SAKATARIYA TA COMPLETE NOVEL

SAKATARIYA TA COMPLETE NOVEL

“Yaushe haka ta faru?”

Baaba Sabuwa ta ce ” ina ga wata na biyar kenan. Tun lokacin mijin ki na kwance a asibiti”

“Ayya amma ban ji daɗi ba”

“To ya za’ayi, Hannen ce tanada gajen haƙuri, shi kuma aure musamman idan ba kai kaɗai ba ne to dole ka sa haƙuri a ranka, ka dinga ɗauke kai a mafi yawancin abubuwa da za su dinga faruwa a gidan”

Farida ta amsa da hakane. Dan ta san yanzu haka ba zai wuce a kan ɗan ƙanƙanin abu ba ne su ka samu matsala Anty Hanne ta nemi sakin. Dan matar tana da shegen neman saki idan su ka samu matsala da mijin ta.
Ko kafin ta yi aure ma lokacin tana gidan akwai ranan da su ka samu matsala da Baffa Musa ta dinga zage-zage ƙarshe ta dinga cewa idan ya isa ya saketa mana, ya yarabata da sauran igiya biyun da su ka rage. Sai anan ne ma Farida ta san ashe ya taɓa sakin ta sau ɗaya…

Da Baffa ya dawo da dare ta shiga falon sa dan su gaisa da ke ƙarfe takwas da rabi Najeeb ya ce zai zo ɗaukan ta.

“Babana na kaina. Allah bar min kai”

Baffa Musa ya amsa da Amin.

“Baba na” ta faɗa da sigar zolaya

Baffa Musa da ke lissafta wasu kuɗaɗe ya ce “Na’am ‘ya ta”

“Na ce naga ma ka wata kyakykyawar bazawara ‘yar Fulani. Shekarunta ba wani yawa sosai arba’in da ɗaya ne kacal”

Baffa Musa ya ajiye kuɗi ya tattara hankalin sa kan Farida yana mamakin kalamanta. Ta yi auren ma ba ta dena shirme da shiririta ba.

“Baba Allah kyakykyawa ce sosai kuma girmanta bai nuna a jikinta ba, dan idan ka ganta sai ka ɗauka ‘yar shekara talatin ce. Yaranta huɗu ne kacal”

“Tashi ki wuce gidan ki. Shirmen ki yai yawa Farida. Allah ya kaiku lafiya ya dawo da ku lafiya”

“Baba Allah ba shirme ba ne. Sai ka cikata gurbin Anty Hanne da ita”

“Tashi tashi maza, mun gode da ziyara” ya faɗa da ɗan ƙarfi.

“Baba dan Allah ka auri Ummi na. Ka ga sai ya zamana duk kuna kusa da ni”

Baffa Musa ya girgiza kai ya cigaba da abinda ya ke, ganin ya ƙi kulata ya sa ta ce “Baba na ka amince?”

“Ba za ki tafi ba sai na ɗau bulala na zane ki ko”

Farida ta tashi tana dariya…

Bayan sun koma gida kusan ƙarfe tara da rabi Anas da Najdah su ka zo mu su sallama. Da ke dare ne ba su fi awa ɗaya ba su ka tafi. Wannan ne karo na biyu da su ka zo gidan su tare saɓanin zuwan farko Najdah ta ɗan sake jiki an yi hira da ita…

Washe gari da safe ƙarfe takwas Jirgin su ya lula sama. Paris su ka fara zuwa su ka yi kwana huɗu sannan su ka wuce Amsterdam su ka yi kwana biyar. Sai da su ka je Italy da Netherland kafin su ka dawo ƙasar America wanda anan su ka yi kwana goma cur, sun zaga garuruwa da dama da wajajen tarihi har makarantan da Najeeb yai tundaga kindergaten har MIT inda yai first degree na shi.
Ba ƙaramin soyayya su ke gwada wa junan su ba. Yanzu kam Farida ta zaƙe sosai wajen ganin ta sace zuciyar mijinta da abubuwa. Tunda babu zafin yanzu zaƙewa ta ke yi su sarrafa junan su da kyau ta inda za su gamsu da juna sosai.

Daga NewYork ta ƙasar America sai Dubai. Farida kam tun tana mamaki da ƙorafin kashe kuɗi da Najeeb ke yi har ta dena.

Daga Dubai sai ƙasa mai tsarki inda su ka gudanar da Umara. Kullum su ka je Ka’aba sai Farida ta yi kuka, tana kuka tana roƙa wa mahaifinta gafara, tana roƙawa Umminta, Baffa Musa, ƙannen ta da ‘yan uwanta da kuma ‘yan uwan Mijin ta samun albarka da kuma tsira da duniya lafiya.
Above all kuma addu’a wa mijin ta da kuma ‘ya’yan da za su haifa.

