ABDUL JALAL PART 2

ABDUL JALAL PART 2

“daddy a dawo lafiya, ka musu Allah ya sanya Alkhairi in sun dawo na musu Allah ya sanya Alkhairi, bani da lafiya bazan iya zuwa ba, ka tabattar sakona ya isa gurin Jawwad”

Ta juya ta cigaba da danna remote, haka ya mike ya fice daga palourn tabi bayansa da harara.
Ya fita ba dadewa sega Ilham ta fito daga dakinta, tazo ta samu guri kusa da Mummy ta zauna. Ji tayi Mummy tana tsaki ta dan kalleta tace
“Mummy lafiya kuwa?”

“barni da abun haushi, daddy ze batamin rai, wai se in bishi bauchi gurin bikin nan, ta yaya zanje gurin da Salma zata, ana Auren danta inje, ai na gama zubewa, ba dan ita ba da kodan Jawwad senaje bikin nan, Amma saboda Salma da wannan banzar yarinyar bazani gurin nan ba, Amma bayan biki har can Abujan zanje gidan Jawwad in masa Allah ya sanya Alkhairi, yanzuma na bawa Daddy sako ya bashi, Amma ai naga ke kawar Nana ce, meyasa baki bisu ba? “

Ya mutsa fuska Ilham tayi tace

“Tabdijan akan me zanje, Ai daga baya na gane da hadin bakin ta Wannan banzar take son janye hankalin Yaya Jalal daga kaina, dan haka ba abunda zanje in musu, suje can su karata”
Haka suka cigaba da hirarsu, Ilham na kara kushe Jalila a gurin Mummy.

Jalila Tana fitowa daga hall din ta samu jikin wata mota ta tsaya tana waya, Ahmad ya kirata, tasa wayar a kunnenta tace

“Hello my, ina jinka” ba”a iya jin me ake cewa amma tace “Shikenan in an nagama zan maka magana se mutafi tare” ta dan kumayin shiru tace “A’a idan na koma gida zanci Abinci, bazan iya cin Abinci yanzu ba, in aka tashi zan maka magana”

Ta kashe wayar, tana juyowa taji gabanta ya fadi, Jalal ne a tsaya a bayan ta, ya kura mata ido ko kyaftawa ba yayi
Dan tsayawa tayi itama tana kallonsa, tunda yazo ko sannu bata hadasu ba, ba karamin kyau manyan kaya sukeyi masa ba, gashi gaba daya ya cika gurin da kamshin turarensa, tayi kokarin bin ta gefensa ta wuce, ya kara tare mata hanya, dagowa tayi tana kallonsa ya hade rai kamar be san meye dariya ba yace
” Zoki wuce mu tafi”

Tai masa kallon ban gane nufinka ba tace “Kamar ya, mu tafi ina?”

“ban sani ba, ki wuce mu tafi nace” yayi maganar cikin fushi”

Zumbura baki tayi, tace
“Wallahi ba inda zani ba’a gama ba” yasan halinta da taurin kai, dan haka yasa hannu ya janyo ta har tana kokarin faduwa saboda takalmin ta me tsinine, ba shiri tabi shi be tsaya da ita ko’ina ba se gaban motarsa, ya bude motar yace
“Shiga”
ta kalleshi, cikin muryarta me sigar shagwaba tace
“meyasa zan shiga? Ina zaka kaini kowa yana can ana abun Arziki”
“Wallahi in baki shiga ba zan sakaki da kaina”
Zare ido tayi ta kalli idonsa, babu alamun wasa a abunda ya fada tabbas ze aikata, ba shiri ta shiga motar, ya za gaya ya shiga ya kunna motar, yafara tuki cikin nutsuwa ya bar harabar gurin, yafara tukin kenan aka kirashi a waya, ya daga wayar yasa a hands free, da’alama abunda ya shafi aikin suke tattaunawa shida wanda ya kira shin, dukda zuciyarta a kule take da haushi, Amma bayan ya gama wayar tace
“Ya Aikin kuwa?”
Kamar jira yake tayi magana yace

“ban sani ba, bakida kunya, saboda ke na tafi aikin nan for almost four months baki nemeni ba, Rayuwa ta kaman wanda yake cikin rijiya ne yake neman taimako, kin mikomin abu ina kokarin fitowa kin saki nakoma ruwa, dan kinga ina lallabaki kikemin wulakanci ko? “

