ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

Itama Jalila a ranta mita take “tsabar wulakanci koma ya tambayeni ya nake, bayan tafiyar sa ya na karke, ya tafi ya barni ba lafiya koya bugo waya yaji ya jikina, ya sani a gaba da kallo yaki cin Abincin in baze ci ba ni in tafi, mtseww ta danyi tsaki, tsakin ya fito fili ba tareda sanin ta ba.
Saurin dagowa yayi suka haďa ido ta basar.
Mikewa yayi ba tareda ya kalli inda Abincin yake ba ya mike ze fice, itama ta mike da sauri tasha gabansa suka tsaya suna kallon Juna, lokaci na farko da suka kasance tare tun bayan daura Auren su
“lafiya meye haka?” ya tambayeta
“ya zan kawo Abinci ka tashi baka ciba? Salon in koma ayita tuhuma ta”
“in sun tuhumeki kice su koya miki yadda ake kula da miji, dan baki iya ba” Ta dan yatsina fuska ta kalleshi

“Waye mijin? Aini banga miji anan ba, kaima yakamata a koya maka yadda ake kula da mace dan….. Se kuma tayi shiru ganin yadda ya kura mata ido, Ashe fa yanzu mijinta ne, ba kowace magana yakamata ta gaya masa ba

“Ni kike cewa bakiga Miji anan ba ko?, Nagode sosai, matsa kibani guri in wuce”
Hanya ta bashi ya fice daga dakin, bata bi ta kan kayan ba itama tayi waje abunta.

Washegari ma da Safe Aka sa Jalila ta kai masa Abinci, haushin taki kulashi jiya yasa beci Abincin ba yakuma barinsa.
Yana fita ya tafi gurin Abee, bayan sun gaisa Abee yanata tsokanarsa, Jalal yace
“Abee so nake kasa baki su kaimin matata, ko in dauketa mu tafi basu sani ba”

Abee yace “A’a baza’ayi haka ba ai, kwantar da hankalinka, ko gobe kake so za’a kaimaka ita zan saka baki suba ka ita, na goyi bayanka tunda Daddynka yana jin nauyinsu, ina dalili kanada Aure amma sun barka kana ta fama sun rike maka mata” haka Abee ya lallaba Jalal ya tafi.

Yaje yasamu Anty yace mata “kinga tun wuri kubawa yaron nan matarsa yana son abarsa, yamuku kawaici amma kunki ganewa”

Anty tace “Abee Akwai dalilin da yasa muka riketa anan ne”
“A’a Ku bashi matarsa kawai, in baso kike kiga tafara miki laulayi a gidan nan ba, sannan ku kwasheta ku kaita”
Zare ido Anty tayi “Haba dai”
“Eh mana, yanzu da muka rabu da shi yake gayamin insa baki ku bashi matarsa”

Aimin hakuri fa rashin posting akan lokaci, abubuwa sunyimin yawa, adinga min uzuri nagode da kulawarku

Vote and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

What’s app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724

???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ???? 

              *ABDUL JALAL*

         _Story, writing and edited _

                        By
              AISHA HUMAIRA
              ( _Daddy's girl_) 

PERFECT WRITER’S
ASSOCIATION????

(???????? ????????ℕ’???? ℙ????ℝ????????ℂ???? ???????????? ????????’ℝ???? ????????????????????????, ????ℝ????????ℕ???? ????????ℝ ???????????????? ???????? ???????????????????????????????? ????ℕ???? ????ℕ????????ℝ????????????ℕ ????????ℝ ℝ????????????????ℝ????????)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

P.W.A✍️

        PART 2         
                      _PAGE 5️⃣2️⃣ 105

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what’s app number dina
07063065680
Or email address @ www.humaira17@gmail.com
Watpad @Ayshercool7724

         _MY FIRST NOVEL _

Zare ido Anty tayi tace “gaskiyane Abee, tunda ya iya budar baki yace a bashi matarsa he mean it, zanyiwa Anty Salma magana gaskiya, a bashi iga suje can su karata, tunda be san abun Arziki ba”

Abee yace “gara dai kuyi tunani, wannan ba mafita bace ku bashi matarsa kawai”

Tunda Abee ya bashi goyon baya A ranar Jalal ya shirya ya tafi kano ko sallama basuyi da Jalila ba, dan in dai suka hadu fada zasuyi.
Yayi waya da Daddy ya gaya masa yana son zeyi magana dashi, Daddy yayi masa Alkawarin zezo Nigeria su hadu a kano.