Sati bakwai su ka yi wajen tafiye-tafiye kafin su ka dira a Nigeria. Dawowar su ne su ka samu labari biyu ma su taɓa zuciya. Ɗaya Allah ya yiwa Nanna rasuwa sati uku da su ka wuce ɗaya kuma Najdah ta yi ɓarin cikin wata ɗaya.
Maganar ɓari ya sa Farida ta ankara da itama fa rabon ta da period tun barin su Nigeria.
Addu’a ta ke a ranta Allah ya sa itama cikin gareta. Kwana uku da dawowa su ka wuce Jos ta’aziya. Shi Najeeb bayan yai gaisuwa Kano ya dawo ita kuma ta zauna akan sai ta yi kwana biyar. A wannan kwanakin ne ta siyo PT strip ta gwada a gida, ganin test line ɗin ya fito amma bai fito ral ɗin nan ba ya sa hankalin ta ya kasu biyu. Hakan ya sa Washegari ta shirya ta je asibiti aka ma ta gwajin jini sai ga shi result ya nuna positive. Kiran Najeeb ta yi a take a wajen amma lokacin da ya ɗauka ta kasa sanar da shi, she’s too excited…

Da ke Ummi ta kwana da zazzaɓi shiyasa ba ta dawo Saturday ba kamar yadda ta tsara. Ranan Monday da safe ta kamo hanya bayan sun rabu baran-baran da Ummi akan ta ce ma ta ta auri Baffa Musa…

…………………………

Takunta da kayan jikin ta su su ka nunuwa sakatariyar cewa wannan matar babbar macece. Tun daga nesa matar ke aika ma ta harara ta rasa a wanni dalili. Ta ƙurawa matar ido wanda sai da ta ƙaraso kusa da ita sosai ta gane ko wacece matar. Matar Oga ce, matar da hotunan ta ya cika office ɗin Oga Najeeb.

Matashiyar yarinyar da bazata wuce shekaru ashirin da bakwai zuwa da tara ba ta yi saurin miƙewa tsaye tana faɗin “welcome ma”

“Mi ya kawo ki nan? Ke wacece?” Farida ta daka ma ta tsawa.

Budurwar ta rikice ta fara i’iina tana faɗin ” Ma, I’m.. i’m the new secretary. Naomi …. Naomi Masoyi is my name”

Farida ta ma ta kallon banza ta ce ” Mrs Comfort Masoyi na sani a wannan kujeran mi ya kawoki nan?”

“Mrs Comfort mahaifiya ta ce, ta yi accident ne kuma yanzu tana amfani da wheelchair shiyasa ta nemi alfarma a wajen Oga Anas akan na maye gurbinta”

Farida ta ja dogon tsaki kafin ta wuce office ɗin Najeeb.
Yana zaune yana amsa waya lokacin da ta shigo. Murmushi kawai ya ke sakar mata har ta iso. Kai tsaye ta haye cinyar sa ta zagaye hannunta a wuyar sa, ajiye wayar yai ba tareda ya yi sallama da wanda ya ke wayan ba ya shiga kissing matar shi. Sun jima suna gaisawa da juna kafin ya ce “my Queen ya hanya?”
Hannun sa ta kamo ta ɗaura a cikin ta ta ce ” ni da babyn ka mun dawo lafiya”

SAKATARIYA TA
…….(My Secretary)…….

Azizat……✍
Wattpad @000Azee

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

0️⃣4️⃣9️⃣

Ido ya zaro waje yana faɗin “really?”
Ta gyaɗa ma sa kai.

“Alhamdulillah, Alhamdulillah. Thank you my Queen”

Ɗaukan ta yai sama yana juyi da ita.

“My Champ saukeni Hajijiya na ke ji”
Bai sauketa ko’ina ba sai a wajen kujerun da ake zama dan hutawa.

Yana riƙe da hannun ta ya ce “ban san da mi zan fanshi wannan good news ɗin ba. Ask me anything my love”

Hannunta da bai riƙe ba ta kai saitin kirjin sa ta ce “ka mallaka min zuciyar ka ni kaɗai, i want your heart to beat only for me. Abinda na ke so kenan”

Sai da ya kissing goshin ta kafin ya ce “zuciyata ta jima da zama mallakin ki. I love you Aysherh only you”

Haɗe bakin su ta yi tana faɗin “i miss you”

A hankali ya zare suit ɗin jikin sa ya fara ɓalle buttons ɗin shirt ɗin ciki.

“My Champ mu na office ne fa” ta faɗa in between kisses.

“Wait here” ya faɗi tareda tashi ya je wajen table ɗin sa. Waya ya ɗauka ya kira Sakatariyar shi.

“Ki sa ka do not disturb tag a jikin ƙofa”

Bai jira mi za ta ce ba ya katse kiran. Wani remote ya ɗauka ya kulle ƙofar shiga office ɗin wanda ko mutum ya zo shiga babu yadda zai yi sai dai an buɗe ta ciki. Ya rage wutan office ɗin kafin ya ƙarasa wajen Madam ɗin sa.

A hankali su ka fara gudanar da abubuwa akan kujera. Nishin da Najeeb yai lokacin da wani daɗi ya ziyarce shi ya sa Farida faɗin “za a jimu fa”
“Soundproof” kawai ya iya faɗa ya cigaba da shiga ciki ciki…
Sai lokacin ta tuna da mafi yawan lokuta da ta ke son jin gulma amma ba ta iya ji ba saboda duk abinda ake a office ɗin ba ka jin sa a waje, Lokacin da ta ke Miss Salihu…

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102Next page

Leave a Reply

Back to top button