SAKATARIYA TA COMPLETE NOVEL

Wani hutu, Nabilah ta ɗau Najeeb da Najma ta wuce da su Bahrain wajen iyayen ta. Sai aka bar Aisha a gida.
Aisha tun tana tsoro har ta dena, kwana uku da tafiyar su Adam ya zo ya ɗauketa ya wuce da ita Belgium.
Ya kira Nabilah ne sai Najeeb ya ɗauka ya ke shaida ma sa ai sun bar Aisha ita kaɗai a gida kuma itama ta gama jarrabawarta.
A Brussels babban birnin ƙasar Belgium su ka sauka. Ba su tsaya ko’ina ba sai gidan shi. Haƙuri ya dinga ba ta na barinta da aka yi ita kaɗai.
Da dare ya zo dubata a ɗakin da ya sauketa sai ya samu tana kuka. Hankalinsa a tashe ya ce ” Aisha mi ya same ki?”
Ya ɗauko biro da takarda ya ma ta rubutu. Ya miƙa ma ta biron akan ta rubuta ma sa amsa. Ta amshi biron ta rubuta ” ina so na je wajen Mama”
” ba kya son zama da ni ne? Kin tsane ni ko? Saboda ba na zama ina kula da ke” ta yi saurin girgiza kai bayan ta karanta.
Jawota jikinsa yai ya rungumeta sosai ya na ɗan bubbuga bayan ta a hankali har bacci ya saceta…
Wannan sati ukun da ta yi a Belgium cikin gata da kulawa ta yi su. Adam yana tare da ita koyaushe, harta office mafiyawancin lokuta da ita ya ke zuwa. Har ‘yar ƙiba ta yi saboda kwanciyar hankali.
Da hutun ta ya ƙare ya maida ita lokacin su Nabilah sun dawo. Ita da ta dawo ba ta ga Aisha ba, ta ɗauka Nigeria ta wuce sai da ta ga Adam ya dawo da ita hankalinta ya tashi. Ta san yadda ta gansu akwai abinda ya shiga tsakanin su nan da nan ta nuna sai dai Adam ya rabu da ita ba za ta iya zama da kishiya ba ko kuma ya rabu da Aisha.
Rikici sosai su ka yi har ya ma fi na farkon lokacin da ya ce ma ta ya auri Aisha.
Ƙarshe ta ce za ta shigar da shi ƙara a raba auren tunda ba zai saketa ba. Ta chanja gida ta ɗau yaranta amma Najeeb ya gudo ya koma wajen Aisha.
Abu sai ƙara rikicewa ya ke, wata rana da ta zo ɗaukan Najeeb sai ta lura da ciki ajikin Aisha, wannan ya sa hankalinta ya kuma tashi. Ƙarshe ta shigar da Adam ƙara, ganin ya ba da haƙurin ta ƙi haƙura ya sa ya ma ta saki ɗaya dan mutum mai matsayi irin na sa ace yana hayaniya da matarsa a kotu ba dacewa bane…
Ma su aiki biyu Adam ya ɗaukawa Aisha dan su dinga kula da ita lokacin cikinta ya girma.
Lokacin da cikin ta ya shiga wata na takwas Hajiya Mama ta ce za ta zo ta zauna da ita, ta shirya zuwa sai aka ma ta rasuwa Babban yayan su ya rasu sai ta ɗaga tafiyar zuwa wa ta sati….
“Sir Najeeb, Sir Najeeb”
Muryan Farida ya dawo da shi daga dogon tunanin da ya ke.
“Sir ka na da meeting ƙarfe tara”
“Ok” kawai ya faɗi ya miƙe tsaye.
Yanayinsa kaɗai ya nuna ma ta akwai abinda ke damun Najeeb, kuma koma minene to yana da girma.
SAKATARIYA TA
…….(My Secretary)…….
Azizat……✍
Wattpad @000Azee
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Free page
0️⃣1️⃣4️⃣
Tana zaune a office Faruƙ ya kirata wai gashi a kamfanin su. Kwatancen office ɗin ta ta ma sa sannan ta ajiye wayar tana cigaba da aiki. Minti biyar kacal sai ga Yakubu da Faruƙ sun shigo.
“Farida haka yaron nan ya zama luƙeƙe. Kin san da farko ban ganeshi ba”
“Kai ma ka faɗa ai, wannan sai ya goyeni yai yawo da ni duk faɗin garin nan bai gaji ba”
“Haba Anty, ɗan ni ɗin nan” Faruƙ ya faɗi yana dariya
Yakubu ya fita ya basu wuri, dama wajen Anas zai je ya haɗu da Faruƙ ɗin.
‘Yan uwan biyu su ka zauna su na taɗi, su na yi su na dariya.
Wayar Farida ya ƙarɓa ya na duba hotuna. Ko ba a gaya ma sa ba ganin hotunan selfie da Farida ta yi da wani saurayi ya tabbatar ma sa shine Rayyan.
“Sis, wannan shi ne sirikin na mu ?”
“Kai ba na son gulma”
“Wallahi ba ku da ce ba, wannan ai kin fi ƙarfinsa. Hmm ina tausaya ma sa wallahi, aka yi auren nan mijin ta ce zai koma dan ba zai iya da masifar ki ba”
“Buuuuyagi” wafce wayan ta yi tana faɗin ” ka ji min rainin hankali, wato dai ni ka ke zagi ko” ta maki kafaɗar sa ta ce ” Faruƙ yaushe ka raina ni haka?”
