Dactor na gode ƙwarai”.

Daga nan Ɗahira duba yarinyan ta soma yi, ta jima tana duba ta kafin ta saka mata ruwa tayi mata allura ta cikin ruwan sannan tayi mata sallama ta wuce

Sauran gadon ta nufa ta duba su su ma, sannan taje wasu Rooms ɗin, sai da ta gama ta koma Office ɗin ta.

           Tana shiga taga Baffa zaune yana kallon ta yana sakar mata murmushi

Itama murmushin tayi masa ta shigo ta nufi wajen zaman ta ta zauna, cikin muryan ta na yanga take cewa, “Yaya na yaushe ka shigo?”

“I Come in right now, what’s your job?”

“Alhmadulillah. How’s yours?”

Murmushi yayi yana shafa suman kansa yace, “uhmm sai godiyar Allah my Sister amma babu daɗi”.

Dariya Ɗahira tayi tana kallon sa tace, “kai kenan Yaya, kai da ka jima tsawon shekaru kana aiki kake faɗan haka ina ga Ni da jiya na soma? wlh Yaya da wahala sosai aikin nan duk na gaji”. Taƙarike maganar ta tana lanƙwashewa ajikin kujeran

Baffa dariya yayi yace, “oh my dear sister ke dai kawai ki ce ke raguwa ce, amma daga fara aiki kice kin soma gajiya?”.

Murmusawa kawai tayi tana ɗan lumshe idanuwan nata don tasan halin yayan nata tsokana yake ji, ita kuma ta gaji ko maganar ma  daƙyar take amsa masa

Baffa da ya tsare ta da idanun sa yana sakin murmushi me ƙara masa kyau yace, “sis Naga da alamun kin gaji tashi muje muci abinci”.

Shiru tayi tana ɗan tunani

Hakan ya saka Baffa yace, “Do you have a job?”

Girgiza masa kanta tayi tana miƙewa ta zare rigan aikin tace, “No let’s go”.

Tashi yayi shima cike da jindaɗi suka fito suka jera har wajen lifter, shiga suka yi yakai su downstairs, mota suka shiga suka bar cikin asibitin, babu nisa da Resturant ɗin da suka je.

More Comments more post????????‍♀️????????‍♀️????????‍♀️????????‍♀️
[5/23, 9:05 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
             FAMILY DOCTORS
                         ????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
  NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????
        

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

        EPISODE Eleven

       Bayan sun shiga sun zauna ne Baffa ya tambaye ta abinda take so?

and she answered, “Everything she wants to eat”.

And he ordered Jallof Rice da ferfesun Kayan ciki with some drinks

and they started eating.

Ɗahira ta kalle sa tana murmusawa tace, “How do you get used to coming to your GirlFriend’s restaurant like this?”

Sosai Baffa yayi dariya yana kallon ta yace,  “Why did you say that?”

“Uhmm only”.

Murmushi yayi a wannan karon yace, “ke dai ki faɗa abinda ke zuciyar ki”.

Maƙe kafaɗa tayi cike da yauƙin muryan ta tace, “Yaya Ni dai nasan kana min rowan ta ne shiyasa ma baka taɓa nuna min ita ba ko da a hoto ne, but nasan dai kuna fita irin wajen shaƙatawan nan”.

Baffa kallon ta kawai yake yi cike da burgewa, ji yake yi aran sa tamkar yace, “ke ce macen da na taɓa so a RAYUWATA, sai kuma ya girgiza kansa still yana murmushi yace, “My sister kenan, idan har zaki yarda wlh ban taɓa yin budurwa ba”.

Ƙwalalo idanu tayi tace, “kai Yaya dagaske kake yi ko wasa? How can it be said that Handsome Guy and you have no girlfriend? Ko dai yaya kana ɓoye min ne ba ka son na sani?”.

Cikin ido yake kallon ta cike da wani irin salo

Hakan yasaka ta ɗauke kanta tana ci gaba da cin abincin ta cike da yanga da ya zamar mata jiki, komi nata hakan take yin sa

Huro iskan bakin sa yayi be ɗauke ido a kanta ba yace, “Da gaske ƙanwata ban taɓa budurwa ba wlh, akwai wacce nake matuƙar ƙauna sai dai har yanzu na kasa sanar mata”.

Ɗago kai tayi tana kallon sa da mamaki kafin tace, “why?”

“Saboda kwarjinin ta..”

Dariyan ta ya saka shi yin shiru yana sake ƙure ta da idanun sa, sosai take dariya shi kuma yana bin ta da kallo cike da tsananin ƙaunar ta da burge shi da take yi

Sai da tayi son ranta sannan tace, “Yaya har akwai macen da zaka kasa sanar mata ƙaunar ka gare ta sabida kwarjini? Shin me tafi ka dashi ne? Kyau ko nasaba ko kuwa kuɗi? Ni na tabbata Yayana duk kwarjinin ta baza ta kai ka ba, kai dai kawai kace kana jin tsoron ta; abun kuma da ban san ka dashi ba”.

Baffa yace, “baza ki gane bane Sister, duk abinda kika lissafo tana dasu, sai dai kamar yanda nace miki kwarjinin ta da cikan kamalan ta ya zarce duk tunanin namiji ya iya tunkarar ta da soyayya, a kullum idan nayi yunƙurin zuwa gare ta da soyayyata sai inga girman ta da kwarjinin ta bazai bari na sanar mata ba, yanda nake ji a gaban ta da bugawar zuciya da zaran nayi yunƙurin sanar mata sai in kasa, sau ba adadi nayi hakan amma na gaza”.

Kallon Yayan nata kawai take yi cike da tausayin sa har yayi shiru, sannan ta ɗaura da cewa, “How can I help you find her love? Why don’t you let me know who I am; and I promise to tell her, sannan kuma zan taya ka yaƙi har sai ta amince da kai, Yaya ban ga macen da zata ƙi son ka ba komin kyan ta komi kwarjinin ta kuwa, sai dai idan har baka faɗa mata ba, Yaya ka cire tsoro ko fargaba ka sanar mata don Allah”.

Murmushi yayi yace, “na gode ƙanwata, haƙiƙa nasan kina son farin ciki na, sai dai bazan iya faɗa miki ko ita ɗin wace ce ba, but I promise I will try to tell her.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button