NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Tana fita Shakira ta saki murmushi tana cewa, “Dama haka nake so gwara kije ki faɗa ma Hajiyar ki don ta ƙara ƙullatan ta, shegiya Ni wlh ba ƙaunar Ɗahiran nan nake yi ba, da wani idanu sai kace na fataken dare, kai ko a turawan ma bana tunanin akwai masu irin wannan idanun..”

Ƙaran buɗe ƙofarta shi ya katse mata maganar ta, tayi saurin juyawa tana kallon me shigowa, ganin Mahaifiyar ta ne ya saka ta sauke ajiyan zuciya har da dafe ƙirji

ƙarisowa wajen ta Hajja Fatu tayi tana kallon ta tace, “What happened to Yusra leaving here in a rage?”

Dariya Shakira ta kwashe dashi tana cewa, “me kuwa zai faru in ba zugo ta da nayi ita da Ɗahira ba, ai yau sosai na fusata ta don har maganar Ya Usman nayi mata, yanzun ma Mahaifiyar ta za taje ta sanar ma wa”.

Sai kuma ta kuma kwashe wa da dariya tana cewa, “wlh da ma maganar ya koma kunnen Ya Usman inga yanda zai yi ƙulun kubura da ita”.

Hajja Fatu itama dariyan tayi tace, “yauwa ɗiyar albarka ai gwara da kika zugo ta ɗin, idan ta sanar wa mahaifiyar ta na san yanzu gaba ta soma ita da A’isha, hmmm mu zuba yanzu ma aka soma”.

Wannan shine halayyan Shakira da Mahaifiyar ta, ko ince ƙudurun su akan Ɗahira da Maman ta

Yusra da Ɗahira basu shiri tun farko; sakamakon zigin da Shakira take yi a tsakanin su batare da sun sani ba, ita Yusra akwai zafin kai da saurin fushi, tun farko dama ba wani shiri suke yi da Ɗahira ba, hakan yasaka Shakira ta samu dama take ƙara wa abun wuta, duk idan suka zauna tare da Yusra sai ta ce mata, “Ɗahira ta zage ta, ko tayi gulmanta”, hakan yasaka Yusra ko magana ta dena ma Ɗahira kullum kallon ta da abun take yi, ita kuma Ɗahira dama ba me son shiga harkan da babu ruwan ta bane bare kuma idan ana mata wulaƙanci, don haka itama ɗin sai ta fita harkan ta a cewar ta “duk ranan da ta sauko ta dena ɗaga mata kai sai su ci gaba da mutunci” kuma dama Ɗahira tana ganin itace Babba babu yanda za’a yi ta zauna tana bin ƙanwar ta don kawai tana son su shirya tunda ta san bata yi mata komi ba, duk da su huɗun ba wani tazara ne a tsakanin su ba duk sa’annin juna ne, sai dai Ɗahira aka fara haifa yanzu haka shekarun ta 25years and Two Month, sai Shakira me shekaru 25years cif-cif, sai kuma Yusra me 24years and 8month, maraban su da Fadila kwana goma ne

Gaba ɗaya ahalin gidan halayyan su ɗaya ne na jijji da kai da nuna taƙama, sai dai na wasu ya fi na wasu ne musamman ma Usman da ya fi kowa a gidan, kuma hakan a jinin su yake.

_Hmm now the game has started because there is a lot cakwakiya  in this family, just go ahead and follow me and suburbuɗo me a comment to get more Post.
[5/22, 10:47 AM] Oummu Ɗahirah: ????????????????????????????????????????
FAMILY DOCTORS
????
????????????????????????????????????????

????????????????????????????
NAFEESAT RETURN
????????????????????????????

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT????????‍

بسم الله الرحمن الرحيم

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION????

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS ????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirah????

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba ɗaya. GOMA’S FAMILY

*EPISODE Seven*


      Sallama tayi ta turo ƙofar ta shigo, Aunty Amarya dake zaune gefen gado ta'amsa mata tana kallon ta

ƙarisowa tayi ta zauna kusa da ita tare da miƙa mata ledan tana cewa, “Ga shi Mama”.

Bata amsa ba tace da ita, “Where have you been waiting for me?”

Ɗahira tace, “na je wajen Shakira amsan Littafaina ne”.

Gyaɗa kai kawai tayi tana ɗaukan ɗan kitt ɗin dake gaban ta ta miƙa mata tace, “ga shi Abbun ki ya ce in baki kyautar sa ne”.

Saurin miƙa hannu Ɗahira tayi ta’amsa tana buɗe wa, murmushi ta saki ganin danƙareriyar sarƙan gwal kana ta kalli Maman nata tace, “ina Abbu ɗin?”

