NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Daga ƙarshe ma Hajiya tashi tayi ta nufi cikin ɗakin ta tabar Yusra nan tana kumbura fuska kamar Flower, ba don ranta ya so ba itama ta tashi ta fice a part ɗin ma gaba ɗaya, duk zuciyarta babu daɗi.

   ⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

TOMORROW MORNING

      Monday tushen aiki ko Bature na tsoron Monday

Gaba ɗaya ahalin gidan sun tafi aikin su, sai su Umma da aka bari su uku a gidan sai kuma masu aiki, sannan Kaka dake Part ɗin sa

Hajiya itama tunda ta tashi ta soma soye-soyen ta wanda zata tarbi Babban ɗanta dashi, yau gaba ɗaya farin ciki ya cika ta Allah-Allah take yi anjima yayi ta ga dawowar sa, dama sun yi waya jirgin ƙarfe 02:00pm. Yace mata zai biyo; don haka komi take yin sa a tsanake, ita da kanta ta shiga ɗakin sa ta gyara masa tayi masa duk abin da ya dace, bayan ta saka airfreshna sannan ta ƙara masa da turaren tsinke ta rufo ɗakin ta koma kichen taci gaba da harkokin ta.

          ⚫⚫⚫

     Ɗahira tunda ta fara duba Patiens ɗin ta take jin kanta na sara mata, amma dayake ita ɗin jajirtacciya ce bata bi takai ba taci gaba da harkokin ta

Bayan ta gama ta nufi
Ward ta duba sauran mara su lafiyan ta sannan ta dawo Office ɗin ta

Tana son yau ta koma gida kamar lokacin tashin ta but ko kaɗan ba ta ƙaunar taje ta haɗu da maƙiyin ta (sunan da ta saka masa kenan)

Tunda Baffa ya shigo ɗazu ya sanar mata da lokacin da zai je ɗauko sa a airport take ta jin ta babu daɗi, sosai kan nata yake ƙara ciwon

Agogon dake ɗaure a tsintsiyan hannun ta takalla taga ƙarfe 01:20pm. Ne yanzu

Tsaki taja ta tashi ta nufi drower ta ciri magani tasha da ruwan Robber dake ajiye saman table ɗin ta, Labcoat ɗin ta tacire ta rataye akan Hanger sannan ta cire Eyeglasess ɗin ta ta’ajiye saman table ɗin ta nufi Toilet

Alwala ta ɗauro ta fito ta tada sallah, har ta’idar tana zaune nan tana lazimi, barci ne ya soma fisgarta don haka ta tashi ta ninke sallayan ta’ajiye ta nufi gaban table ɗin ta taɗau Glasses ɗin tamayar a idanun ta

Hanyan ƙofa ta nufa don zuwa Office ɗin Abbu ta kwanta acan, amma me ta tuna sai ta dawo tana jan tsaki

Ta san idan taje can zai tilasta mata ta koma gida ne, kuma a yau dai ba ta buƙatar ganin ta a gida, shiyasa ta dawo ta zauna kan kujeran ta ta ɗaura kanta a Deks ta rufe idanun ta, dayike barcin ne sosai yake cin ta don haka babu daɗewa ya ɗauke ta.

Koda ta farka babu ciwon kan a yanzu, sallan Asar tayi sannan ta saka Labcoat ɗin ta, tana shirin fita ne Beeper ɗin ta ya soma ruri, don haka ta fita da sauri tayi hanyan emargency ward.

        ⚫⚫⚫

       At home, everyone was celebrating Usman’s return
      

Gaba ɗaya matan gidan suna part ɗin Hajiya sun je taya sa murnan dawowa

Sai da kowa ya watse sannan Shakira da Yusra da take Part ɗin su Shakiran yanzu suka nufi sashen Hajiyan don su gaishe sa

Yana zaune a dainning yana cin abincin da Hajiya ta girka masa da kanta

Yayi wanka har ya sauya shigan sa cikin ƙananan kaya kamar yanda ya saba

Koda suka shiga gaishe sa suka yi, ya’amsa musu cikin Izza da taƙama

Basu sake cewa komi ba suka miƙe suka fice don ba shi wuri, Part ɗin su Shakiran suka koma suka dasa hira.

