ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Yauma duk da tarin farinciki da Jalila ta tsinci kanta a ciki yau, amma bacci ya kauracewa idanuwanta, jikinta na bata Jalal yakoma shan giya, da kyar ta samu bacci ya dauke ta, amma mafarkin Jalal a cikin wani yanayi na shaye2, yasata farkawa, gabanta na wata irin mummunar faduwa, wayarta ta dakko ta duba karfe biyu da rabi na dare, ga shi ita ba lambar Jalal ce da ita ba, tarasa mema zatayi gallery dinta ta shiga tana dubawa, tsofaffin ajiyayyun hotunan ta take dubawa, hotunan da sukayi da Jalal tun wani zuwa da Hanan sukayi, haka taita kallon hotunan, a haka har ta kawo kan hotunan birthday dinsa, cin karo tayi da wani hoto da’akayi harda Hannah a ciki, take gaban Jalila ya fadi, dan sam ta manta da Hannah, kuma barin Hanna ba tareda daukar wani mataji ba tamkar kashe maciji ne ba’a sare kansa ba a rayuwar Jalal.
A hankali ta ajiye wayar, ta sakko daga kan gadon ta shiga toilet tayi alwala tazo ta tada salla.

Ranar litinin Jawwad shima yayi nasa shirin tsaf domin tafiya Gurin nasa aikin dake birnin tarayya, Abba yayi masa Nasiha sosai tareda sa masa Albarka, haka ma bangaren Maama, tayi masa Addu’a da sa Albarka, dukda marin da Maama tayi masa akan Naja, hakan besa ya nuna mata har yanzu yana fushi ba, Bangaren Jalila kuwa har kuka tayi, saboda zatayi kewar Yayan nata sosai
Abba yace “Jalila kina kuka dan zeyi tafiya, kuda kwanan nan zeyi Aure gaba daya zasu bar gidan, su barki seke kadai”
Kara fashewa da Kuka Jalila tayi, Nana tace “Abba ka gani ko? Wannan yar taka ta fiye shagwaba wallahi”
Jawwad yace “haba babyn Abba, sekace ba jaruma ba, zan dawo ai kidena kuka”
Sukayi ta tsokanarta ita kuwa dagaske take kukanta.
Haka sukayi sallama da Jawwad shima yakama hanyar tafiyar sa.

Jalal yana waya da daddyn sa sosai, sannan suna waya ds Jawwad, suna shirye2 yadda biki ze kasance a tsakanin su.
Abban su Jawwad yana kasuwanci ne a tsakanin Kano da lagos, dan haka in yaje suka haduwa da Jalal.

Jalila Nason sanin halin da Jalal yake ciki, amma babu wata hanya da zata san hakan, dan haka taketa kokarin boye damuwarta.

Maama Allah ya temaketa Abba ya sakko daga fushin dayake da ita, sannan tunda abun nan ya faru Su Yaya mairo ko a waya basu kara neman Maama ba, abun ya dameta sosai dan haka ta shirya da kanta taje gidan su.
Tunda tayi sallama suka amsa suka shareta suka ki kulata, ita tayiwa kanta gurin zama, ta gaida Yaya mairo amma taki kulata, seda ta bata ‘yan kayan data saba kaimusu, shine Yaya mairo ta dan saki rai suka gaisa, Naja ta gani a lullube tana bacci, Maama tace “Yaya, Naja ba lafiya ne?”
Kafin Yaya mairo ta amsa Naja ta fara magana cikin maye “Ni… Ni.. Ba… Wallahi baaaaani da…. Da lafiya, Shiyasa naiwa kaina caaajiii, baaaa danki yaki Aure na baaaaaa, wallahi….
Cikin tsawa Yaya mairo tace” yimin shiru dan ubanki, ciwon mara take, shine ta sha magani fiye da ka’ida”
Gaba daya jikin Maama yayi sanyi saboda babu tantama Naja maye takeyi. Shiru tayi takasa cewa komai, Naja ta cigaba da surutai, can kuma ta kwalla uwar kar, sega jini na gudu a tsakar dakin daga karkashin Naja.

Se bayan la’asar su Jalila suka gama lectures ta gaji matuka, haka kurum tun suna lectures takejin gabanta yana faduwa, da kyar ta tsaya aka gama lectures ta fito, danma manu direba ne yaje dakko ta daga school, abunda yabata mamaki be wuce ganin motar Hannah a gabansu ba, tana tsala gudun wuce sa’a, kuma da alama layinsu zata shiga, Jalila tasa Manu direba yayi parking a farkon layinsu, ta sauka ta shiga layin da kafarta, aikuwa tana zuwa taga Hannah tayi parking din motarta ta shiga gidansu Jalal, Jalila batayi shawarar komai ba ko tunani tabi bayan Hannah zuwa cikin gidan.

Masu kirana a waya please am sorry, ku dinga min magana ta what’s App, ina kokarin duba messages, amma kira musamman idan ina aiki, bana samun daga bakuwar lamba am sorry.
Ina godiya da kulawa.