Ba zato ba tsammani Ilham ta dawo taga motar Jalal a harabar gidan, ai a guje takarasa cikin gidan ta nufi dakin Mummy tana kwala mata kira,
“Mummy Kinsan Jalal ya dawo kuwa?”
Mikewa Mummy tayi “dagaske ko wasa”?
“Wallahi dagaske nake, ga motarsa can”
Jinjina kai Mummy tayi tace “Shikenan rabu dashi, nasan tunda yazo Akwai abunda ya kawo shi, kyleni da shi kawai”

Ilham ta koma dakinta tana cigaba da tunanin wani mataki Ummanta ke shirin dauka akan wannan lamarin, Itakuma me yakamata tayi?
Wasa2 kwanan Jalal uku da dawowa amma sam Mummy bata sa Jalal a idonta ba, da kanta taje dakin Jalal amma baya nan.
Ilham ma duk yadda taso taga Jalal bata ganshi ba, ko ina yake tafiya oho?.

Bangaren Jalila kuwa sekuma shan gyara takeyi, basu gaya mata Jalal yace zasu koma kano ba.

Kwanan Jalal hudu a kano sannan Daddy ya dawo, koda ya dawo babu wata tarbar Arziki daya samu daga Mummy se mita da masifa, Bebi takanta ba ya cigaba da sha’anin sa, babban abunda yake kular da ita kenan, tasa shi agaba taita masifa Amma ya kyaleta yaki kulata.

Ranar da Daddy ya dawo da daddare Jalal ya shigo, ba kowa a palourn dan haka ya wuce part din Daddy, shikansa Daddy yaji dadin ganin Jalal,

Daddy yace “Ango, Ango se wani kyau ka keyi, alamu hankalin ka a kwance”

Jalal ya dan bata fuska yace

“Ina wani hankalina a kwance yake, Kawai su Anty sunje sun rike ta a can gurinsu ko mene amfanin hakan oho?”

Daddy yai murmushi yace “Tunda sukayi haka Akwai dalili”

Jalal ya dan hade fuska yace
“koma meye dalilin nasu ni munyi magana da Abee zan dakkota tazo ta tare”

“Jalal meyasa kai haka? Zasu ga kaman bakayi musu kara ba”

“Daddy sati guda da komawa makaranta yakamata ace ta koma itama, sannan kasan in dai da Auren nan idan nazo kano bani da masauki, bani kwanciyar hankali saboda masifar Mummy indai nazo gidan nan, nasan bata son Auren nan, nikuma inason abuna, kaga ko nazo Kano a gidana zan sauka baseta ganni ba bazan zo mata gida ba”

Murmushi Daddy yayi yace “koma dai meye she’s your Mum, yakamata ka dinga mata uzuri sannan ka dinga hakuri da ita”

Jalal yace
“Daddy maganar gidan da zan zauna ne yasa nazo Kano fa”

“to wane gidan zaka zauna, gadon kayan zaka koma kokuma yaya?”

“No bazan koma gadon kaya ba, zamana a gidan nan zena tunamin abubuwan da suka wuce masu batamin rai”

“to ya kake so ayi?” daddy ya tambayar yana bawa Jalal attention dinsa

“gida zan siya a tarauni, a can zan zauna in danyi nesa daku, bana son yawan fitina ko hayaniya, Gobe in Allah ya kaimu se muje ka tayani zaban gidan”

“hmm Jalal kenan, to ai tunda bani zan zauna ba, kai da ita matar taka yakamata ku zabi gidan da kuke so”

“Kyaleta kawai duk gidan dana zaba baza tace beyi ba”

“to shikenan ina fatan kun daidai ta kanku babu matsala”

“karka damu Daddy, in Allah ya kaimu gobe muje a siyi gidan, ka gayawa Abba, next week Insha Allah in basu kawo ta ba, zanje in dakko ta”

Daddy kallon Jalal kawai yake, jalal din maganar sa yake kansa tsaye kuma hankali kwance ba wata kunya ko makamancin haka a tare da shi.
Suna ta hirarsu ba zato ba tsammani sega Mummy ta shigo ďakin, seda ta danyi turus ta tsaya, ganin Jalal da tayi kanan kayane a jikin Jalal kaman yadda yasaba sakawa, Amma abun mamaki dogon wandone har kasa a jikinsa, da riga me dogon hannu, wuyansa babu sarka, sannan babu wannan askin banzan da yakeyi kuma ya sawa kan color duk babu, yayi kiba abunsa kuma fuskarsa ba laifi a sake yana murmushi, sabanin da da kullum fusakarsa a murtuke.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button