          Shi kuma bayan ya gama ɗakin sa ya koma, kwanciya yayi kan Three sitter ya lumshe idanun sa, shi ba barci yake yi ba kawai kwanciyar yayi, sai da aka kira sallan la’asar kafin ya tashi yayi alwala ya fita

A waje suka haɗu da Baffa suka jera har masallacin dake nesa kaɗan da gidan su

Bayan sun dawo a haraban gidan suka haɗu da Abba da Abbu da dawowar su kenan daga aiki

Gaishe su yayi cikin girmamawa, su kuma sai tambayan shi hanya suke yi cike da fara’a, haka ya’amsa musu sannan ya wuce ya nufi babban Parlour

Fadil na zaune a kan kujera yana kallo shi kaɗai ya shigo

Da sauri Fadil ɗin ya gaishe shi

Da kai ya’amsa masa ya nufi hanyan da zai sada shi da ɗakin Kaka

Da idanu Fadil ya bi shi dashi, sai da ya shige sannan ya taɓe baki a ransa yana mitan “miskilin banza! kai da Fadila wlh ban san wanda yafi mugun hali ba”.

Sai kuma ya kwaɓe fuska yaci gaba da kallon sa.

   Tura ƙofan yayi ya shiga yana motsa bakin sa

Kaka dake zaune kan Wheel chair ɗin sa kamar ko yaushe yana karatun Jarida ya ɗago yana kallon sa, sai kuma ya yalwata fuskar sa da fara’a yace, “Maraba da Jikalle na”.

Takowa yayi ya zauna saman kujeran ɗakin yana kallon Kaka, kaɗan ya saki fuskar sa yace,
“Old man are you still alive?”

Sai Kaka ya saki dariya me sauti yace, “ja’iri ka ƙosa na mutu ko? To ina nan babu inda zan je sai na ga auren ka”.

Kyakykyawar murmushin sa yayi yana shafa gashin kansa yace, “uhmm Kaka kace da sauran ka kenan tunda Ni dai ba yanzu ba”.

“Koma dai me zaka ce sai naga auren ka tukun zan bar duniyar nan, dama tunda nayi muku maganar kai da takwara babu wanda ya haɓɓa sa, kun fi so dai a haɗa da ƙannin ku ko?”.

Usman taɓe baki yayi sai dai be ce komi ba

Kakan changed the conversation and asked, “Ya hanya?” Shi kuma ya’amsa masa a taƙaice

Kaka sai zuba masa hira yake yi, shi kuma daga ya’amsa da Eh sai A’a, daga ƙarshe wayan sa ya ciro yana latsawa yana sauraron Kakan, a haka yaja dogon lokaci a ɗakin kafin ya miƙe yayi masa sallama ya fice.
[5/26, 12:54 PM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
             FAMILY DOCTORS
                         ????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
  NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
                 NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT ????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

        
SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

        EPISODE Sixteen

           Sai ƙarfe 05:45pm. Ɗahira ta koma Office ɗin ta, Jakarta ta ɗauka da abinda zata buƙata ta fito ta rufe Office ɗin ta nufi Lifter

Tana sauka ta fita ta nufi inda motan ta yake ta buɗe ta shiga, rufewa tayi ta’ajiye jakar ta kan Kujeran me zaman banza sannan tayi ma motan keey, sai dai yaƙi tashi, ta daɗe tana gwadawa amma yaƙi ya tashi, guntun tsaki taja tana dafe goshin ta, lumshe idanuwan ta tayi na kusan minti 2 kafin ta buɗe ta sake gwadawa amma ina har yanzu be tashi ba, fitowa tayi tana ɗan waige-waige, sai kuma ta nufi gaban motan ta buɗe Garage ɗin ta soma tattaɓa wa, duk ta duba ko da akwai matsala ne amma ita a fahimtan ta bata ga komi ba

Tana nan tsaye a wajen tana ɗan sake duba wa taji sallama, sai ta ɗago kyawawan idanuwan ta wanda ƙwayan ciki suke ƙyalli sakamakon Hasken fitillun haraban wajen, amsa mishi tayi tana kau da kanta ganin kallon da yake mata tamkar zai haɗiye ta

“Are you all right? I’ve seen you here before. Are you still gone? What’s going on?”

Ɗahira kamar baza tayi magana ba, sai kuma ta ga hakan be dace ba tunda taimakon ta zai yi, bata ɗago ba ta bashi amsa, “Wlh nima ban sani ba, kawai ta ƙi tashi ne”.

Dr. Sa’id yace, “ok bari in duba miki mu gani ko?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button