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.
Watpad @Ayshercool7724
????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE  4️⃣5️⃣98

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

A hankali Jalila ta cigaba da bin bayan Hannah, ba tareda ita Hannah ta sani ba, Hannah ta bude kofar babban palourn ta shiga, Jalila ta biyo bayanta amma ta tsaya a corridor yadda ba wanda ze ganta, Hannah ba karamin mamakin kyai da tsaruwar gidansu Jalal tayi ba, an kashe masa dukiya matuka, tun daga harabar gidan zaka gane mzauna gidan na cikin ni’imar ubangiji ta dukiya da yake bada ita ga wanda yaso a lokacin da yaga dama.
Koda ta shiga palourn ba kowa, seda ta tsaya ta karewa tangamemen palourn kallo, sannan ta jinjina kai tareda yin ajiyar zuciya, ta fara sallama, Mummy dake kitchen ta amsa tareda fitowa da jug a hannunta, suka gaisa da Hannah, Mummy na mata kallon rashin sani,
Mummy tace “bari in kira miki Ilham din, dan a zatonta kawarta ce” Hannah tace “A’a ba gurinta nazo ba, Mummy dan Allah Jalal fa?”
Mamakine yakama Mummy amma ta dake tace “Ai kusan watansa guda baya gari, yana lagos”
Hannah tace “Ai dole ya lallaba ya gudu lagos mana, Ina fatan mahaifinsa yana nan”
Mummy tace “lafiya kuwa?”
“Ina fa lafiya, ina son ganin mahaifinsa tunda shi baya nan”
“me mahaifinsa ze miki ne? Ki gayamin menene?” hakan yayi daidai da fitowar Ilham da alama fita zatayi, kawai taga Hannah, take gabanta yayi mummunar faduwa, kirjinta yafara dukan goma2, ta wani hade rai, ta karaso palourn cikin kasaita kaman gidan father dinta, tazo ta tsaya tareda kama kugu tanawa Hannah kallon da wacce kika zo?.
Kallo daya Hannah tayi mata ta dauke kai, tareda yin murmushi a ranta ta kalli Mummy tace “Gara in gayawa mahaifin Sa abunda ake ciki, na gaya masa wancan karon be dau mataki ba, shi namjine ke ba lallai ki iya daukar abunda zan fada ba”
“ki Fadamin bakomai ni mahaifiyarsa ce ai”
Hannah ta gyara zama, sannan ta kalli Mummy tace “wancan karon da nazo nayiwa mahaifinsa magana, nace yayi yadda zeyi a hadu mu rufawa juna asiri amma ba’ace min komai ba, nikuma asirina yana daf da tonuwa, Ina dauke da cikin Jalal na watanni uku a yanzu”
Da sauri Jalila tasa hannu ta toshe bakinta tana zare ido, gaba daya taji kafafuwanta suna rawa.
Hannah ta cigaba da cewa “muna haduwa da Jalal a hotels, kokuma idan yake night clubs, yasaba yimin ciki yace in zubar, wannan karon likita yace rayuwata na shirin fadawa hatsari muddin na zubar da cikin nan, ga iyayena na kokarin ganewa, soyayyar Jalal ce tasa na bashi kaina, wallahi koya aureni ko nayi kararsa ya kula dani da dansa”
Hannah ta karasa maganar cikin kukan kisisina, kasa magana Ilham tayi saboda mamaki.
Hatta Mummy kasa motsawa tayi daga inda take, se ido da take bin Hanna dashi
Hakan yayi dai2 da fitowar Daddy sakamakon jin hayaniya sama2
“lafiya me yake faruwa haka?”
Kafin su bashi amsa, ya sauke idonsa akan Hannah, be manta ta ba, ya kalleta yace “yarinya lafiya kuwa?
Cikeda karfin hali Hannah ta korawa daddy bayani kamar yadda tayi wa Mummy
“Karya kikeyi, Wallahi Jalal baya neman mata, mata basa gaban shi, yana shaye2 amma be yadda da neman mata ba, Jalal ba mazinaci bane ba” Ilham tayi maganar ilahirin jikinta yana rawa
“Masha Allah, dukkan yabo ya tabatta ga Allah, kin fadi magana kuma kin karyata kanki Ilham, tunda kinsan Jalal ba mazinaci bane, ta yaya kika san ina bashi kaina?”
Jalila ce ke maganar cike da kwarin gwiwa, gaba daya suka juyo inda Jalila take, kanta tsaye ta tako har gaban Ilham ta Kalle ta ido cikin ido tace
“Nagode Allah, kinyiwa Jalal kyakyawar sheda, yadda baya neman mata nima ba’a haifi namijin da Jalila zata bashi kanta a titi ba, Wallahi Ilham kinji kunya, tun wuri ki canza hali, tun kafin ki kaini bango in miki abunda se kin kasa shiga mutane”
Ta juya ta kalli Hannah tace

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button