” ni wani wulakancin nayi maka? Mekake so in maka kuma? In cigaba da bibiyar ka mahaifiyarka tana min kallon mazinaciya? Da kazo garin nan kana kallona shekaran jiya, har kusa faduwa nayi saboda dalilinka, ko kallona bakayi ba, so kake inta binka, kokuma goyaka zanyi? Ni kawai ana can ana Ta shagali nikuma ka dakko ni, duk gurin nan nika dai na tsole maka ido, ga Ahmad ma yama jirana, yanzu se yayi ta jirana, idan ya tarar bana nan bazeji dadi ba”

ya lura gaba daya a fusace take, yai mata shiru taita mita, yadda Jalila ke kuma fadar Ahmad yafi komai bata masa rai, dan haka yaja wani uban birki a kan titi da seda ta firgita, ya juyo yana kallon ta, ya matso da fuskarsa daf da tata, har suna jin numfashin juna, Jalila najin saukar numfashinsa a fuskarta, gaba daya Jikin Jalila ya hau rawa, taji numfashinta na kokarin tsayawa, gaba daya kamshin turarensa ya cika mata hanci, ga kuma wani mugun kwarjini da yayi mata, cigaba da matso da fuskarsa yake daidai tata, har dogon hancinsa na shirin taba nata, rintse ido tayi sosai jikinta na cigaba da rawa.
A hankali ya dauke fuskarsa, yace mata

“stop shivering, kina tunanin wani abun zan miki? Ba abunda zan miki, sedai ina kokarin nuna miki illar shigar da kikayi ne, look at yourself,”
Jin abunda ya fada, Yasa A hankali ta bude idonta tana cigaba da sauke numfashi.
Ya kuma kallon ta yace

“kalli jikinki babu mayafi, kin hau stage kina Rawa, kowa ya zubo miki ido kina rawa, kalli jikinki, kalli yadda kayan nan suka matse ki, hakan ya dace? “
Kallon kanta tayi, taga yadda rigar ta zauna a jikinta, taga irin yadda Jalal yasata a gaba da kallo, gaba daya seta ji kunya ta kamata, Amma ta maze ta dake, takuma hade rai tareda dauke kanta tace
“Ai dai bahaka na keyi ba, dan dai yau daya, ana biki zaka wani takuramin, naga kai da gajeren wando kake yawo a layi, waye ya dameka?”
Jalala seyayi kamar besan dashi take ba, ya fuskanci rigima takeji, idan ya biye mata fada za suyi a titi, banzan da yayi da ita, hakan ba karamin batawa Jalila rai yayi ba, wayarta ta fara ringing, tasa hannu ta ciro wayar daga jakarta, ta daga wayar tasa a kunnenta, beji me aka ce ba, sedai Jalila cikin shagwaba tace

“please my, na dan fitane yanzun zan dawo Insha Allah, ka jirani semu tafi tare”

Cigaba da wayarta tayi hankali kwance, ta gama tana kokarin ajiye wayar, Jalal yasa hannu ya fizge wayar daga hannunta yace

“Wallahi bazaki koma gurin nan ba”
“Saboda me? Ni gaskiya ka maida ni, wai meye haka?”
“Wallahi kika kuma yi min gaddama, Kano zamu nufa a daren nan, daga nan zuwa a Asuba ma isa kanon, babu abunda yayi min zafi da wani zargi ko wani abu daza’a ce akan hakan, kinsan ni bana gudun magana”

A firgice ta kalleshi, babu alamun wasa a idonsa, he mean what he said, yadda fuskarsa take murtuk din nan, ta tabattar ze aikata abunda yace dan haka taja bakinta tayi tsit, tana kallon wayarta tanata ringing, Amma Jalal ya share, ga shi tana tsoron abunda ya fada, dan ze aikata.

Tanaji tana gani ya maida ita gida, yayinda ana can ana rakashewa, gaskiya Jalal ya kwafsa mata, suna zuwa harabar gidan taga motar daddy, da sauri tace “laa motar daddy yazo”
Nan ma shiru Jalal yayi mata, yana parking ta bude motar ta fice, cikin Sauri ta nufi wata kofa, da ya kasance bangarene da Daddyn Hanan yake saukar manyan baki idan suzo, kamar yadda aka nuna mata.
Tana zuwa ta bude kofar ta shiga da sallama, Daddyn Jalal ne, da Daddyn Hanan sekuma Abba, da wani babban mutum wanda Hanan tace mata baban Yaya Yusuf ne, suka amsa mata cikin sakin fuska.
Tana zuwa ta zauna a gefen Abba, ta kalli daddyn Jalal tace “Daddy sannu da zuwa ya hanya?”
“lafiya kalau Jalila ya taro?”
“lafiya kalau Daddy”
“to Masha Allah, Allah yasanya Alkhairi, Allah ya kaimu naki da rai da lafiya”
Suka amsa da Ameen amma banda Jalila da ta sunkuyar da kai.
Daddyn Hanan yace ” ‘yar baba, keko ganinki bana yi tunda aka fara bikin nan, ina kika shiga haka?”
“Baba ayyuka ne dayawa, kuma naga baka dawowa se dare”
“Hakane kam, sannun da aiki, Allah ya kaimu naki auren ‘ yar Baba”
Abba yace
“Baby ya akayi kika dawo ke? Naji ance kuna gurin walima, ina Kika baro Amaren?”
“Suna can ba’ a tashi ba, ba Yaya Jalal ne… Bata karasa ba Jalal ya turo kofar dakin ya shigo da sallama”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129Next page

Leave a Reply

Back to top button