“Ya fita, Ni kuma ki riƙe wannan ledan da kika amso sai ki ɗinka”.

Dariyan farin ciki Ɗahira ta saki kana tayi mata godiya tare da nuna murnan ta a fili, buɗe ledan tayi ta soma duba wa, atamfofi ne guda biyu masu kyan gaske sai kuma Material guda ɗaya

“Mama Nagode sosai Allah ya saka da alheri”.

Murmushi Aunty Amarya tayi tana kallon tilon ƴartan cike da so da ƙauna tace, “ki dena godiya tunda ya zama dole ne mu yi miki”.

Daga nan miƙe wa Ɗahira tayi zata fita, Aunty Amarya ta kira ta ta dawo, sake zama tayi inda ta tashi tana kallon Mamar nata

Ita kuwa cikin sauya fuska tace, “Meyasaka kika kai ƙarar Usman don ya fasa miki waya?”

Shiru Ɗahira tayi tana sunkuyar da kai ƙasa

“I don’t want to hear it again, do I?”

Gyaɗa kanta tayi

“Tashi ki je Allah miki albarka”.

Sai da ta’amsa da “ameen”. Before leaving

Tana fita ɗakin su ta shiga

Fadila na kan gadon ta tana latsa waya sai faman doka murmushi take yi, idan za’a rantse ma bata san da shigowan ta ba

ita kuwa Direct wajen gadon ta ta nufa ta’ajiye kayan hannun ta, fiddo kayan tayi tana gani, har ta gama dubawan ta’adana sannan ta dawo ta zauna ta ciro Books ɗin ta zube su saman gadon

dai-dai lokacin ne Fadila ta ɗago kai ta kalle ta, nan idanunta suka faɗa kan NOVELS ɗin dake zube kan gado, da sauri ta’ajiye wayan ta tataso ta nufo wajen ta tana zama kan gadon;, ta saka hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin litattafan, cikin farin ciki ta ɗago tana kallon Ɗahira tace, “Hey Sis Where did you get this book?”

Ɗahira da take riƙe da ɗaya daga cikin litattafan me suna BARRISTER IBRAHIM KHALIL tana dubawa ta bata amsa, “It’s mine”.

“Wayyo Allah wlh na daɗe ina neman Littafin RAUDHAN nan amma ban samu ba, Please ki ara min in karan ta, sosai nake son Littafan JIKAR LAWAL GOMA amma na rasa inda zan samu, ko da naje kasuwa nayi yawo but Allah be sa na samu ba”.

Ajiye Littafin hannun ta tayi tana kallon ta tace, “Ni kam samun littafan ta ba ya min wuya, idan kina so sai ki bari adawo min da wayata in saka ki group ɗinta”.

Murmushi Fadila tayi tace, “Thanks Sis, kai wlh har naji daɗi! na ƙosa naga ƙarshen abinda zai faru tsakanin RAUDHA da Captain Rayyan”.

Miƙe wa Ɗahira tayi ta shige Toilet ta bar Fadila nan zaune har ta soma karanta NOVELS ɗin.

If you need my Book so contact me on this Number 07065334256.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

    Tun sanda ya fito General parlour ya nufi part ɗin su, cikin ɗakin sa ya shiga ya rufo ƙofan, Direct gaban Royal Bed ɗin sa ya nufa ya zauna a bakin gadon, har a lokacin be saki fuskar sa ba sai dai baza ka iya gane a halin da yake ciki ba, ya jima ahaka yayi shiru yana tunani sannan daga baya ya miƙe ya soma haɗa kayan sa cikin trolly, bayan ya gama Toilet ya shiga be jima ba ya fito ya bar ɗakin, yana fito wa parlour ya tarda Hajiya zaune tana kallo, a hankali ya taka ya’iso wajen ta ya sami waje kan sofa ya zauna

Hajiya kallon sa tayi tace, “Dama kana ciki?”

Gyaɗa mata kai kawai yayi yana mayar da idanun sa kan t.v

kallon sa Hajiya take yi tana karantan yanayin sa, duk da ta san halin ɗan nata ba kasafai kake gane alƙibilan sa ba, kiran sunan sa tayi

hakan ya saka ya juyo yana kallon ta sai dai be amsa mata ba

“Ina son ka fita harkan yarinyan nan ba na son ko kaɗan wani abu ya sake haɗa ku, yanzu ba kamar Da bane”.

Usman kallon ta yake yi a rashin fahimta, don be fahimci abinda take magana akai ba, sai dai kuma bazai iya buɗe baki ya tambaye ta ba

itama Hajiya ganin yayi shiru be ce komi ba; sai taci gaba da kallon ta don ta san ba amsa mata zai yi ba

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button