Yarfe hannu ta farayi shi kuma ya fara dariya. ” jikin ka kamar wani katako, wai yaushe ka girma ne haka? Faruƙ”
“Serious Anty Farida ba ki dace da shi ba, kin ga lokacin Lukman…”
“Faruƙ!” Ta faɗa da ƙarfi.
Ya haɗa hannu ya ce “afuwan Anty na ta kai na”
Haɗe fiska ta yi ta tsume.
Faruƙ ya sa hannu ya fara tattaɓa kumatun ta yana tsokanarta kaman yadda yake yi lokacin suna yara.
“Anty kumatu, Anty Kumatuttu”
Ba ta san lokacin da dariya ya kuɓuce ma ta ba.
“Yaron nan ka mugun raina ni wallahi”
Yai dariya ya ce ” na tuna da, lokacin idan na ce mi ki Anty Kumatu har maƙota sai anji faɗar mu”
Ta fara dariya sosai harda kama ciki.
Faruƙ ya cigaba ” lokacin tunda na gano bakya son sunan sai na samu abun tsokala. Kin tuna lokacin da ki ka kwaɗa min tukunya har goshi na ya fashe?”
“Ai ranan Ummi ta zane ni kamar ba gobe” ta faɗa cikin dariya. Suna cikin dariyan kakkausan muryan Najeeb ya doki kunnen ta.
“Miss Salihu”
“Sir” ta faɗi tana miƙewa tsaye.
“To my office”
Ya jima tsaye yana kallon su tun daga lokacin da Faruƙ ya ke shafa mata kumatu. Zuciyar sa ta yi baƙi haka nan idon sa ya kaɗa yai ja, a take ƙwaƙwalwarsa ta tariyo ma sa sunan da ya gani ranan My Ray
Ta ya za ta kawo saurayinta har office tana iskancin da ta ga dama. Enough is enough dole ya taka ma ta birki. Abinda zuciyarsa ta tsayar kenan dai-dai lokacin da Faridan ta shigo.
“Ga ni Sir” ta faɗi a hankali
Da ƙarfi ya fara masifa “Miss Salihu yaushe ki ka maida office wajen soyayya da iskanci?. Listen young Lady, idan ba ki san yadda za ki kama kan ki ba go and get married. Ki dena mayar min da office wajen karuwanci. And i…”
“Sir Najeeb ba fa ni na kar zomon ba balle a bani ratayar sa. Daga ƙani na ya kawo min ziyara sai ka maidashi wani zancen banza wai karuwanci. Ba Karuwanci ba a’a Kwartonci”
Kalmar ƙani na da ya ji shi ya sanya duk wani masifar da ke cinsa ta washe, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kamar kiftawar ido, muryar sa da yanayin sa su ka chanja. Cikin sanyin murya ya ce “Miss Salihu, da ƙanin ki da saurayin ki, nan ba wajen ziyara ba ne”
Haushin sa da ta ji kaman ta makeshi takeji sai dai yanzu ba ta son samun matsala da shi dan ankusa biyan albashi, ƙaramin aikinsa ne ya cire mata wani kaso a ciki.
“Zan iya tafiya?”
Yai ma ta nuni da hannu. Sai da ta fita ya sauke numfashi. Cikin zuciyarsa yana cewa to ma miye ruwansa idan ma saurayinta ne?.
Tana zama ta yi tsaki ” shi komai masifa, yai wa mutum kyakykyawar fahimta ba zai yi ba”
“Sis Ogan kin nan ya burgeni fa. Saurayi da shi amma ya mallaki babban kamfani kamar wannan, gaskiya na jinjina mi shi”
“Ko za ka je ya baka aiki ne. Nan za ka san wannan saurayin zuciyar dutse gareshi”
“Oh really”
“Hmm ai ni ma ba dan bana barin hau ta hauni ba da tuni an jima da fatattaka ni”
“Kai Masha Allah, wa su kam Allah ya basu duniya, ga shi handsome, ga kuɗi, ga class…”
“Zan make bakin ka Faruƙu”
Dariya yai ya ce ” Jiya na yi mafarkin kin auri wani millionaire. Wai gamu a wani haɗaɗɗen mansion, wai nan ne gidan ki”
“To Sayyadi Sheikh Umar Faruƙ, ma su mafarkin waliyyai”
“Da gaske fa Anty Kumatu”
Ta ɗau wani littafi za ta buga ma sa ya kauce yana dariya…
……………….
Wannan karan ba ta yi garajen barin wajen aiki ba dan ta san yana ɗaya daga cikin babban dalilin da ya sa Najeeb ya rage albashinta a watan farko da ta fara aiki. Ranan Laraba ta tambayeshi leave ɗin kwana biyu ya ce ya bata kwana ɗaya. As usual sai da ta yi ƙorafi amma bai kulata ba.
Wannan karan bayan Walima ba abinda za’ayi. Baffa yai iya ƙoƙarinsa wajen yiwa Maijiddah kaya, duk da bikinta ya zo ma sa cikin matsi.
Ranan Alhamis aka je yi ma ta jere, su Farida ne ‘yan gaba-gaba wajen ganin komai ya tafi dai-dai. Gidan yana da kyau sosai, tana da ɗakuna biyu na ta sannan an ware ma ta kitchen daban sai dai store ne za su haɗa da Aneesa…